Abu Rasheed Hausa Novel Complete

Abu Rasheed Hausa Novel Complete

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

Tag: ABU-RASHEED

 

 

 

Zainab Habib(Mom Islam

 

 

_Ga masu so a tallata musu hajarsu suyimin magana ta nan 08141799224_

 

 

 

 

_Bismillahar rahmanir rahim_

 

 

*Ƙauyen Ƙauran Domawa*

_Dake cikin garin saminaka_.

 

 

9:am 23/6/2022 Thursday.

 

 

p 1-2

 

Yarinya ce ƴar kimanin shekaru goma da aihuwa , hannunta riƙe da tulu tana tafiya tana ƴan wake-waƙenta ,

Da sallama ta shigo gidan nasu daya kasance ginin Æ™asa wanda ke É—auke da É—akuna huÉ—u ,É—aya na Goggo Amina ,É—aya na Inna Laure , É—aya na baba ,É—ayan na kwananta tana isowa da ruwan data É—ibo ta kawo gaban Inna Laure ta ajiye tare da cewa “Inna ina tuwon nawa ?”

Inna Laure ta galla mata harara kafin tace “sai da kika gama yawon barkancin naki zakizo kina tambayata abinci ?”idan baki É“acemin da gani ba wallahi sai na cire miki Æ™afa ”

Goggo Amina dake keÉ“e baki tace “kema kika kulata ta gaji munafurcinta ta Æ™yale mutane ,

Shigowar baba ne yasa ko wacce tayi tsit sai suka hau cewa ” Hasina Æ´ar albarka maza jeki rumfa ki É—auko tuwo kici ,kasancewar baba yazo É—aukar wani abu ne yasa bai sauraresu ba tunda bashi da saurin fahimta ya fice .

Inna Laure ta danguware mata kai kana tace “kije ki dakamin yajin can Æ´ar iska “.

Hasina ta miÆ™e tana share hawayen dake zubo mata , ta É—auki robar da barkono yake ciki ta juyo a turmi ta É“are magin dake ciki guda É—aya tasa gishirin data gani a ciki tahau daka ,tanayi tana atishawa ,kafin ta gama dakan yajin duk tasa a hancinta , ihu tasa kasancewar ta gurza hannunta a ido tare da yin tsalle tana cewa “wayo Allah Ummana yaji a idona ”

See also  Zafin Hawayena Hausa Novel

Babu wanda yayi yunƙurin kulata bare su nuna sun ganata , har ta gama kukanta ta share hawaye suna zaune .

Bayan ta kammala dakan ne takawo gaban Inna Laure tace “gashi Inna ” batare da ta É—ago ta kalleta ba tace “ki É“acemin da gani ”

Hasina ta fice da gudu kai tsaye gidan Æ™awar Ummanta ta shiga , da sallama a bakinta tana shiga ta tarar da Æ™awar Umman tata a gindin murhu tana sakun É—anwake , dama sana’arta kenan kullum da safe .

Tana ganin Hasina tace “Æ´ar Umma ina kika shiga ne kwana biyu banajin É—uriyarki ?” Hasina tahau goge ido tana cewa ” ba Inna Laure da Inna Amina bane suka yimin duka shekaranjiya ba ,jiya kuma suka É—oramin tallah har tirai biyu , yau kuma Inna Laure taban dakan yaji har yana shigemin ido , suka hanani abinci ” ta Æ™arashe maganar tana kuka ,

Cikin tausayawa Æ™awar Ummanta da ake kira da Inno ta kamo hannunta kana ta zaunar da ita tace …

Karanta littafin Gidan Uncle Hausa Novel

Hasina na fita baba ya shigo hannunsa riÆ™e da ledar taliya guda biyu , cikin fara’a su Inna suka tareshi tare da ce masa yau zamuci daÉ—i ”

Baba na faÉ—aÉ—a fara’arsa yana waige ,sunsan wa yake dubawa sarai babu wacce ta kulasa , sbda baiji É—uriyata bane ya sashi cewa ” wai ni ina Hasina ne ?” Inna Amina tace “cewa tayi ita bazataci tuwo ba sbda bashi ka bayar a dafa a gidan ba ”

Cikin Æ™unar rai baba yace “wato Hasina ta É—auko ruwan dafa kanta ,ita ba Æ´ar kowa ba amma ta dinga zaÉ“en abinci ?” yanzu ina ta shigane wai ?”baba ya tambayesu cikin É“acin rai .

