Aljanar Gidan Mu Hausa Novel Complete

Aljanar Gidan Mu Hausa Novel Complete

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

Aljanar Gidan Mu Hausa Novel Complete

 

 

 

Daga Alƙalamin

 

_Sarat Alƙasum(Maman Nusaiba)_

 

JARUMAI WRITER’S ASSOCIATION

Aljanar Gidan Mu

Daga marubuciyar:

Amir da Amira.

Aljanar Jarumai.

Hafsat.

Ƙaddara ce.

Tani da Manu.

Rayuwar ma’aurata.

Sumayya baiwar Allah.

Abba ne.

And new book.

Aljanar gidanmu.

 

Ya Ubangiji yadda ka bani damar É—aura AlÆ™alamina ka kuma bani dama da ikon sarrafa tunanina da baiwar da ka mini, ina addu’a ka bani ikon É—auke shi lafiya, ya rabbi ka bani ikon rubuta abin da zai amfani Al’ummar Annabi Muhammad (S.a.w) Habibi É—an gatan Allah shugaban duniya da Æ™iyama. Allah ka Æ™ara mana lafiya da wadatar zuci ka hanemu ga aikata saÉ“o….

 

 

*WhatsApp number +966599791573*

 

*بسم الله الرحمن الرحيم*

 

0️⃣1️⃣

 

Tsaye take a gefen babban titi tana rusar kuka, gefenta wata tsohuwa ce kwance tana rawar sanyi bakinta na haÉ—ewa da labbanta saboda yadda jikin nata yake rawa sosai. Juyowa yarinyar ta yi za ta yi magana sai ta fasa ta mayar da hankalinta ga wata mota da take mata oda, tsayuwa ta yi tana ƘifÆ™ifta idanu tana jiran taga wanda zai fito daga motar…

 

Babbar motar ce fara sol ta yi parking a gaf da ita, direban dake a set ɗinta ya buɗe murfin motar ya fito fuskar shi na nuna fushi, yana zuwa bai tsaya yin komai ba ya kife yarinyar da mari ya kuma ƙara mata wani a ɗayan kuncin..

Karin wasu littafai da zaku so

Powered by: www.mynovels.com.ng
“Ke uban wa ya ce ki zo kan hanya ki tsaya? Dan uwarki ana magana kin wani tsare da manyan idanunki kamar wata maiya, to ki shiga hankalinki so kike ki É“ata mini suna a gari na Æ™are rayuwata a gidan yari ko me?”

 

Shuru yarinyar ta yi ta zuba masa idanunta wanda ya ciko tam da kwalla, sosai taji zafin marin da ya mata hakan ya sa hawayen idanunta suka shiga zubowa jikinta nawa, da sauri ta sunkuyar da kanta tana goge kwallar data zubo mata tare da lumshe idanun nata, sai da ta jima kafin ta ɗago kai za ta yi magana taga ana ƙoƙarin buɗe motar daga set ɗin baya ta yi shuru tana kallon ƙofar..

See also  Guntun Goro Hausa Novel

 

Wani babban mutum ne ya fito tare da wata Æ´ar yarinya mai kimanin shekaru 13 tana riÆ™e da Æ´ar Teddynta, idanunta ne ya sauka akan yarinyar da taga an mara ta yi saurin sakin hannun mahafinta ta isa gurin yarinyar ta tsaya, a sanyaye takai hannu ta shafa gefen fuskarta da shatin yatsun direbansu yake kwanta tar.. “Ki yi haÆ™uri zan rama miki marin da ya miki kinji.” Yarinyar ta faÉ—a ta Æ™ara da cewa” Ya sunanki?”

 

Ajiyar zuciya yarinyar ta sauke ta buÉ—e idanunta akanta sannan ta ce” Na gode sunana Amra.”

 

Murmushi Yarinyar ta yi ta kamo hannun Amra da yake É“ace da taÉ“o ga dauÉ—a data kwanta amma bata ji kyamarta ba ta riÆ™e hannun nata tana shafawa ta ce” Sunanki mai daÉ—i ni kuma sunana Afra amma ana ce mini Auta dan ni ce Auta a gidanmu, kuma z.. Bata Æ™arasa maganar da take son yi ba mahaifin nata ya iso gurin tare da fisge hannun Auta daga na Amra ya ce” Auta me ya sa bakya ji ne? Yanzu wannan Æ™azamar yarinyar kike taÉ“awa ko ba ki ga yadda take da datti ba? Kalle ta fa sai wari take.”

