Anya Baiwa Ce Hausa Novel

Anya Baiwa Ce Hausa Novel

 

 

 

 

 

 

 

 

 

Tag: ANYA BAIWA CE?

 

Na

 

*AMEERA ADAM*

 

 

_LITTAFIN NAN NA KUÆŠI NE DA NAIRA 200 ZAKI KARANTA SHI CIKIN KWANCIYAR HANKALI, GAME BUƘATAR VIP POSTING SAU BIYU A RANA ZAI BIYA 400, GABAÆŠAYA ZAKU BIYA TA WANNAN ACCOUNT ÆŠIN, FIRST BANK 3090957579 AISHA ADAM ZA’A TURO DA SHAIDAR BIYA TA WANNAN LAMBAR 0706 206 2624,DAN GIRMAN ALLAH IDAN KINSAN ZAKI FITARMUN DA LITTAFI NA YAFE CINIKINKI._

 

 

FREE PAGE 1

 

 

 

Tafe take tana ɗan waige dan gudun kar wani ya ganta ko taci karo da wani a hanya, saboda abin da ta gano take san zuwa ta isar da shi ko ta samu ɗan alheri, aikuwa batayi aune ba tana shiga soron tsakiya suka yi gware da mutum a zabure ta ja da baya tana sauke ajiyar zuciya kamar wacce tayi tseren gudu, kallan tsaf yayi mata yana karantar yanayinta yasan tabbas akwai abinda ke ƙunshe cikin bakin ta, aɗan diriri ce ta kalle shi ta ce.

 

“Yautai mugun tsuntsu masha miyarka sai yayi dare”

 

Kallanta yayi sai da yayi murmushin gefen baki yana Æ™ara karantar yanayin ta sannan ya ce, ” Tauraruwa mai wutsiya…, Kura kike ga tsoro ga ban tsoro. Ina zaki kike sauri kina ta juye-juye haka? ” Sai da ta juya hagu da dama ta kuma leÆ™a soron Æ™arshe tana mai miÆ™a wuya cikin Æ™asa da murya ta ce, ” Gobara daga teku maganin ta sai Allah, wata Æ™ura ce take Æ™oÆ™arin kunno kai a cikin gidan nan amma karka ce kaji daga baki na ” ta Æ™arasa magana tana kuma duba gabanta da bayanta.

 

“Jakadiya Kubura kenan, ay harbi ga É—an jaki gado ne, kuma iya ruwa fidda kai gayamun ina sauraron ki kowa ya biya allon sa ya wanke ” ya faÉ—a cikin son jin labarin.

 

Sunkuyowa tayi dabda shi sannan ta ce, ” Kasan koda girgiza kurna tafi magarya, mai tsoron a mutu shi yake maho ” Ƙara gyara tsayuwarta tayi sannan ta ce, ” Ƙaramar kyauta tafi babbar rowa ” ta Æ™arasa faÉ—a tana miÆ™a masa hannu alamar ya bata wani abu.

 

Ya gano abinda Jakadiya ta ke nufi, dan haka ya sa hannu cikin aljihu ya É—ebo mata silallah ya zuba mata akan hannun ta yana faÉ—in, ” Ke dai ciki kike mai manta kyautar jiya, kuma Kura kike mai manta alherin baya”

 

Juya su tayi cikin jindaÉ—i ta kunto bakin zaninta ta É—auresu tana faÉ—in, ” Domin rana É—aya ba’a Æ™in zuguri, kuturu da kuÉ—insa alkaki sai na Æ™asan langa, buÉ—e kunnen ka yanzu zaka sha labari, ashe Fulani Zaliha ciki gareta har ya girma, kasanta da shegen nunkufurci ba ta cika bada fuska a shiga sashenta ba ” zaro idanu yayi waje shima yana waigen bayansa sannan ya ce, ” Lallai tsugunne bata Æ™are ba ansai da kare an sayi Mage, naji daÉ—in wannan albishir naki jeki anjima zan neme ki ” ya faÉ—a yana yin gaba abinsa.

 

Jakadiya Kubura ta fahimci sarai inda maganar Galadima ta dosa har yaje bakin Æ™ofa ta ce masa, ” Injunan ka sammako wani tafe ya kwana, kuma hargagin É—an damisa bashi tsorata Namijin zaki, ka taka a sannu kasan Fulani Maryama ba kanwar lasa ba ce ” kamar bazai bata amsa ba sai kuma ya juyo ya ce mata, ” Tabbas inkaji mutum na tsoron dare ba’a É—aure shi ya Æ™wance bane, Ki bar ganin allura Æ™arama itama Æ™arfe ce, dan haka bazan ce miki komai ba mu zuba mu gani kowa tasa ta fishsheshi ” yana gama faÉ—a ya sanya kai ya fice daga cikin soron.