See also  Bazawara ce Hausa Novels Doc Download

Inna Laure tace “ai bazata wuce gidan Inno Æ™awar uwarta ba tunda acan suke kitsa munafurcinsu ”

Ran baba a É“ace yace “tashi Laure ki kiramin ita ” Inna Amina tace a’a malam ka bari dai ta shigo aja mata kunne yin hakan zai iya janyo maka zagi a gari ”

Baba yace “to shikenan amma ai wannan tozarci ne “,

Yana rufe baki Hasina ta shigo abinka da yaro da taci abinci a gidan Inno ko goge baki batayi ba ,

Tun daga nesa baba ya fara É—ura mata zagi yana cewa “kinaso kiyi halin baÆ™ar uwarki mai baÆ™in hali ,kinaso ki mayar dani matsiyaci ne ehe ?dahar zakice baki cin tuwo ?Hasina ta sanya hannu a baki alamun mamaki cikin tsoro tace “wallahi baba ba’a ba… yazo inda take ya É—auketa da mari wanda sai dataga giftawar taurari ,kafin yace “matsiyaciya kusa mata tuwo ina kallo taci “.

Jikin Inna Amina yana É“ari ta nufi gurin É—umamen tuwon ta sako mata har guda huÉ—u ,ta zubo miya koriya shar wacce babu tabbacin akwai manja a cikinta bare magin kirki “zoki É—auka ” Inna Amina tace kasancewar itace da abinci kuma itace amarya .

Jikin Hasina na karkarwa ta É—auko tuwon baba na zaune ta fara ci , kasancewar ta fara Æ™oshi ,yasata ci kaÉ—an kana tace “ta Æ™oshi ”

Baba ya zaro mata ido tare da cewa “ko zaki amayo dashi sai kin cinye ”

Dan kinga kece kaÉ—ai Æ´a a gidannan shine kike yiwa mutane iskanci ,suma basu cire rai da aihuwaba tunda Allah ne bai basu ba ,ni bazanyi miki goyon da za’azo ana zagina ba dan haka ki kula da rayuwarki ,idan kin munafurcesu kanki kikayiwa ,bayansu baki da wasu iyayen da zaki sanar ma damuwarki ” baba ya Æ™arashe maganar yana sanya hannu a cikin aljihunsa ya fito da naira hamsin yace “ayi cefanen taliya ”

See also  Tobe Dan Dambe Hausa Novel

Inna Amina ta karÉ“a kafin tace “,tunda kin Æ™oshi tashi ki siyomin manja na talatin maggi dunÆ™ule na goma farin magi na ashirin inada goma gashi maza ina jiranki ”

Hasina ta wanko hannu zata fice taci baba yace….!

 

Kinson jin ƙarashen labarin ? da nace bayan sallah zanyi posting sakamakon mutane da suka matsamin yasa na saki littafin yau ,ina fatan masoya littafaina zaku nunamin love ta hanyar siyan littafina .

*Wannan littafin na kuÉ—i ne akan sassauÆ™an farashi ,normal 200 vip 500 special 1k zaki turo da kuÉ—inki ta wannan account É—in 3175689751 Zainab Habibu first bank shedar biya ta wannan number 08141799224 ko kuma katin hoton katin mtn ta wannan number 08141799224 , ga masoyana da basayin whtsapp akwai group dana buÉ—e wanda zandinga yi muku posting ma’ana Æ´an facbook , Æ´an Niger kuyimin magana in faÉ—a muku inda zaku biya nagode.*

 

 

MOM ISLAM

Leave a Comment

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Scroll to Top