Amatulmaleek Hausa Novel Complete

Abokiyar Nishadi YouTube channel and Meerah Herbs present you the sweetest story#

AMATULMALEEK
Mamuhgee
#ZafafaBiyar

1
BismillahirRahmannir Raheem

Shiru tayi tana sauraron yanda muryar kawunta ke tashi sbd yanda yake daga sautinsa cikin fushi da bacin rai,
Fushi da bacin rai ne sosai tareda gajiyawa bayyane a fuskarsa datake a hade Babu sauki ko rahama ko kadan,

Duk wannan fushi da bacin ran tareda daga sautin mahaifiyarta Dake zaune tana sauraronsa yakewa,

Daga ita maaman har ita ‘yar tata datai girman da ciwo takeji sosai aranta a duk lokacinda aka zaunar da mahaifiyarta ana mata irin wannan fadan takeji Babu Wanda ya dago acikinsu ya kallesa bare tankawa fadan dayaketa tada jijiyar wuyansa Yana yi,

Shi kansa kawu bellon akoda yaushe ransa tsananta Kuna da Baci yakeyi a duk lokacinda zaizo ya ringa zazzaga kwandon masifarsa a gabansu Amma Babu Me tankawa acikinsu Seya gama maama din ta bisa da yayi hakuri kawai,ita JANNAT ko kanta Bata dagowa bare tai magana.

Wannan Karan fadan nasa da maganganun nasa sunyi tsauri akansu Dan haka idanuwanta Dana maama din duk sun ciko da kwallan da Babu dayansu dakeson yaga hawayen Dan uwansa.

Zufan goshinsa ya share da babbar rigar jikinsa cikin maimaitawa maaman kalman karshe yace

“Tabbas idan Abdulhameed ya sake zuwa makarantar bokon Nan aka kawo min qararsa wlh tallahi almajiranci zan Kaisa bazan iya da baqin ciki ba ‘dan uwana ya mutu be barmun komaiba Se lalurarku,
Idan bazaki tsaya inda Allah ya ajiyeki ba keda yayanki to ki tattara ko qara gaba bazamu iya ba”.

Juyawa yayi yabar gurin batareda ya Dena masifa da fadan da yake yi din ba harya bar kofar qaramin sashen nasu da Tin bayar rasuwar mahaifinsu suke su kadai cikinsa.

Numfashi maamah din ta sauke batareda Kalli gefen da AmatulMaleek din take zaune ba itama tana cigaba da dinkewa Abdulhameed wandonsa Daya barke da allura duk Bata Wani iyaba sbd shekarunta Basu Kai ta iya din sosaiba.

Dukkaninsu Babu Wanda yace komai sbd AmatulMaleek din tsananin zurfin cikinta yayi yawa duk da yarintarta Amma sosai ta iya danne abu ta boyesa a ranta.

Maamah datasan AmatulMaleek din ba magana zatai ba sai kawai ta hadiye hawayenta sbd kada ma AmatulMaleek din ta Gani ta miqe daga zaunen datake ta nufi kayan wankin data fitar masu shegen yawa tafara yi.

Satar kallanta AmatulMaleek tayi tareda ajiye allura da zaren hannunta tana zubawa maamah din fararen idanuwanta batareda tace komaiba,

Abu Daya ne koyaushe yake yawo aranta shine idan har Mommy ‘yar uwar maamah dince meyasa koyaushe Se dai a Turo musu kaya da abinci Amma takasa rabasu ta daukesu daga wannan azabar rayuwar wulaqanci da tozarcin da suke ciki a hannun dangin mahaifinsu,

A duk lokacinda abincinsu ze qare qaninta dayake qanqani sosai bara yake zuwa yayo ya samo abinda zaici su kuwa Se dai su wuni su kwana ahakan Kokuma maamah tayiwa matan gidan aikin abincinsu na dare idan ta gama a San mata Wanda zataci da ‘yayanta.

Babban mamakinta a duk ranar da aka kawo musu kayan abinci daga gurin mommyn a ranar ake taruwa a rarrabe komai abarsu da Wanda iyakacinsu kwana biyu ya qare sun koma cikin tsanani..

A rayuwar dasuka taso gidan dayake dauke da iyayensu Maza yanne da qannen mahaifinta kowannen da iyalinsa daga me mace biyu sai me mace uku harma dame hudu Dan haka gidan yake na taro,

Kowa acikin gidan kansa ya sani sai iyalansa,
Babu me iya taimakawa Wani sbd kowa nauyin dayake kansa ma yafi karfinsa Dan haka kusan rayuwar kowa tasa ta fishesa akeyi.

Su biyar ne manyan gidan Maza Kuma kowannensu Yana cikin gidan da nasa iyalan Babu Wanda ya bar gidan duk kuwa da zaman matsuwa da akeyi a gidan,

Babanta shine qaraminsu gaba Daya Kuma shine yayi karatun Boko Kuma shi kadaine yake aikin gwamnati a primary school din Dake qauyen nasu wanda Babu yanda baayi dashi yabar kauyen yaje abasa Wani aikin Amma yakasa tafiya anan yake vice principal har manyanci yaxo ya rasu yabar matarsa da ‘yarsa Daya AmatulMaleek dakuma jaririn qanin Amatun Wanda aka mayar masa sunan mahaifinsa Abdulhameed.

Kafin rasuwar Babah rayuwarsu acikin gidan ahalinsu me suna Sanda Fulde rayuwa ce data bambamta da duk ahalin gidan sbd gata da kulawa da Babah ke Basu itada mahaifiyarta,
Babah baitaba raayin Kara aureba sbd matsi da rayuwar gidan take ciki dakuma ganin yanda tarbiya ma Neman gagara takeyi ga Yan uwansa sbd yawan iyalai duk da kusan da yawa yaran gidan shine yake dauke da lalurarsu sbd nasu iyayen bazasu iyaba ba hali Kuma ahakan bawai sun Dena haihuwar bane.

AmatulMaleek itace hasken idon mahaifinta sbd burinsa da buqatansa na son kebantar da tarbiyarta daga sauran yaran gidan da tarbiyarsu takeda qaranci duk da Yana iya kokarinsa gurin Basu tarbiyar Amma Yana yi ne iyayensu na warwarewa Dan haka ya tsayu sosai Akan tasa ‘yar wadda yake burin tata rayuwar ta ingantu dama sauran kannanta da zasuzo Dan haka baiyi qasa a gwiwa ya Sakata karatu Wanda kaf gidan a mata ita kadaice ta shiga karatun bokon.

Ya rufe idanuwansa tareda kunnuwansa ga duk abinda zaa fada akan ‘yarsa da rayuwar Daya zabar mata Dan haka ita kanta AmatulMaleek din ta taso tamkar miskiniya Bata Hulda ko iya shiga mutane sosai hakama Bata iya fita daga sashensu zuwa kowane sashe agidan sbd sunyi yawan sosai a gidan da kusan daga Wani bangaren idan zaka Wani bangaren sai Wani acikin mazan gidan ya tare yarinya ya lalatata a hanyoyin gidan dasukeda duhu wasu lokutan,
Da yawa yaran gidan wasunsu sun lalace ne a tsakaninsu Wanda haka ake rufe idanuwa ana daura musu aure da junansu.