 

Bin bayansa tayi da mugun kallo sannan ta ce, ” Mai Æ™afa huÉ—u ma ya faÉ—i bare mai biyu, ajuri zuwa rafi wata ran tulin zai fashe ” tana faÉ—a ta juya ta cigaba da tafiya, kai tsaye sashen Fulani Maryama ta nufa.

 

Tana shiga ta zube Æ™asa cikin salon kirari ta fara magana, ” Barka da hutawa Uwargida na bango madafar bayi, uwar marayu uwar mara gata mai iyayenma kin gamai musu komai, Ƴar sarki jikar sarki Matar Sarki kuma gaki Uwar Sarki, Allah ya Æ™ara girma ya raya mana Yarima mai jiran gado, Mulki da Sarautar Masarautar Kano gaba É—aya ta ku ce, Mai Uwa agindin murhu bazai ci miyarsa lami ba… ” murmushi Fulani Maryama tayi saboda jin daÉ—in kirarin da Jakadiya tayi shiyasa ma ta katse ta da faÉ—in, ” Jakadiya anjima zan turo da saÆ™on maÉ—i mai ke tafe da ke?? ” russunar da kai Jakadiya tayi tana mai sauya yanayin fuskarta cikin damuwa ta ce, ” Tuba nake Uwar gijiyata banzo dan isar da mugun labarin nan dan wata manufa ba sai dan ki tashi tsaye ki É—au mataki kuma asan abin yi, Kaicona da tuntuni ban ankare ba har lamarin ya girmama, amma dukda haka ba za’a rasa abinyi ba dan ba’a rasa nono a riga, ina mai neman gafarar ki saboda labarin bamai daÉ—i bane ranki shi daÉ—e ”

 

Tunda Jakadiya ta fara magana Fulani Maryama gabanta ya yanke ya faÉ—i saboda tasan labarin bazai mata daÉ—i ba, shiyasa a hargitse ta wurgo mata tambaya, ” Jakadiya banasan Kewaye-kewaye tafi kanki tsaye, Me yake faruwa ne?”

 

Jakadiya kara sauya muryarta tayi ta ce, ” Ina neman gafararki da jin kalamai na dama Fulani Zaliha ce ke da juna biyu, kuma ayanayin dana lura har yayi Æ™wari…” cikin tsananin tashin hankali Fulani Maryama ta Æ™unduma wani ashar sannan ta ce, ” Aikin me kike tun tuni baki sanar dani ba tunda wuri? ”

 

Jakadiya ta bata amsa da, ” A gafarce ni Uwargijiya ta kinsan Yarinyar da nunk…”

 

Katseta Fulani tayi cikin tsawa ta na faÉ—in, ” Ya isa haka, Lallai Fulani Zaliha ta É—ebo ruwan dafa kanta, Samun sararin kuturu gaÉ—a a cikin rama, wato haka ta miÆ™e Æ™afa da yawa? Lallai abinda ya faru a shekarun baya dole ya Æ™ara faruwa yanzu, tabbatas dole labari ya Æ™ara maimaita kansa, Aikuwa kowa yaci tuwo dani miya yasha, tashi kije Jakadiya anjima zan neme ki bayan Sallar Isha’i ”

 

Jakadiya najin haka ta kuma rissinawa ta ce, ” ALLAH ya huci zuciyar Fulani, Ramin kura da wuyar shiga a gayawa kare yayi hankali, tabbas bakin rijiya ba wajen wasan makaho bane wace ce Fulani Zaliha da zata iya haÉ—a sahu da Uwar É—akina, ni mai bin Umarnin ki ce akowanne lokaci ” Jakadiya na gama faÉ—a ta tashi ta fice zuciyarta fess saboda tasan ba Æ™aramin alheri zata samu ba.

 

Tunda Jakadiya ta fito daga ɗakin, Fulani Maryama ta kasa zaune ta kasa tsaye sai kaiwa da komawa take, abun duniya gabaɗaya ya isheta, ita kaɗai sai saƙa da warwara ta ke tana san nemarwa kanta mafita, Jaririnta ɗan kimanin wata biyar da ke kwance ta je tasa hannu ta ɗauke shi tana juya shi cikin zuciyarta da shawarar da ta yankewa kanta.