 

Amra ta kawar da kanta gefe ta durÆ™usa a gaban shi ta ce” Ranka ya daÉ—e ka taimaka mana kaga Mamata can a kwance bata da lafiya bamu da gurin kwana ko abinci da Æ™yar muke samu muci, ka taimaka mana na kaita Asibiti” Ta faÉ—a tana riÆ™e Æ™afafunsa.”

 

Cikin azama ya buge ta ta yi baya ta faÉ—i. “Ƴar matsiyata ni za ki taÉ“awa jiki É—an uwarki kinga na miki kama da matsiyatan mutane irin ki? To ba zan taimaka ba É—in ko an faÉ—a miki kuÉ—in a banza nake samun su da zan ke yiwa kowa hidima kamar ban san ciwon kaina ba? Ke kuma ki fice mu tafi gida” Ya faÉ—a yana damÆ™ar hannun Auta da ta yi tsaye baki buÉ—e tana kallon Mahaifin nata..”

 

“Waiyo Allah! Daddy don girman Allah ka taimaka mata kalli fa yadda Mamanta ke rawar sanyi, haba Daddy me ya sa ba za ka taimaka mata ba kuma har kake dukanta? Ni dai ka barni na tashe ta sai mu tafi” Auta ta faÉ—a tana mintsinin hannun Daddy da yake Æ™oÆ™arin janyeta daga gurin..

 

“Ke ba ki da hankali za ki taÉ“a jikinta? Wannan fa tsami take ki rabu da ita mu tafi gida” Cewar Daddy yana Æ™oÆ™arin janta.. Fir Auta ta kafe ta ce ba fa inda za taje sai ta tashi Amra dake Æ™asa a yashe, haushi ne ya kama Daddy ya É—auke cak ya sata a cikin mota yana ta masifa. Da sauri Auta ta buÉ—e schoolbag É—inta ta fito da biskota gida uku da kuÉ—i ta dubi Daddy ta ce” To ka bari na bata wannan tun da ba za ka taimaketa ba.” Dafe kai Daddy ya yi bai kuma ce mata komai, ganin haka ya sa Auta ta balle murfin motar ta fito da gudu-gudu ta iso inda ta bar Amra zuwa lokacin ta tashi tana kusa da Mamanta tana rusar kuka. “Amra! Ta kira sunanta da É—an Æ™arfi ganin hankalinta baya inda take. Juyowa ta yi tana kallon Auta bata amsa ba sai binta da kallo da take.. Murmishi Auta ta yi ta miÆ™a mata kayan hannunta ta ce” Ki yi haÆ™uri da abin da suka miki Amra Allah zai saka miki ga wannan kici wannan kuÉ—in kuma ki kai Maman naki Asibiti kinji” Ta faÉ—a da muryar tausayi.”

See also  Dr. Ahmad Hausa Novel

 

Itama Amra murmishin ta yi ta miÆ™a hannu ta amsa sannan ta ce” Na gode Auta kina da kirki ba zan manta dake ba a rayuwata.” Jinjina kai Auta ta yi ta ciro zoben dake hannunta mai kyau ta kalli Amra ta ce” Bani hannunki nasa miki zobe ina so ki za ma Ƙawata.” Ba muso ta miÆ™a mata hannunta wanda Æ™uraje Æ™anana suka fito a yatsotsin nata wasu har sun yi ruwa kuÉ—a nata bin hannun. Cikin tausayawa Auta ta kalli hannun ta ce” To ki riÆ™e karki saka tun da naga Æ™uraje sun fito miki ki sayi magani kisha sai su mutum zan ke sawa direba ya biyo nan dani dan nake ganinki.” Jinjina kai Amra ta yi tana zubar da hawaye da Æ™yar ta ce” Na gode Ƙawata.” Ba komai Auta ta ce kana ta miÆ™e ta mata bye bye sannan ta koma cikin motar direba yaja suka bar gurin….