Wannan shine Mafi girman abun Dake daga hankalin Babah da maamah akan rayuwar AmatulMaleek data fita daban a cikin yaran gidan Dan haka Sam Babu inda Amatun ke fita idan ba tareda mahaifinta ba Koda kuwa aike ne to tabbas hannunta na riqe dana mahaifinta.

Akwai tsautsayin Daya taba kusan afkuwa ga AmatulMaleek din Wanda shine abu na farko Daya daki zuciyar Babah ya Sakar masa ciwon zuciyar Daya zamar masa ciwon jiki Wanda daga karshe kusan shine ajalinsa.

Daga Aiken Amatun can kuryar gida Wani babban Dan kawunta ya dafeta cikin soron gaba ya rufe mata Baki batareda ya bari ta gansa ba yaso illata rayuwarta batareda laakari da shekaruntaba.

Babah ne da kansa ya riski wanna mummunan kaddarar data Saka Yanke jiki ya Fadi Allah yasa Babu abinda ya faru din AmatulMaleek din ta tsira Dan haka ya tattara masu kayansu itada mahaifiyarta zuwa Abuja gurin ‘yar uwar Kuma Aminiyar maamah sukai zamansu acan sai bayan kusan watanni masu tsayi suka dawo.
Bayan dawowansu zuciyarsa Bata taba samun nutsuwa ko kwanciya ba da rayuwa acikin gidan Kuma ba Dan haka ya kama haya a kusa da gidan ya koma da iyalansa,

Acan rayuwarsu ta inganta hankalinsu ya kwanta a lokacin ne AmatulMaleek tafara wayon sanin alaqar mahaifiyarta da ‘yar uwarta Mommy abeeda wadda gabaki daya rayuwarta data maamah ta bambamta Kuma bambamci me girman gaske.

Da farko Bata taba sanin ba uwa Daya Uba dayane ya haifesu sai daga baya idan sunje gidan mommyn Taga yanda mahaifiyarta ke aiki cikin masu aiki tafara fahimtar tabbas ba uwa Daya ce ta haifesu ba Amma har lokacin tana Saka ran Uba Daya ne ya haifesu.

Kafin rasuwar Babah babu abinda yake daga zuciyarsa tareda cizonta da girmamman kunci irin yanda rayuwa zatayi da AmatulMaleek da mahaifiyarta a cikin Yan uwansa.

Wannan dalilin ya Saka ya Yanke hukuncin karban aikin da ASH TALBA ke bibiyansa dashi tin tini.

Bayan ya karbo offer ta aikin da muhallin zama acan Allah beyi zaiyi aikin ba ciwo ya kwantar dashi Wanda ya zama ajalinsa.

Da farko bayan rasuwarsa Babu yanda Madame abeeda bataiba ta tafi ‘yar uwarta musamman sbd haihuwar datai ko suna baayiba Babah din ya rasu Amma Sam dangin Babah din suka qi yarda sbd Dan abinda yabari sukeso aci dasu Dan haka dole madame ta barta a cikinsu tareda AmatulMaleek wadda take tsarar tata ‘yar qwalli Daya itama.

Rayuwa a gidan da Babah yabarsu tayi musu nauyi sbd qarin kulawa da suke buqata Dan haihuwar maamah din da basuda me kulawa dasu ga ciwo Daya shigeta sosai itama na rashin Miji da haihuwa Amma Babu me kulawa dasu.

Hayarsu ta qare Dan haka tini suka tattara suka koma cikin gidan zuria da suka fito Allah yasa ma Babu Wanda ya shiga bangaren nasu Dan haka suka gyara sukai zamansu.

Tin bayan rasuwar Babah madame tabar qasar tareda mijinta da Daman ba’a qasar yake zaune ba sai dai suzo su koma.

Madame tabar qasar Bata San halinda yar uwarta da ‘yayanta suke ciki ba na qunci da tsananin buqata Kuma Daman kaf itace kadai ke kulawa da Aminiyar tata sbd sune danginta.

Maamah ta taso ne a hannun kakarta Amma mahaifin madame Abeeda ne yake dauke da nauyin duk wata lalurarta sbd mahaifinta kafin ya rasu shine babban yaronsa.

Itada abeeda baitaba bambamta tsakaninsu ba sbd daukansu matsayi Daya a ransa Kuma haka ya tsaya tsayin daka ya Saka musu tsananin so da kaunar juna suka taso tamkar Yan biyu sbd tsananin kaunar dasukewa juna tareda daukan junansu Wani bangaren na rayuwarsu.

Abeeda ma marainiya ce mamanta ta rasu Dan haka a hannun matar mahaifinta ta taso,
Duk Wani karatu tare sukai har matakin secondary Wanda suna shekarar karshe alhaji mahaifin Abeeda ya rasu Wanda Hakan ya kawo rabuwarsu Badan sun dena kaunar juna ba sai Dan lokacin rabuwar da yayi.

Maamah wadda sunanta na Yanka yake Asmau ta koma kauye tareda kakarta inda acan riqonta ya koma hannun dangin mahaifinta itama.

Bayan karatun secondary Wanda Bata qarasa ba Babu Wani cigaba daya sake kusanto rayuwarta har Allah ya kawo Babah Akai mata Auren kauye Wanda ya sake durqusar da rayuwarta gaba Daya zuwa qasa danma Allah yasa ta samu Miji me kaunarta da kulawa kamansa sai rayuwar ta Dan yi mata sauki.

Abeeda kuwa bayan rasuwar alhaji dangin mahaifiyarta itama karbanta sukai da gadonta me tsananin yawa suka bar garin gabaki daya da ita zuwa porthcrt inda acan akaci gaba da inganta rayuwarta cikin gata da kulawa tareda tarin arziki me yawa.

Abeeda ta wuce Malaysia acan tayi karatunta Wanda a daidai lokacin Kuma Asmau tana cikin zuriar Sanda Fulde tana ganin rayuwar Auren da Babu komai acikinta sai hakuri da jarabawa bayan jarabawa.
##MAMUH
Regular 700
Vip 2k
0022419171 access bank Maryam sani
09033181070
Abokiyar Nishadi YouTube channel and Meerah Herbs present you the sweetest story#

AMATULMALEEK
Mamuhgee
#ZafafaBiyar

2
Nisan dayake tsakanin Asmau da abeeda Bai taba rage kauna ko girman junansu ba a zuciyarsu,
Babu dawowar da Abeeda zatai Nigeria Bata zo har kauye ta ziyarci Yar uwar tata ba Dan haka kusan kaf dangin mijin asmaun Babu Wanda baisan girman alaqarta da kaunar Dake tsakaninta da Abeeda ba,

Duk wata sutura da abincin datake ci Daya bambamta Dana Yan kauyen duka abeeda ce ta tsaya Mata akansu Koda Bata qasa ko tana qasar duk lokaci bayan lokaci sai an aikowa da Asmau abinci da suturar datake sakawa.