 

A fili ta fara surutai kamar wata zautacciya, ” Yarima yanzu kai ake shirin yiwa kishiya a gidan nan, tabbas bazata yuwu ba tunda ban bari wata ta haifi namiji ba dole na dakatar da cikin Zaliha ”

 

Jakadiya tunda ta fito daga sashen Fulani Maryama kai tsaye sashen su ta wuce tana zumuÉ—in sauraron kiran da Fulani Maryama ta ce zata yi mata, kamar wacce a ka mintsina tashi tayi ta fito daga sashen bayi wani gida ta faÉ—a bakin ta É—auke da sallama, ” Balaraba matar Ciroma dake tankaÉ—e ta amsa mata sallamar tana faÉ—in.

See also  Rayuwar Saleema Hausa Novels Complete

 

” Yau kuma Jakadiya ce da doshin magariba haka?? ” Kujera Jakadiya ta janyo ta zauna sannan ta ce, ” Eh ko bakya maraba da zuwan nawa ne?? ” cigaba da tankaÉ—enta tayi ta bawa Jakadiya amsa, ” Ni na isa nace banten Sarki yayi É“urtu, ai hanyar lafiya abita da shekara, meye labari?? Dan nasan bakin ki baya rasa motsi?? ”

 

Murmushi Jakadiya tayi ta ce, ” Ai dama ni kujera ce dole a zauna dani, kuma abokin cin mushe ba’a É“oye masa wuÆ™a, wai kuwa kinsan Fulani Zaliha na É—auke da juna biyu?? Wa ya sani ma itama ko Namijin zata haifo ni zanso ma ta haifo Namijin naga yanda Fulani Maryama zatayi ” ta faÉ—a tana Æ™asa-Æ™asa da murya.

 

Da sauri Balaraba ta saki rariyar Hannunta waigawa bakin Æ™ofa tayi sannan ta cewa Jakadiya, ” Da gaske kike wannan maganar?? aikuwa muddin zancen nan yaje gun Fulani Maryama kinsan bazai mata daÉ—i ba, kuma kinsan dole wani abu ya biyo baya”

 

Jakadiya Æ™ara matse bakin zanin ta tayi ta ce, ” Ai a bakin wawa akanji magana, wai da kunne yaji muguwar magana wuya ya tsere, kinsan dai ai ciki badan tuwo akayi shi ba, bayan ke babu wanda yasan da wannan maganar ”

 

Tsuke fuska Balaraba tayi da alama bataji daÉ—in maganar Jakadiya ba dan haka ta maida mata da martani, ” Tafasar tukunya bata gefe É—aya bace, haka nan abinda baki ya Æ™ulla hannu bashi iya kunce shi, idan kinji makaho ya ce ayi wasan dutse to tabbaci haÆ™iÆ™a ya taka dutse, Jakadiya koma dai mene ne daga bakinki wannan maganar ta fito kuma ni nan da kika gani na iya taku na”

 

MiÆ™ewa tsaye Jakadiya tayi tana gyara É—aurin zaninta ta fara takawa har sai da taje wajen bakin Æ™ofa sannan ta juyo ta ce, ” Mutum fari ne shi ke rina kansa ya zama baÆ™i, bakinki dai Æ™anin Æ™afarki kuma harshenki linzaminki ” bata saurari mai Balaraba zata ce ba ta fice daga gidan.

 

 

_UMMOU ASLAM BINT ADAM

[18/07, 8:16 am] : *FIRST CLASS WRITERS ASSO

 

 

*ANYA BAIWA CE?*

 

Na

 

*AMEERA ADAM*

 

 

_LITTAFIN NAN NA KUÆŠI NE DA NAIRA 200 ZAKI KARANTA SHI CIKIN KWANCIYAR HANKALI, GAME BUƘATAR VIP POSTING SAU BIYU A RANA ZAI BIYA 400, GABAÆŠAYA ZAKU BIYA TA WANNAN ACCOUNT ÆŠIN, FIRST BANK 3090957579 AISHA ADAM, ZA’A TURO DA SHAIDAR BIYA TA WANNAN LAMBAR 0706 206 2624, DAN GIRMAN ALLAH IDAN KINSAN ZAKI FITARMUN DA LITTAFI NA YAFE CINIKINKI._

 

 