 

Sai da taga tafiyar su sannan ta miÆ™e da Æ™yar tana dafe kwankwasonta da yake mata zafi. “Wash Inna Æ™ila Æ™ashin kwankwasona ya karye” Ta faÉ—a tana buÉ—e kwalin buskotar..

 

ÆŠago da kan Inna ta yi tana jera mata sannu ta tashe ta, kafaÉ—arta ta shiga ta taimaka mata ta miÆ™e. Napep ta tsayar ta ce masa ya kaisu kyamis mafi kusa, kallon Amra mai Napep É—in ya yi yana done hanci, tsaki yaja yana ce mata taya zai dauketa tana tsami salon ta kashe masa kasuwar shi ga mota da mutane biyu.. Kuka Amra tasa ta durÆ™usa ta ce” Ka taimaka ka kaimu kaga Innata bata da lafiya magani zan sayo mana ko nawa kake so zan baka ina da kuÉ—i.”

 

Wani kallo ya kwatsa mata ya yi gaba abin shi..

 

Kuka sosai take tana riÆ™e da Inna sai neman faÉ—uwa suke, sai da ta gaji da tsayuwa sannan ta samu wani ya daukesu ya kaisu kyamis….

 

Tun da suka bar gurin Auta ta murtuke fuska tana kumbura baki, shi ko Daddy ko a jikin shi sai ma faÉ—a da yake mata akan biskotanta da ta bai wa Amra….

 

 

Suna zuwa gida Auta ta fito a guje ta nufi ciki tana kuka..

 

Kicibus ta yi da Fadila da ƙawayenta biyu sunsha kwalliya suna wani ɗage kai..

 

“Ke dalla can jaka daga gidan uban wa kike yanzu?

 

Auta ta tsayar da kukan da take ta É—ago kai tana saba baki ta ce” Anty Daddy ne.”

 

“Kuma dan Daddy ne ya sakaki kuka sai ki shigo mana afujajan kamar wadda ta gudo daga Dawanau? Nifa kin sani bana son iskanci za ki wuce ko saina bangajeki daga hanyar? Ta faÉ—a tana nuna mata hanya..

 

Wani kukan Auta ta kuma sakawa tana sakin schoolbag ɗinta a ƙasa ta kuma ƙarawa kukanta sauti.. Tass tass ƙaran marin ya daki dodon kunnen Direba da yake ƙoƙarin shugowa da ƴar Teddyn Auta. Waro idanu ya yi yana ja da baya jikin shi na rawa..

See also  Ruwan Jakara Hausa Novel Complete

 

“Kai kuma munafiki uban me ka shigo yi cikin palonmu? Cewar Fadila tana jefa masa gorar ruwan da tasha rabi ta bar rabi..

 

Kuka Auta ta Ƙwalla tana riÆ™e kuncinta cikin jin zafin marin ta sunkuya ta É—auki schoolbag É—inta tare da nufar hanyar cikin palon, har ta kusa kaiwa palo ta dawo ta isa gurin direba ta amshi Æ´ar Teddynta, kallon Fadila ta yi ta ce” Muguwa azzaluma Allah ya isa ban yafe miki sai na faÉ—awa Daddy” Tana faÉ—in haka ta kwasa a guje ta shiga ciki.”

 

Kanbu! Ni ki ka cewa muguwa? Zan dawo na haÉ—u dake yau zan ga mai rabamu dake a gidan nan, ba dai Mommy bata nan ba zan yi maganinki” Cewar Fadila tana girgiza jiki ta yi gaba suka bi bayanta.. Tana zuwa saitin mai gadi ta ce” Kai kuma ÆŠanladi sai na sa Daddy ya koreka daga aiki tun da in na ce ka wanke mini mota ba za ka yi ba ko?