See also  Zurfin Ciki Hausa Novel Complete

Acan dangin mahaifiyar abeeda Babu Wanda Bai gama sanin matsayin kaunar Dake tsakaninsu ba Dan haka Babu Wanda yayi yunkurin hanawa saima tsayuwa da sukai akan inganta rayuwar asmaun duk da tana kauye Dan haka itama asmaun Bata da tamkarsu.

Nisansu Bai hanasu zama abokan sirrin juna ba Dan kuwa Babu matsalar Asmau da abeeda Bata saniba kamar yanda asmaun Babu damuwar abeeda da Bata saniba.,

Rashin samun haihuwar Asmau da wuri yasaka Abeeda ta samu Samar dauko asmaun ta tafi da ita ganin Wani likita a porthcrt,

Da farko hankalin Asmau Bai tashi ba da rashin haihuwarta ba Amma ganin yanda abeeda ta damu ta kwallafa Rai Akai sai hankalinta ya tashi Wanda yasaka dole aka tsaya aka ringa yawon asibiti da asmaun.

Kamar yanda hausawa sukace ita dai kaddara yashi ce ko an dunkulata Bata dunquluwa, Abeeda ta tsaya da karfi da dukiyarta an nemawa Asmau lafiya Bata samu nutsuwa da Kwanciyar hankaliba Saida Asmau ta wayi gari ta samu ciki a jikinta.

Cikin Asmau nada wata biyu Aka kulla Auren Abeeda da Wani ‘dan babban Aminin mahaifinta Aleeyu Muh’d Talba Wanda dagashi har ita bawai suna son juna bane Amma dayake Auren na connection ne Basu damu ba.

Auren Abeeda da Aleeyu aure ne na fitowar Rabon haihuwa kawai Wanda Allah ya kaddaro a tsakaninsu sbd Auren da wata uku Allah ya karbi ransa sanadin jinyar ciwon cikin kwana Daya kacal.

Bayan rasuwarsa ranar da Abeeda ta fita takaba ranar Asmau ta haifi AmatulMaleek wadda taci sunan Abeeda Amma suke kiranta da AmatulMaleek din sbd shine sunan da mahaifinta yafiso din Dan haka take amsa sunan AmatulMaleek din Amma a rubuce Abeeda AmatulMaleek ne sunanta.

Abeeda Bata samu zuwa haihuwar AmatulMaleek ba sbd itama tana fama da tsohon ciki me tsananin wahala Wanda ya Sakata shiga ciwo sosai.

Asmau duk da jegonta bata zaunaba haka taxo ta zauna jinyar abeeda harta samu sauki itama ta qarasa watanninta ta haifi ‘ya mace itama take aka Saka mata sunan ASMAU Amma ana kiranta da Husnah.

A ranar da akai sunan Husnah a ranar aka daura Auren Abeeda da ASHRAF MUH’D TALBA ‘dan uwan Aleeyu Wanda suke Yan biyu batareda sun taba ganin juna ba Amma hakanan zuciyar abeeda tafi kamuwa da son Ash Talba akan Aleeyu sedai Kuma halin Aleeyu ya bambamta sosai da ASH Dan haka zamanta dashi yafara Bata wuya ta bangarora da dama.

Wanna shine damuwar data fara Sako Auren Abeeda a gaba sedai Kuma Asmau ta tsaya sosai gurin Bata qwarin gwiwa Dan ta fuskanci aurenta ta tsaya ta riqe mijinta da kyau.

ASH baida raayin Auren mace biyu Bai taba shaawan Hakan ba Dan haka a zuciya da gangar jikinsa ya amshi abeeda dari bisa dari sedai rashin fuskantar halin juna da sanin juna yanda ya kamata yake azabtar da Auren nasu Amma Kuma kasancewar sunada ilimi dukkaninsu ya Saka Basu taba nunawa junansu gajiya ko gazawa da zamanba bare juna ba,

Matsalar datafi quntatar da Auren nasu shine rashin iya kulawa da soyayyar Auren Abeeda wadda Sam ta kasa yanda zata iya shiga zuciyarsa ta mallakesa ta hanyar kauna ko soyayyarta.

A idanuwansa tana iya hango tsananin girmamawa ne kawai yake mata Babu wata soyayyarta bayan Hakan Dan haka ta dage sosai dan ganin ta mallakarwa kanta zuciyarsa da Babu kowa a cikinta.

A duniya da yawa basusan ba Ash ne mahaifin Husnah ba kaman yanda Babu Wanda yasan matar Ash din bashine ya fara aurentaba.

Zamansu me dadi da Kwanciyar hankali da wayewa suke rayuwar aurensu Dan haka ya dauketa daga kasar suka tafiyarsu inda yake rasuwarsa tareda mahaifiyarsa da kanwarsu qwalli Daya wadda ta kasance tana gida bayan auranta Daya mutu ta fito da saurayin ‘danta Wanda ya girma sosai Yana karatu Shima.

Duk Nisan da Asmau tayi da Abeeda Hakan Bai Hana ASH yiwa Asmau farin sani ba sbd shaquwa da kusancinsu hakama da kansa ya fahimci irin girman junansu a zuciyarsu Dan haka yake respecting Asmau sosai tareda Mai gidanta Wanda yaso ya taimakawa sosai Amma Babah din yaqi yarda da Hakan Dan haka sai kawai mutunci da kusanci suka ya shiga tsakaninsu duk da Hakan ya taimakawa babah din sosai.

 

Bayan shekaru sunja sosai a rayuwar kowannensu Abeeda tayi nasarar shiga zuciyar ASH sedai batada tabbacin ta mamaye zuciyar ne duka Amma ko a iya inda ta samu din a zuciyarsa tanada tabbacin babu Wani guri da wata zata samu shiga sbd ita kanta gurin data samu a zuciyar tasa sai data share shekaru a cikin auren kafin ta samu wannan gurin a zuciyarsa Dan haka ta tabbatarda zuciyar ASH ba guri me saukin samu ga kowace mace ba.

Baida raayin mata kaman yanda baida Wani raayi ko time na abubuwan dasuka danganci soyayya bayan ta matarsa Abeeda wadda yake ganin iya sonta da ita din ta ishesa a rayuwarsa Bata buqatan Qari sbd baida Wani gurin bawa wata macen a rayuwarsa kwata kwata.

Rayuwar Abeeda ta sauya ne ta tashi daga arzikin mahaifinta ta koma arzikin mijinta Wanda ya take ya rufe arzikin mahaifinta datake ganin yanada ta gado,
A familyn ASH kusan shi kadaice me irin wannan arzikin duk da mahaifiyarsu ma nada arzikin Amma ba kamar na mahaifinsu da suka gada ba.