FREE PAGE 2

 

 

 

Da daddare Bayan sallar Isha’i Jakadiya ce tafe tana lalube har ta Æ™arasa sashen Fulani Maryama, da sallama ta shiga ta russuna tana cewa, ” Barka da hutawa Uwar É—akina ance kina san ganina yanzun nan ”

 

Fulani Maryama dake tsaye hannunta É—auke da Salman miÆ™awa Jakadiya shi tayi ta ce, ” Jakadiya inasan muyi tafiyar sirri kamar yanda muka saba da ke a shekarun baya, ayau basai gobe ba zamu kai ziyara ga Boka Marduska, saboda bazan iya kwana da maganar da kika sanar da ni ba, batare na nemi mafita ba ”

RiÆ™e Salman Jakadiya tayi tsam kamar wani zai Æ™wace shi sannan ta ce, ” Duk abinda kika ce haka za’ayi, bani da ikon bijirewa umarninki, da kai da kaya duk mallakar wuya ne ”

 

Fulani Maryama na gama jin haka ta juya ta shiga cikin ɗakinta, cen ƙasan adakarta ta buɗe ta ɗauko wani kurtu tasa hannu ta ɗebo waɗansu irin wuri guda biyu da wani ɗan ƙaramin zobe, maida kurtun tayi sannan ta dawo gurin da tabar Jakadiya ke tsaye.

 

MiÆ™awa Jakadiya Wuri É—aya tayi sannan ta fara karanta waÉ—ansu irin É—alasiman tsafi, ba’a É—auki lokaci ba sai wani haske ya mamaye gurun atake suka É“ace daga cikin É—akin.

 

Tsaye suke abakin wani kogon dutsen dake cikin wani surÆ™uÆ™in daji mai matuÆ™ar duhun gaske, Fulani Maryama runtse idanunta tayi ta fara Æ™walawa bokan kira har sau uku, ” Marduska! Marduska!! Marduska!!! ” tana gama faÉ—a ta buÉ—e idanunta.

 

Ji sukayi ankece da wata mahaukaciyar dariya sai da aka É—an É—auki lokaci anayi sannan aka tsagaita, sannu a hankali haske ya mamaye gurin, cikin wata irin murya aka fara basu umarni, ” Ku sanya Æ™afafunku cikin waccen Æ´ar Æ™oramar sannan ku tako ku shigo ciki.

 

Kamar yanda aka gaya musu haka suka bi umarnin mai magana sannan suka shiga cikin kogon dutsen, daga cen nesa suka hango shi zaune akan buzun damisa, gaba ɗaya jikinsa lulluɓe yake da gashi tamkar ba bil Adam ba, Fulani Maryama na gaba Jakadiya na biye da ita a baya.

 

Zama sukayi sannan Fulani ta kalli bokan zata fara magana ya É—aga mata hannu sannan ya kuma kecewa da dariya, sai da yayi mai isarsa sannan ya fara magana,

 

” Ai duk wanda ya bamu iska dole kwaÉ“arsa tai ruwa, Maryama kin É—auke mana Æ™afa na wasu shekaru sai da buÆ™atarki ta tashi zaki waiwayo mu ”

 

Fulani Maryama ta russunar da kai ta ce, ” A gafarceni sarkin bokayen duniya, nayi kuskure awancen lokacin amma yanxu baza’a sake ba ”

 

” Na amshi tubanki kuma nasan abinda yake tafe dake, kalli nan ” ya janyo wata Æ™warya mai cike da jini yana nunawa fulani.

 

Tana leÆ™awa Fulani Zaliha ta gani kwance akan gadon ta tana baccinta hankali kwance, jinjina kanta tayi ta cewa Murduska, ” Ya babban boka sarkin bokayen duniya so nake a salwantar da cikin da ke jikinta inda hali ma akashe su gaba É—aya, domin bayan Salman bana san kowacce matar sarki ta sake haihuwa acikin su saboda bansan gaba mai zasu haifo ba kuma bansan mai hakan zata haifar ba ”

 

Ƙwala-Æ™walan idanunsa ya kafe ta dasu yana ce, ” Daga ganin Sarkin fawa sai miya tayi zaÆ™i, badan kinzo ayanxu ba da tuni sauran damar data rage miki ta Æ™are gaba É—aya ” A zabure Fulani Maryama ta ce, ” Ban fahimce ka ba Marduska ”

 

 