 

HaÆ™uri ya shiga bata amma taki ko kallon shi ta shige mota ita da Æ™awayenta, kiÉ—a suka konna kana taja suka bar gidan a guje kamar za su tashi sama…

 

Misalin Æ™arfe 11pm na dare Daddy na zau ne yana duba wata jarida, Fadila dake gefe ta kunna kallo ta kawo MBC2 tana kallon wani American film ana ta nuno wasu masoya suna rungume da juna, Auta dake kan stamp ta rafka tagumi tana kallonsu…

 

Da fito ya sanyo kai cikin palon, shi kuma na bayan shi ya shigo yana waka da turanci kiÉ—a na tashi a cikin wayarsa..

 

“Oh my god! Daddy yaushe ka shigo gari ne ba ka faÉ—a mana ba?” Cewar Sudas yana miÆ™awa Daddy hannu.

 

Dariya Daddy ya yi ya ce” My Son’s ai dama surprise na muku daga ina haka?”

 

Wani juyi Sauban ya yi tare da yin rawa ya iso gaban Daddy ya bashi hannu suka tafa, kallon su Auta ta yi sai kuma ta yi saurin saukowa tana murna ta nufo su. Tana zuwa saitin Fadila tasa Æ™afa ta taÉ—eta ta faÉ—i tim a Æ™asa. Sudas ya yi saurin juyowa ya ce” Kai Auta bi a hankali mana har kina faÉ—uwa.”

 

Kallon Fadila Auta ta yi bata ce komai ba ta miÆ™e ta isa gurin Sudas ya É—aurata akan cinyar shi ya yi yana shafa guiwar hannunta da take mata zafi…

 

” Sannu Auta Mommy bata dawo ba?” Cewar Sauban yana danna wayar shi…

 

Bata cewa kowa komai ba har suka gama surutun su suka rabu da ita…

 

MiÆ™ewa Fadila ta yi ta wuce É—akinta, Auta ma ta miÆ™e ta nufi É—akinta. Tana hawa kan stap taga Æ´ar Teddynta tasa hannu ta É—auketa ta wuce É—akinta…

 

Tana shiga ta faÉ—a kan gado sharar hawaye…

 

Ƴar Teddynta ta rungume tana ci gaba da kuka har bacci ya kwashe ta..

 

Bata fi minti goma da soam bacci ta farka, saukowa ta yi daga kan gadon riƙe da ƴar Teddynta ta buɗe ƙofa ta fita..

 

ÆŠakin Fadila ta nufa tana mutsitsika idanu, tana isa ta shiga buga Æ™ofar da Æ™arfi tana faÉ—in” Anty Fadila ki buÉ—e mini Æ™ofa.”

 

Cikin bacci Fadila taji ƙaran buga ƙofar ta miƙe, a fusace ta nufi ƙofar ranta na tafasa, tana buɗewa ta faɗo ɗakin ta takure a guri ɗaya..

 

Galala ta saki baki tana kallonta, wani É“akin ciki ne ya rufe Fadila ta janyo cazar wayarta ta soma tsula mata tana faÉ—in” Dan uwarki uban me za ki mini a É—aki ni z.. Bata Æ™arasa ba taji an yi caraf da hannunta an zafga mata wani gigitaccen mari wanda ya yi sanadiyar É—aukewar jinta da ganinta na wani dakikun…

 

 

 

 

_*Maman Nusaiba ce*_



Muna dauke da Littafan marubutan Hausa…

 

​

 

 

Name: [Aljanar Gidan Mu Hausa Novel Complete]
File Type: Download Novels as .TXT .PDF .DOC (WPS) .HTML
Uploaded By: www.mynovels.com.ng
Category: Hausa Novels Documents
Tags: #Hausa Novels Documents #Hausa Novels Books Complete Hausa Novels #Hausa Novels #Hausa Novel #Romantic Hausa Novels #Sabbin littafan hausa
Novel Price: Free
Last Modified: October, 2022

 

 

Idan Kuna Bukatar Hausa Novels Audio Ku Shiga anan Kana ku danna Subscribe a tashar My Novels TV

Zaku iya sauke Manhajar Android ta My Novels anan Domin samun littafan Hausa maras adadi


Zaku iya shiga WhatsApp Group namu na My Novels anan domin samun Littafan Hausa Maras adadi


Domin samun littafai a saukake su shiga group namu na Telegram


Powered by: www.mynovels.com.ng

Leave a Comment

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Scroll to Top