ASH da Aleeyu mahaifinsu daban Wanda bayan rasuwarsa mahaifiyarsu tayi aure ta haifi Aysha wadda ita mahaifinta daban dasu Amma dai mahaifiyar tasu Daya ce.

Sune masu arziki sosai sbd mahaifinsu shine me arziki sabanin Aysha da nata mahaifin baida Wani abun bayan rufin asiri.

Da wannan qyashi da Jin zafin Aysha ta tashi a cikinsu har Allah yasa Akai mata aure ta haihu ta fito daganan aurenta uku tana fitowa karshe dai ta hakura da auren sbd takasa samun masu iri arzikin ‘dan uwanta ASH dashi kadaine yanzu ya rage mata hakama ummansu ta rasu Dan haka ta tattara itada ‘danta NAUFAL ta suka dawo karkashin ASH tamkar shine Uba mahaifin Naufal duk Wani gata da Jin dadi Babu abinda basa samu a gidan karshe dai kusan gidan ya dawo hannun mom Aysha kaman yanda ake kiranta da girma yazo mata sbd ta girma Abeeda sosai ba laifi Dan haka kusan gidan idan aka cire Mai girma me gidan the grt ASH TALBA mom Aysha itace me fada a ji Dan kusan kamar matsayinsu Daya agidan Ash itada abeeda.

Rayuwar mom Aysha a cikinsu ya Saka duk yanda kusancin Asmau da abeeda yake yafara raguwa sbd mom Aysha Asmau ce macen datake Jin har cikin zuciyarta Bata kaunar kusantuwarta da Yan ahalin gidan Dan haka tsauri da kaidojin mom Aysha akan Asmau yasa taji Bata shaawan zuwa gidan Abeeda Koda suna gari Dan haka da wannan kusancinsu yafara raguwa dakuma manyanci Daya zo musu dukkaninsu.

Bayan haihuwar husnah Abeeda Bata sake haihuwa ba Saida manyanci yaxo musu ta haifi ‘da namiji Wanda ya kasance a gurin ASH TALBA shi kadaine jininsa Amma Kuma a zuciyarsa haydar din da Husnah matsayinsu Daya Dan kuwa ita kanta Husnah duk da ta girma batasan ba ASH TALBA mahaifin Daya haifetaba.

AmatulMaleek tanada shekaru goma sha uku a duniya maamah ta sake haihuwar ta haifi qaninta Abdulhameed Wanda harya girma baisan mahaifinsa ba tinda kafin sunansa Babah ya rasu yabarsu cikin halin qaqanikayi.

Rayuwarsu ta zama me Wani irin babban gibine da basusan tayaya zamu cikesaba ko samun me cike musu shi,
Qunci da wahala da yunwa da azaba tareda hantara suke rayuwa acikinsa har Abdulhameed ya girma yayi wayo,
Tunda tagama primary karatunta ya tsaya,
Abdulhameed kuwa karfi da yaji ya zama kamar almajiri sbd ko suturar da zai Saka basuda ita sai abinda Allah ya Basu kawai suke Samu.

A gidan kaf Babu Wanda yake iya Basu abincim da zasuci sbd kowa ta kansa yakeyi kowa na fama da rashi.

Madame abeeda wadda a yanxu matsayinsu da sunansu ya zarce na Baya sbd matsayin da ASH yake dashi a gurin Al’ummar Dake tsananin son ya tsaya musu a matsayin gwamnan jahar Amma baida raayin siyasa duk da Hakan jamaa sosai sukeyinsa Dan haka kusan Babu Wanda baisan the grt ASH TALBA ba.

Rayuwarsa data iyalansa kwata kwata baa qasar yake yinta ba sai dai yakan Fi iyalan nasa zuwa Dan haka jamaa sukeyinsa sbd taimakon dayake bayarwa kaman baisan zafin dukiyar ba Dan haka manya da yawa mutanensa ne hakama talakawan ma mutanensa ne hakama masu kudin Dan haka kowa yinsa yakeyi duk da da yawa baisanma sunayi ba Amma Kam sosai aketa Daman gwagwarmaya da rigimar shi akeso amma Sam Baya raayi.

Ta bangaren matarsa Abeeda kuwa wadda duniya ke kira da Madame abeeda Talba tini rayuwarta data ‘yayanta ta zama abin kallo daga nesa sbd tsaron da ake Basu bana wasa bane sbd ASH Bai hadasu da komai nasa ba Dan haka a yanzu tsakaninta da maamah aike ne kawai Shima sai can idan lokaci me tsayi yaja Dan haka itama maaman ta hakura ta rungumi marayun ‘yayanta.

 

*****Bayan rasuwar Babah da shekara biyu kawu bello ya aure Maamah din wadda bayan wahala da ukubar data ringa sha a hannun kishiyoyi Babu abinda suka Qaru dashi itada ‘yayanta
Ahakan suka ringa Shan kuncin rayuwa har kawun ya gaji ya saketa sbd yace bazai iyaba lalurar tai masa yawa Dan haka dai anan cikin gidan Akai auren anan Akai sakin taci gaba da gwagwarmaya itada ‘yayanta Wanda tanaji tana Gani Abdulhameed yakoma almajiri AmatulMaleek kuwa haka take zaman gidan Bata taba barinta fita ba Koda zuwa cikin gidan sbd yanda gidan yake sake zama hadari sosai ga duk Yan matan gidan da Yara qanana ma Dake tasowa duk da yawa sun lalace a tsakaninsu batareda sanin iyayensu ba.

AmatulMaleek tinda tafara wayo rayuwarta ta zama tamkar kurma sbd rashin magana tinda basuda abin magantuwa akansa Dan bayan tarin kunci Babu komai a rayuwarsu Dan haka ta taso a miskilar gaske Wanda Hakan yafiwa maamah dadi da farin ciki sbd kullum kukan maamah a gaban Allah shine yanda zata bawa ‘yayanta kariya daga masifar gidan musamman AmatulMaleek datake mace.

AMATULMALEEK
Regular 700
Vip 2k
0022419171 Access bank Maryam sani
09033181070

#MAMUH#
#LA HOT
#LIFE
#ASH TALBA
#AMATULMALEEK
#NAUFAL TALBA
#MEERAH HERBS
#ABOKIYAR NISHADI TV CHANNEL

Abokiyar Nishadi YouTube channel and Meerah Herbs present you the sweetest story#

AMATULMALEEK
Mamuhgee
#ZafafaBiyar

3
Maamah Bata taba yin qasa ko sanyaba akan tsaro da tarbiyarsu kaman yanda babansu ya dage ya tsaya kafin rasuwarsa duk da ta Wani bangaren dukansu har ita suna cikin hadari a gidan Dan ita kanta ansha shigowa bangarensu da dare da niyar a afka musu ko ita ko AmatulMaleek din Amma dai Allah na tsaresu shiyasa duk tsanani basa fitowa fitsarin dare gudun a keta musu haddi basuda abin yi Dan duk Wanda aka Bata gidan bayan hakuri Babu abinda zaiyi bawai Kuma Dan baa San masuyi din ba kawai dai bakada iKon magana ne ayita rigima da iyayensu ana Allah ya Isa da tashin hankali karshe dai cuta ce anriga an cuceka.