Wani mudubin tsafinsa ya É—auko yasa wata jelar É“auna dake hannun sa na hagu cikin Æ™waryar ya yarfawa mudubin, inuwar wani É—an Æ™anÆ™anin Yaro ce ta bayyana na É—an wani lokaci sannan ta É“ace, maida mudubin yayi gefe sannan ya maida kallonsa ga Fulani Maryama ya ce, ” AlÆ™alami ya riga da ya bushe, duk duniya babu wani ko wata da zai iya dakatar da cikin jikinta har sai ta haifeshi, Zata haifo ÆŠa namiji Mai kama sak da Mahaifinsa kuma koda baki ci wannan Alwashin ba haihuwa ta dakatawa Sarki Aminullah, duk wacce kika ga ta kuma haihuwa sai dai in wani ne mahaifinsa ba Aminullah ba ”

 

Cikin damuwa Fulani Maryama ta ce, ” Yanxu babu wata mafita da zaka bani ya Shugaba na?? ”

 

Wani Allon jar ƙasa ya ɗauko ya jingine ya na faɗan waɗansu irin kalmomi, yana watsa wani tafasashen jini dake cikin wani ƙoƙon kan Ƙwarangwal, yana cikin haka baiyi aune ba sai gani sukayi Allon jar ƙasa ya ruguje wani irin hayaƙi mai wari na fita daga jikinsa.

 

A tsorace gaba É—aya suka ja baya Marduska ba Æ™aramin tsorata yayi da ganin faruwar haka, cikin yanayin firgici ya fara magana, ” Tabbas Ruhin wasu ababen hallita na katange da shi, idan na matsanta halaka shi ba mu ba hatta Aljanun da suke taya ni aiki sai sun halaka, maganin kar ayi kar afara inba haka ba wanda baiji bari ba yaji woho ”

See also  Siddabaru Hausa Novel Complete

 

Fulani Maryama jikinta ne ya gama sanyi amma duk da haka zuciyarta bata karaya ba ta ce, ” Marduska abar batun Halaka shi tunda ni kaina ganau ce ba jiyau ba, amma bayan haihuwar sa ba damar a aiwatar da wani aiki akansa ko a nakasa shi? ”

 

Matsawa yayi bakin wutar dake ci ya ɗebo wani garin magani mai haɗe da garin naman mage da haƙoran jemage ya zuba aciki, take wutar ta kuma tashi sama sannan wata ƴar ƙaramar ƙorama ta bayyana aciki, daga cikin ƙoramar wasu litafan tsafinsa ya ɗebo guda biyu ja da baƙi, baƙin ya fara jefawa cikin wannan jinin dake cikin ƙwarya sannan ya zura kansa yana karewa Ƙwaryar kallo dake ta zaɓalɓala.

 

Sai da ya gama kallo tsaf sannan ya É—ago da kansa da yayi gumi sharkaf ya fara mata bayani, ” Tabbas cikin biyun za’a iya gudanar da É—aya amma biyun bazasu iya wanzuwa akanshi ba, zamu iya nakashi ta kowacce siga haka nan zaki iya sawa a fitar dashi daga cikin masaurautar, amma shi ne kuskuren da zaki fara tafkawa a rayuwar ki, domin kuwa ta wannan silar dukkan asiran da kika binne za’a binciko domin kuwa allura ce zata tono garma”

 

Fulani Maryama harta fara jin daÉ—i Æ™arshen maganarsa ya sa ta shiga damuwa, kallansa tayi cikin rashin fahimta ta ce, ” Bangane mai kake nufi ba? ” mayar da Æ™waryar yayi cen gefe ya ce, ” Abinda na gani kenan zaÉ“i ya ragewa mai shiga rijiya…, kowanne zaÉ“i kika É—auka yana da nashi Æ™alubalen da zaki fuskanta ki nutsu da kyau ki saurare ni inba haka ba zakiyi gudun gara ki faÉ—a gidan zago ”

 

Jakadiya dake gefe tayi tsuru sai raba idanu ta ke cikin zuciyar ta ta ke faÉ—in, ” Lallai Fulani Maryama kema ba Æ™aramar makira ba ce, amma ajuri zuwa rafi…, Ay bahaushe ya ce inzaka gina ramin mugunta gina shi gajere, amma lallai wannan ÆŠa na Zaliha ya zama kainuwa dashen Allah, wata Æ™ila shi ne zai zama magajin mulki muga ta tsiya, dama ance kayun ÆŠan Æ™warai ya gaji Ubansa ”

 

” Ina sauraren kowacce kalma da zata fito daga bakinka kuma kowacce zan saka ta amazaunin da ta da ce ” Fulani Maryama ta faÉ—a.