See also  Gabe Na Hausa Novel

Maamah Bata taba Dana sani da damuwar aure a gidan taro me tsanani ba irin wannan sai yanzu sbd illarsa tafi dadinsa da albarkarsa yawa,
Amma dai tinda Allah yasa rabonta na ‘yaya anan yake Babu yanda zatayi da kaddara bayan dagewa.

Ko islamiyya Bata barin AmatulMaleek tafiya ita kadai kullum tare suke zuwa lokacin tashi nayi taje su dawo tare duk da ta Dan girma Amma dai hankalinta baitaba Kwanciyar tabarta taje ita Daya ta dawo ita Daya sbd yawun da samarin gidan suka hadewa ‘yartata Dan haka tasan ko a hanya zasu iya binta.

Ita kanta AmatulMaleek tasan rayuwarta a gidan tana cikin hadari Dan haka take kiyayewa tareda kame kanta Babu inda take taba zuwa Dan haka wasu da yawa a kauyen Basu Santa ba sbd Bata fita koyaushe tana dakin maamah ana tsaronta kamar wata gwal me tsadar gaske.

Abdulhameed Daya kasance qaninta shi Kuma sai ya zama kowa shi ya sani sbd shi Kam yawonsa yake zuwa yi tinda bara yakeyi duk da Shima Maamah din na kokari akansa Amma dai tafi Maida hankali akan Amah,
Yaron ya kasance Yana so da shaawan karatun Boko Dan haka kullum saiyaje makarantar bokon kauyen ya shige cikin Yara
Wannan dalilin ne yasa ake yawan kawo kararsa ga kawu bello sbd sunyita korosa Amma Baya Dena zuwa Dan haka kawun keji Asmaun da ‘yayanta sun ishesa Daman kuka aure yakeson qarawa duk da manyancinsa sosai Dan haka so yake Asmau ta tattara tabar gidan ya samu bangaren sbd ya aje yar bazawarar da zai auro.

*****
Asmau tayi shekaru sosai rabonta da Abeeda a idanuwanta sedai aike Wanda Wani lokacin har mantawa akeyi dasu kafin su samu Wanda daga Yan Aiken ne da aka aje duk wata sukai musu abinci Amma Sam basa kaiwa sai bayan watanni watanni suke kaiwa ganin madame din Bata qasar sai Suma suke tasu zalamar.

A yanzu da AmatulMaleek tafara zama yar budurwar yarinya tini hankalin maamah yabar jikinta Bata bacci Batada nutsuwa kowane dare Bata iya baccin kirki sbd tsoron rayuwar da ‘yarta zata shiga a yanzu da samarin gidan da babu nagari zasu iya cewa suna son aurenta kuma tasan batada abinda zai Bata damar hanawa tanaji tana Gani zaa lalata mata rayuwar ‘yarta gashi kowannensu yaga budurwa tafara tasawa a cikin gidan sai suce sunaso gashinan da qananun shekaru sunata Tara mata daga me mace biyu Se uku sbd suna cewa sunaso akeyin wuf ayi auren sbd karfafa zumuntar da Babu so ko jin qai a cikinta.

******
Iyalan ASH TALBA sun sauka a kasar Nigeria a bazata sbd rasuwar mahaifin mom Aysha wanda yake tamkar mahaifin ASH din Shima Dan haka dolensu suka dawo Nigeria.

Saukarsu da labarin rasuwar tasa yasaka Maamah shiryawa dole itada ‘yayanta sukai Shirin tafiya duk da batada kudin mota Amma hakanan ta siyar da akuyoyinta guda biyu datake ta Reno sbd auren AmatulMaleek idan zaizo kafin lokacin sun qara hayayyafan da zasu isheta yiwa AmatulMaleek din Wani abu.

A wulaqance aka siyesu sbd anga tanason kudin amma Bata damu ba sbd zuciyarta Sam bamai Saka damuwa bace hakama Allah yayi mata sanyin hali da tsananin hakuri me yawa Dan haka baka gane ko ka quntatar da ita sbd tana hadiye komai da sanyin halinta.

AmatulMaleek da batajin dadin tafiyar tasu Sam Amma Bata nuna ba itama sbd kusan halin mahaifiyarta itace ta dauko sak na boye damuwa da hadiye kowanne bacin Rai da sanyin hali Dan haka itace da maamah din sukai wankin kayansu da zasuce tsumma ne ma Amma Kuma su suke dasu Dan haka dasu zasu.

Abdulhameed kuwa farin ciki yakeyi sosai sbd baitaba barin ko wajen kauyen ba bare zuwa babban birni ba dukda baimasan me birnin ke nufi ba Dan shi Kam asalin bafulatanin kauye ne.

AmatulMaleek din ma dai kana ganinsu kaga fulanin kauye sun fito Amma Kuma nutsuwarta ke Hana duhun kansu fitowa.

Ranar da zasu tafi gidan kaf murna sukeyi su tafi sbd bangarensu da kowa keso saikace ce musu maamah tayi bazata dawo ba,
To sukam Koda zata dawo din to idan ta dawo sedai ta koma zauren gidan da zama Dan kuwa duk Wanda ya shiga baida niyarnta gidan sbd AmatulMaleek dasuka qwallafawa Rai akan tana Isa aure zasu aureta su jefa cikin matansu.

Duk Wani Shirin tafiyarsu sun kammala Dan haka washe gari tinda asuba suka hau mashin Abdulhameed na gaba maamah da AmatulMaleek a Baya suka fita kauyen zuwa kauyen gabansu da acan ake Hawa motar zuwa babbar hanyar titi da acan Kuma zasu hau motar zuwa cikin state din kafin daga can su hau motar zuwa Abuja.

Tinda suka hau mashin din Abdulhameed ke washe Baki cikin tsananin farin ciki sbd Bai taba Hawa ko Keke ba bare mashin sai yau din.

Tafiya me Dan tsayi sukai kafin suka Isa kauyen kurmawa,
Saukowa sukai daga kan mashin din maamah na ajiye jakar kayansu gefe
Ita Kuma AmatulMaleek Abdulhameed Dake zare idanuwa Yana kallan koina ta kamo hannunsa suka dawo gefen maamah din.

Kudinsa Maamah ta Ciro ta basa na mashin ya juya Yana musu Allah ya kiyaye Abdulhameed ne kawai ya amsa da Amin cikin murna da farin cikinsa da Baya boyuwa.

Wata motar a Kori kura suka nufa wadda ita kadai ce Daman a kauyen take fita da mutane Dan haka kusan Tama cika Dan haka ba Bata lokaci aka kama su Abdulhameed din da AmatulMaleek aka Dora a sama kafin Maamah ta miqawa Amatu jakarsu tukuna itama ta tattara zaninta ta kama motar ta Haye ta zauna gefen ‘yayanta suna Dan gaisawa da sauran mutanen Dake bayan motar a Bude kowannensu kura ta gama rife koina jikinsu kaman anyi juyen yashi a jikinsu sbd iska da akeyi.

Tafiya suka fara Babu me magana acikinsu sai Abdulhameed Dake kalle kalle har bacci ya daukesa a jikin AmatulMaleek wadda itama tafara komawa kamar bokanya sbd iska da qura Dayake Kara sauya kamannin kowa Dake motar.

Tafiya me tsayi Nan ma sukai sosai kafin suka iso babban titin hanyar shiga kauyukansu masu shegen Nisa.

Saukowa sukai kowa qafafunsa sunyi sanyi gashi zuwa lokacin Rana tayi Dan kuwa sha Daya saura Dan haka komai Basu tsayaba ruwa kawai da biredi kawai maamah ta Siya musu suka fada wata motar da zata kaisu state acan su samu shiga motar Abuja.

Babu Bata lokaci motar ta cika Dan haka suka sake daukan hanya.

Biredin data Siya musu ta rarraba musu suka fara cin abinsu hankali kwance.

Abdulhameed duk rawar murnarsa fara komawa ciki tayi sbd zuwa lokacinda suka Isa babbar tashar yola tsoro kamasa yayi sosai sbd Bai taba ganin mutane hakaba sosai da hayaniya anata ihun Neman passengers ta bangare daya ga masu talla takoina suna ihun azo a Siya abinda suke tallan,
Hakama a Wani gefen fada akeyi sosai a cikin tashar..

Ba Abdulhameed ba AmatulMaleek ma kanta tsoro ne da firgici me tsananin gaske ya shigeta Dan Basu Saba haka da mutane da wannan hada hadarba Dan haka dukkaninsu qanqame hijabin maamansu sukai ita Kuma ta riqe hannuwansu gam tana Basu kariya har suka samu motar da zata daukesu zuwa Abujan suka shiga ta rungume ‘yayanta tanajin hakanan zuciyarta na karyewa da tafiyar Kuma a yanzu sbd so da dama duk halinda take ciki a kauyen sai tanajin yafi mata nutsuwa akan zuwa birnin duk da wannan tafiyar taji hankalinta ya kasu kashi biyu zatayi ne sbd magana da Madame Abeeda ta rage nauyin zuciyarta da quncin Daya dabaibayeta akan rayuwar AmatulMaleek da batasan Yaya zatai da ita acikin zuriar Sanda Fulde ba.

Shiru tayi tareda Nisa a tinanin rayuwarta tin kuruciya da irin gatan data samu a Baya da rayuwar data taso aciki har kaddararta ta sauya mata hanya zuwa kauye da auren kauye Wanda ayau ta samu kanta a tsaka me wuya sbd rashi na Miji Kuma uban ‘yayanta Wanda da ace Yana Raye da bazata samu Kanta a wannan halin na kakanikayi da ‘yayanta.

AmatulMaleek Dake jin tsoro me tsananin gaske a duk Nisan da suke qarawa na tafiyar shiru tayi jikin mahaifiyarta tana Jin zuciyarta na shiga yanayi na rashin murna da tafiyar dakuma yanayi na sanyi Dan haka ta rufe idanuwanta tana barin baccin datake ji daukanta.

Kallansu maamah ta sake bayan dukkaninsu sunyi bacci jikinta ta shafa kansu su dukan tana Bude zuciyarta cikin amincin Allah tace

“Allah ya kawo madaukakin haske da girma a rayuwarki AmatulMaleek keda ‘dan uwanki,
Allah yasa ki zama tauraruwar macen alfahari a duk inda rayuwa zata kaiki,
Yakuma Baki mijinda zai Miki Mafi girmamman so me tsaftan gaske..Amin”

Numfashi ta ajiye ahankali itama tana lumshe idanuwanta sbd zuciyarta Dake jin kaman tana gazawa da gwagwarmayar.

****
Tafiya yankin azaba kaman yanda aka fada,
Sai yamma lis suka sauka birnin Tarayya,
Daga maamah har su duka kafafunsu sunyi Wani irin nauyi da riqewa Dan haka daqyar dukkaninsu suka iya tsayuwa bayan sun fito motar zuwa lokacin Abdulhameed da AmatulMaleek sosai suke Jin tsoron mutane Dan haka a maqale suke da maamah wadda itama tasan bazata iya Kai kanta gidan ASH TALBA ba Dan haka numbern Madame Abeeda datake cikin kanta kamar hadda ta karanto aka kira musu ita cikin rashin saa akaita kira baa dagawa sbd basa daga bakuwar lamba Dan haka dole guri suka samu a tashar suka zauna ana sake kira lokaci bayan lokaci.

Yunwa da wahala ta Saka AmatulMaleek ringa Amai a gurin har Saida dole aka nemi guri aka kwantar da ita sbd take zazzabi ya rufeta.

Sanyi jikin Maamah yayi ga Abdulhameed Shima duk yayi laushi sbd azabar tafiya da yunwa Dan haka duk taji hankalinta ya tashi damuwa na rufeta ta zuwan nasu.

Sallar magrib ake kokarin shiga Wanda yaketa kira musu numbern ya ringa mata fada Yana cewa wayace suzo batareda sun sanar da inda sukazo din ba?
Basusan baa zuwa Kai tsaye gidajen manya ba batareda an sanar musu ba sbd basason damuwa da takurar talakawa da dangin kauye.

Shiru Maamah tayi sbd zuciyarta gabaki daya Bata mata dadi jikinta yariga yayi sanyi gaba Daya Dan haka batama San me zatace ba bayan sauke Kai kasa.

AMATULMALEEK
Regular 700
Vip 2k
0022419171 access bank Maryam sani
09033181070

#MAMUH#
#AMATULMALEEK
#ASH
#MADAME
#FRIENDSHIP
#LA HOT
#ROMANCE
#LOVE
#ABOKIYAR NISHADI TV CHANNEL
#MEERAH HERBS
Abokiyar Nishadi YouTube channel and Meerah Herbs present you the sweetest story#

AMATULMALEEK
Mamuhgee
#ZafafaBiyar

4
Duk fada da masifar daya daga cikin  ma’aikatan tashar yayi mata akan zuwan nata duk da baisan dalili ba bare Kuma alaqarta da Gidan ASH TALBA din datazo gurinsu Amma dai yasan Hakan datai na zuwan Kai tsaye nada hadari.