 

MiÆ™e Æ™afafunsa yayi da gaba É—aya gashi ya rufe su sannan ya fara mata bayani, ” Zabi na farko zamu iya baki garin maganin da za’a zuba masa a ruwan wanka ina nufin wankansa na farko a duniya kuma ko yaya ne asamu a bashi wannaa maganin ya sha, sai kuma na turare wanda ita Zaliha tana fara NaÆ™uda zaki turara mata, karki bari yaro ya faÉ—o ba tare da kin turara shi ba, to idan kika yi haka bazai iya gani da idanunsa ba, har tafiya da magana ke komai da kika sani sai dai ayi masa, saboda zai kasance a kwance sai dai duk abinda za’a furta zai ji shi babu abinda zai iya wanzarwa ”

 

Murmushin jin daÉ—i Fulani Maryama tayi ganin haka yasa boka ya ce mata, ” Sai dai akwai sharaÉ—in da zaki kiyaye, akwai ruhin wata da na gani tana jingine da shi, zata shigo cikin gidan masarautar ku tana Æ™asÆ™antacciya muddin kika bari ta shigo cikin gidan sarautar, abubuwa marasa daÉ—i zasu fara faruwa gareki kuma duk ranar da tayi tozali da shi suka haÉ—a ido, a ranar aljanun dake riÆ™e da Æ™afafunsa zasu tarwatse alÆ™adarinsu zai karye, idan kika yi sake ta É—au wani abun ci ko abin sha ta bashi da hannunta to a ranar suma aljanun da ke riÆ™e da bakinsa zasu gushe zai fara magana, sai dai aranar zai fara wani irin ciwo kamar zai mutu zai yi ta amai ba Æ™yaÆ™yÆ™yautawa kamar zai amayar da Æ´an hanjinsa, hakan zai É—aga hankalin Mai martaba har yasa anemo wanda ya bashi wani abu tunda shi zaiyi tunanin guba ce aka bashi, amma ba haka bane amayar da gubar da take jikinsa yake ta tsawon shekaru ”

 

 

 

_UMMOU ASLAM BINT ADAM

] : *FIRST CLASS WRITERS ASSO*

 

 

*ANYA BAIWA CE?*

 

Na

 

*AMEERA ADAM*

 

 

_LITTAFIN NAN NA KUÆŠI NE DA NAIRA 200 ZAKI KARANTA SHI CIKIN KWANCIYAR HANKALI, GAME BUƘATAR VIP POSTING SAU BIYU A RANA ZAI BIYA 400, GABAÆŠAYA ZAKU BIYA TA WANNAN ACCOUNT ÆŠIN, FIRST BANK 3090957579 AISHA ADAM, ZA’A TURO DA SHAIDAR BIYA TA WANNAN LAMBAR 0706 206 2624,DAN GIRMAN ALLAH IDAN KINSAN ZAKI FITARMUN DA LITTAFI NA YAFE CINIKINKI._

 

 

FREE PAGE 3

 

 

Ajiyar zuciya Fulani Maryama ta sauke sannan ta ce masa, ” Wace ce yarinyar? Kuma daga wane gurin zata xo? Babu damar dakatar da zuwan nata? Ya za’ay na gane ita ce dan na É—auki matakin daya dace akanta?? ”

 

Boka ya ce, ” Daga ni har sauran matsafan duniya babu wanda ya isa ya ja da yarinyar domin ita É—in FILSIFI ce, abinda muke kira da FILSIFI kuwa aharkar bokan ci, tarraya ko haÉ—akar shuÉ—aÉ—É—un ruhika mabanbanta daga jinsi Mabanbanta, zo ki duba nan ” ya Æ™arasa faÉ—a yana buÉ—e mata wannan jan littafin da ke gefensa.

 

Zanen wasu matasan mata ta gani guda uku sai dai duk cikinsu babu wacce zanen fuskarta ya fito sosai daga Æ™asan kowacce anrubuta wani irin gwamammen rubutu, ta farko ya fara nuna mata yace, ” Wannan da kike gani ita ce Muhaibish ita ta rayu ne tsawon dubbannin shekarun da suka gabata, Ƴar Sarkin jinsin Fararen Aljanun Æ™arÆ™ashin Æ™asa ce, tunda take bata taÉ“a taka doron Æ™asa ba ”

 

Zaro idanu Fulani Maryama tayi tana mamakin abinda ya faÉ—a, ta biyu ya nuna mata ya cigaba da cewa, ” Wannan kuma sunan ta Kalimsiyat Ƴar sarkin fararen Aljanu ce amma ta nan doron Æ™asa itama ta rayu atsawon dubbanin shekaru, acikin wani littafin bincike na karanta cewar ta yi rayuwa ne tun bayan zuwan Annabi Yusuf (A.S) ita kuma tunda ta ke bata taÉ“a nutsawa Æ™arÆ™ashin Æ™asa ba a matsayinta na jinsin aljanu, kuma ita Kalimsiyat mace ce mara haÆ™uri mai faÉ—an gaske, kuma abinciken da nayi dukkan su biyun kashe su akayi bisa doron zalinci, kuma abinda zai baki mamaki kusan duka ruhinsu guda ne, sai dai banbancin nahiya da zamani.

Sai ta Ukun su ita ce aka ce zata xo aÆ™arshen zamanin nan, sunanta Rayzuta ita ta haÉ—a dukkan abubuwan da waÉ—ancen suke dashi harma da wanda suka rasa, Æ´ar baiwa ce me É—auke da É“oyayyun al’amura, ita kanta batasan da wannan baiwa tata ba.”

 

Yana rufe baki cikin azarÉ“aÉ“i Fulani Maryama ta ce, ” To itama ta ukun nasu Aljanar ce? kuma meye alaÆ™ar su da junan su? Kuma meye alaÆ™arta da gidan masarautarmu? ”

 

” Maryama kenan azarÉ“aÉ“in me kike yi? Ai duk gaggauwar asara ta jira samu, kuma duk gaggawar unguwar zoma ta jira a haihu, mai kike ci ne na baka na zuba inkinyi haÆ™uri sannu-sannu bata hana zuwa sai dai adaÉ—e ba’a je ba ”

 

Murmushin tayi sannan ta bashi amsa da, ” Hmmm Marduska ai Ranar biyan buÆ™ata rai ba’a bakin komai yake ba, na Æ™agu na ji matsayin Yarinyar da ka ce da kuma ya alaÆ™arsu ta ke? ”

See also  Rayuwar Ameera Hausa Novels

 

Marduska ya cigaba da cewa, ” Har zuwa wannan zancen da nake miki ruhin su na nan ya wanzu a dora Æ™asa, sai dai babu inda zasu ya da zango sai akan cikon ta ukunsu, kuma ba kowa bace cikon ta ukunsu sai Yarinyar da nace miki karki sakankance har ta shigo Masarautar ku, har yanxu mudubin tsafi na ya gagara gano mun mutum ce ko kuma itama tana cikin jinsin Aljan, sai dai bincike ya nuna akwai wani É“oyayyen al’amar dake bibiyar jinin zuri’ar sarki Aminullahi ”

 

Damuwa ce Æ™arara a fuskar Fulani Maryama ta kuma jefo masa tambaya, ” Ita yarinyar ba dama ka nuna mun hoton fuskarta yanda zan gane kamaninta? ”

 

Mudubinsa ya janyo ya fara wasu surutai yana watsa masa wani ruwa mai yauÆ™i, wata irin Æ™ara suka ji ta tsagewar mudubin har sai da suka tsorata, cikin damuwa Bokan ya ce, ” Gaskiya gaba É—aya aikin da kika zo dashi akwai damuwa da tashin hankali, haka kawai banci nanin ba nanin zata ci ni, na dakata akan binciken Yarinyar nan saboda ceton rayuwa ta ”

 

Abin duniya gaba É—aya ya dami Fulani Maryama amma duk da haka ba ta gushe ba tana faÉ—in, ” Ka taimaka mun kayimun wani abu, ni da kai kaÉ—ai na dogara ”

 

Wani mugun kallo ya bi ta dashi sannan ya ce, ” Baki da hankali ne a gabanki munanan abubuwa suka faru amma zaki ce na taimaka miki kinga idan kinganni a lahira kaini akai, babu uwar da zan iya taimaka miki, bincike na biyu da zan gaya miki shi ne, idan kika sa aka fitar da shi tun yana jariri to ba makawa acikin Æ™asa da makwanni goma zai faÉ—a gurin da zai gamu da ita wannan yarinya kuma dawowarsu shi da ita bazai miki daÉ—i ba, dabara ta ragewa mai shiga rijiya…”