Kallanta yayi Kai tsaye yace ta Fadi sunanta ya rubuta Sako ya tura mata ga numbern,

Jiki a mace cikin sanyi ta fada masa tareda Dana ‘yayanta wainda yayiwa Wani kallan qyama da takaicin yanda ta kwasosu kaman wasu almajirai sunzo garinda basusan koinaba ko tsoro bataji.

See also  Labarinsu Hausa Novel Complete

Kai tsaye sunanta Dana yayan nata ya rubuta a cikin sakon da cewan a taimaka a dauki wayar gasunan Tasha a zube harda mara lafiya.

Tafiyar sakon ya sakashi kallanta yace ta zauna ta jira idan ankira to shikenan idan Kuma baa kiraba motar asubar safe su koma inda suka fito.

Gyada masa Kai tayi cikin sanyi da nutsuwa tareda Bude Baki ahankali tayi masa godiya ta juya ta koma inda su Amatun ta zauna tana kallansu har zuciyarta bataji komai ba na haushi ko jin zafin rashin daukan wayar harma da fadan da ma’aikacin tashar yayi mata Dan kuwa Babu lefi a cikinsu saima uzuri datakewa kowa Wanda shine abin dayafi bawa mutane Daman cutatar da ita ko acan kauye sbd komai kayi mata a rayuwa tanai Maka uzuri Bata fushi Komai girman cutar da zakai mata.

Zaune suke cikin duhu da rashin mafita hakanan ta miqe tayi alwala a gurin tayi sallah har lokacin AmatulMaleek a kwance take jikinta yafara tsanani sosai Abdulhameed ma tini Shima yafara kamuwa da zazzabin sbd wahalar yunwa.

Har Akai ishai Babu Wani bayanin biyo sakon da suka tura da kira Dan haka ta Yanke komawarta da bin motar asuba Kila Wani uzurin ya Hana Abeeda ganin sakon Dan haka bazasu cigaba da damunta da Kiran ba akwai takurawa ga Hakan ta sani.

Ruwa kawai ta ringa bawa Abdulhameed da AmatulMaleek har kusan asuba anan suka kwana cikin sanyi a sararin iska ga sauri da duhu harma da qwari kala kala Dan haka asuba nayi sallah kawai tayi suka miqe Dan shiga layin bin motar komawa.

Koda gari ya fara haske AmatulMaleek kaman bazata tashi ba hakama Abdulhameed Dan haka sai hankalinta ya rabu biyu ga tafiyar sbd bazasu iya bin doguwar hanya a Hakan Amma Kuma Babu zabi na yanda zatayi Dan haka tayi shiru a cikin sanyin jiki Dana zuciya idanuwanta sunyi jajir da damuwar Dake riqe da zuciyarta.

Isowar ma’aikacin tashar na jiya ne gurinta Yana qwala kiranta ya Sakata dagowa ahankali cikin sanyi ta Dan kallesa tareda sauke Kai tana gaidasa da girmamawa.

Da farin cikin dayake tareda takaici ya kalleta Yana cewa tayi Maza tazo ana son magana da ita anbiyo sakon da kira yanzu.

Numfashi ta sauke me dumi kafin ta fito layin a sanyaye ta biyosa zuwa inda ba hayaniya ya miqa mata wayar wadda daidai lokacin aka sake kira.

Cikin nutsuwa ta Bude Baki tayi sallama nauyin zuciyarta na raguwa Jin amsa sallamar Abeeda cikin Wani irin nutsuwa ta wainda suke cikin duk wata ni’imar rayuwar duniya.

Jin muryar Asmau ya Saka Madame abeeda sauke ajiyar zuciya a hankali tareda sake Bude Baki tace

“Asmau kece??
“Meyesa Baki kirani da wayarki ba?
Yaushe kikazo?
Sai yanzu nake duba sakon sbd Banda time na duba wayar rasuwar da Akai ya Saka Sam bana samun Hutu yanda ya kamata.

Shiru sukai dukkaninsu sbd kowannensu da Wani girmamman quncin dayake mamaye cikin ransa Amma baisan tayaya zai tinkari Dan uwansa ba sbd Nisan daya shiga cikin kusancinsu da tsananin kaunarsu

Numfashi mara sauti maamah ta sake saukewa ahankali kafin ta Dan saki murmushi me sanyi tace

“Eh nice,jiya nazo sbd labarin rasuwar ta alhaji babba danaji daga bakin Dan gidan kawu bello dayake Dan shiga birni shine yazo ya sanar mun,
Allah yaji qansa yayi masa Rahama,
Munata damunki da kira ga fama da jamaa Anata zuwa gaisuwa.”

Numfashi Madame abeeda ta sauke kafin tace

“Ba komai yanzu ku Jira ga driver Nan zan Aiko yazo ya dauko ku keda yaran ai gwara da bakiyi saurin juyawaba Ina buqatan ki Asmau,
Ina tsananin buqatan nawa a kusa Dani”

Shiru suka sake yi jikin Maamah na sanyi ita Kuma acan nata bangaren wasu zafafan hawayen da babu Wanda ya taba ganinta dasu ne suka taru a cikin idanuwanta Amma Bata bari sun taba saukowa kan fuskartaba bare yau din Dan haka ta sake hadiyesu cikin dauriya da karfin zuciya kafin ta kashe wayar ta ajiye gefenta sbd Asmau kamar rauninta ce sbd Bata iya boye mata komai duk dauriya da jarumtarta.

Ita kanta Asmau sanyi jarumtarta ke Neman yi Dan haka ta daure batareda ta dago ba tasake yi masa godiya tana koma gurin yaranta da suka koma kamar mahaukatan almajirai.

Zaunawa tayi tareda zuba musu idanuwanta da suke boye duk Wani abinda yake cin Rai da zuciyarta tana musu fatan hayewa matakin nasara a duk inda suke rayuwarsu.

Zaman jigum tayi tana sauke kanta qasa da jiran tsammanin Kuma Ina rayuwa da kaddara zatai dasu itada yayanta a gaba.

Zaman jiran awa kusan Daya da Rabi tayi zuwa biyu kafin Daya daga cikin Mahaukatan motocin gidan ASH TALBA ta iso tashar daukanta.

Da farko numbern da aka bawa drivern yazo daukanta ya kira shine ma’aikacin tashar ya kawosa har inda Maamah take zaune kaman almajira ita da yaranta yace “gatanan”

Kallanta drivern yayi dakyau kafin ya dawo da kallansa kan mutumin Dake nuna masa ita Yana wasi wasin idan wannan din ce akace ya dauka yakai gidan ASH TALBA sbd ko masu aikin gidan bazasu dauki wannan aikin gidajensu ba bare gidan ASH din da kansa.

Lura da fahimtar tinanin dayake gudana a zuciyar drivern yasaka Dan tashar sake basa tabbacin ita din dai ce,daga kauye ta fito shiyasa.

Kasa cewa komai driver yayi sai kawai ya dauki jakar kayanta ya Bude bayan black range Rover Din dayaxo da ita yana sake kallansu maamah din cikin danne mamakinsa da Dan shakkar idan ba kuskuren daukansu zaiyiba.

Maamah dasu AmatulMaleek ma da basusan inda kansu yake ba rakubewa sukai tareda dunqulewa guri Daya bayan motar Babu me iya motsawa sukai shiru Maamah din najin zuciyarta na Dan sake sanyi da taimakon gaggawar dasu AmatulMaleek din zasu samu Dan kuwa data koma dasu a wannan halin ba lallai ta samu Isa gida da duka yayanta biyu ba Kila ta rasa ran Daya a hanya kafin su Isa,sai gashi Allah ya dubi maraicinsu ya kawo sassauci a lamarinsu ta samun Kiran Abeeda.

Tafiya me Dan tsayi sukai kafin suka Isa,
Koda suka Isa tini sanyin ac yakusan sankarar dasu Abdulhameed Duk da sun Saba da sanyin Allah Amma wannan din yayi musu karfi da yawa sosai.

Babban makeken luxury gate din gidan ASH TALBA aka wangalewa motar gidan dasuke cikinta suka shige harabar gidan datake da Wani irin girma da tsari irin na gidajen turai da Kuma masu abin duniyar qasa da qasa,

Motacin Dake harabar sunkai takwas koma fiye,
Motoci ne wainda babu me karamin kudin da zaka iya lissafawa bare manyan,
Dukkaninsu baqaqe ne sai farare guda biyu aciki sai Ash Daya.

Parking yayi daga gefen da ake ajiye duka motacin gidan Dana mutan gidan Banda na ASH dake gefensu daban sbd ta inda yake fitowa daga sashensa da Babu Wanda yake bin kofar idan ba shi ba Dan haka ta Nan yake fitowa ya shige motacinsa yabar gidan batareda ma kana gidanba bare kasan fitarsa.

Tinda Sharif driver yayi parking ya fito yake Dan Jin zuciyarsa na sake shiga shakku idan baiyi kuskuren dauko Wanda Basu aka aikesa daukowaba.

Bude musu motar yayi Yana kallansu yace maamah tafara fitowa tukuna idan ya tabbatarda sune aka sakasa daukowa saisu shiga.

Wayarsa ya fitar cikin nutsuwa ya Nemo numbern Madame din ya Saka kira.

Saida yayi mata kira biyu kafin ta daga Kai tsaye ya sake gaisheta Yana cewa

“Hajiya ga baqin na dauko Amma bansaniba ko na samu kuskuren daukowa wainda Basu ba….

Katsesa Abeeda tayi da cewa

“Bata wayar naji”

Da sauri ya miqawa Maamah wayar Yana cewa “yi magana taji”

Karban wayar maamah tayi tana sallama Abeeda ta kashe wayar tareda miqewa daga zaunen datake ciki lafiyayyan bedroom dinta sanyeda jallabiya ash da mayafi me Dan girma na sallanta ta ajiye wayarta tana nufar kofar barin bedroom din sanyeda slippers masu tsananin laushi da tsadan kudinsu zasu ciyar da maamah din da yayanta na sati uku koma fiye.

Tinda ta tinkaro babban palonta ta nufo kofa ma’aikatan Dake gyaran palon suka ringa gaisheta cikin tsananin girmamawa sun Dan sauke Kai sbd Koma me zai fitarda Madame din harabar gidan a daidai wannan time din me tsananin mahimmanci ne.

Sharif dayaji madame ta kashe wayarta Babu amsar komai Shan jinin jikinsa yayi sbd ta tabbata kenan yayi kuskuren dauko wainnan kauyawan dajin.

Kallan maamah yayi cikin sauri Yana cewa

“Kinga maza shiga na mayar daku inda na daukoku kafin na Rasa aikina”

Juyawa mota maamah tayi tana kokarin komawa batareda tace masa komaiba Dan itama batasan dalilin kashe wayar Abeedan ba.

Cikin fada da daga murya yaci gaba da yi mata sauri sauri Yana cewa

“Wai bazakiyi sauri ba muje?
Kema kinyi gangancin biyoni bayan kinsan Babu ta inda kukeda arzikin Azo daukanku da mota irin wannan Amma haka kawai kika biyoni gashi Kuma Kinga irin gidan da akazo bazaki Bude Baki kice bakuda Hadi da irin wanna guraren”

Shiga motar Maamah ke kokarin saiga fitowar Abeeda harabar gidan tini ta dagakata daga shiga motar tana tsayuwa a inda take gabobin jikinta na Neman saki idanuwanta dasukai Dan ja suna tsayuwa a kan Abeeda wadda itama nata idanuwan akan Maamah din suke tana kallan Wani irin mugun mummunan yanayin da Asmaunta ke ciki kamar wadda Tayo gudun hijira.

Suturar jikinta ta kalla taji hankalinta na mummunan tashi kafin ta tsayar da idanuwanta akan fuskar Asmaun da sauran kadan takoma skeleton sbd rama da bushewa.

Maamah kasa kurar da nata kallan tayi kan Asmau sbd alkunya da muzantar dataji tanayi agaban Abeedan sbd yanayin datazo gidan dashi kamar almajirar data debo tafiyar qafa.

Qasa tayi da kanta lokacinda Abeeda ta tinkarota Kai tsaye jiki a tsananin mace da baqin cikin ganinta ahakan tana isowa hannunta take kokarin kamowa tana ambatar sunanta muryarta na rawa sosai.

Kasa bari maamah tayi Abeeda din ta a kamata sbd jikinta Babu inda yake da tsafta ita kuwa tamkar wata tauraruwar datafi taurari take komai nata na musamman ne sbd Jin dadi,Hutu da daular da Allah yayisu acikinta.

Sharif na ganin Hakan yasan ba kuskuren ne dai aka samu ba Dan haka a Jere ya Sako ajiyar zuciya Yana Bude mota da sauri yahau kokarin kamo Abdulhameed sbd AmatulMaleek bazata dauku garesa ba tinda ta fara zama yar budurwa.

Yanda Sharif ya dauko Abdulhameed kamar matacce ya Saka gaban Abeeda mummunan faduwa tana kallan Motar cikin tashin hankali tace

“Meya samesa?
Ina AmatulMaleek?
Meya samesu?”

Jiki na rawa murya na sauri sharif yace

“Ahaka aka daukosu daga Tasha inaga basuda lafiya sosai sunyi Nisa musamman ita macen ko numfashi ma batayi…””

Bai qarasaba Abeeda ta katsesa da cewa

“What??

Kallan maamah tayi tana Isa motar jikinta na rawa takai hannunta kan AmatulMaleek Dake kwance ba Rai ta janyota kafin tayi Wani yunkuri tini sharif ya kira masu aikin gidan mata su biyu suka iso gurin Dan daukan AmatulMaleek Dan baiyi tinanin Madame din tasu zata iya taba mutanenba.

Leave a Comment

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Scroll to Top