 

Zufar dake goshinta ta goge sannan ta ce masa, ” Marduska wai dole sai akaina wannan masifun yarinyar zasu sauka? Kaina ya kulle fa, dan Allah ka bani mafita…” katse ta yayi da Æ™arfin gaske yana cewa, ” Da alama kin manta dokar kogon dutsen, azaba ta gaggawa zata iya wanzuwa agareki ” sunkuyar da kai Æ™asa tayi ta ce, ” Tsafi ya dafa tuba nake bokana Sarkin bokayen duniya, ina gwanin wani ga nawa Aljani Garbunsa ya Æ™ara ja da zamanin ka ”

 

Motsa bakinsa yayi alamar jindaÉ—i sannan ya É—auko wani ruwa dake cikin tukunyar Æ™asa ya É—aga shi sama da hannunsa ya fara surutunsa na tsafi, ya jima ahaka sannan ya sauko da shi ya leÆ™a wani tiriri ne yake fitowa, sai da ya gama kallon Æ™waryar ya ce, ” Akwai wasu É“oyayun al’amura mai tafe da sarÆ™aÆ™iya, da alama shuÉ—aÉ—É—un abubuwan baya ne zasu iya dawowa wata Æ™ila Tarihi ne zai kuma maimaita kansa, amma bani da tabbas harsashe ne nayi, Æ™arÉ“i wannan ” Ya miÆ™a mata wata manyan layu sannan ya cigaba da bayani.

 

” Ita wannan layar ki saÆ™aleta aÉ—akinki zata taimaka miki na bunnuwar wasu sirrika na ki, wannan kuma ki binneta akan Æ™ofar shiga gidan masarautarku, bance zata Hana faruwar komai ba sai dai wannan layar zata hana tonuwar muhimmin sirinki musamman akan wance yaran, kinfi kowa sanin dai ba jinin Aminullahi ba ne hasalima ba jinin masarautar Kano bane, to ki saÆ™ale ta gun da kikasan bazata faÉ—o ba, ita wannan ta Æ™ofar gidan wasu aljanune zasu miki gadin bakin Æ™ofar don hana ta shigowa, amma banda tabbaci yaÆ™ini nake watakila shigowar Rayzuta gidan ya sa ta faÉ—owa wata Æ™ila kuma bazata faÉ—o ba, kuma na lura da faÉ—uwar gaba a duk lokacin da zaku haÉ—u da ita wannan yarinyar, sai ki riÆ™e wannan duk lokacin da kikaji faÉ—uwar gaba ki dinga lura da waÉ—anda suke tare da ke, ni nayi iya yi na ku tashi ku bani guri ”

 

Jakadiya dake gefe tsumu tayi najin kalaman boka cikin zuciyarta ta ke faÉ—in, ” Au dama Salman ba jinin Takawa bane? Lallai duk inda makirci ya je Fulani Maryama ta kai cen, babu ko tantama É—an wajen Fulani Zulaiha shi zai zama magajin Izza, muje zuwa mahaukaci ya hau kura na tabbata akwai ranar da Ya zata É—akin Ƙanwa, Fulani Maryama kinyi shuka a idon makwarya, lokaci na nan zuwa da kwaÉ“arki zatai ruwa, tafiya sannu-sannu kwana nesa. ”

 

Kamar Fulani Maryama tasan abinda yake ran Jakadiya aikuwa ta juyo cikin tsuke fuska ta fara mata magana, ” Jakadiya duk abinda kika ji agurin nan ki tabbata da ya zama sirri banasan kowacce magana ta fito daga bakinki, bakinki Æ™anin Æ™afarki, kinsanni sarai kinsan wacce Fulani Maryama bani da kyau banida daÉ—i, idan na sake naji wata magana ta É“illa waje to daga gareki ne, kuma insa a hallakaki ba abu ne mai wuya agurina ba ”

 

Jakadiya sarai ta san Fulani Maryama zatayi abinda yafi haka ma ta rissinar da kai Æ™asa ta ce, ” Wane ni da wannan É—anyen aikin ya Shugabata indai wanda ya mutu zai dawo to maganar nan zata tashi, ai duk wanda ya Æ™ona rumbunsa yasan inda toka take tsada, ina ni ina bayyana sirrin Uwar gijiya ta idan nai haka ai kamar na daÉ“awa kaina wuÆ™a ne ”

 

Fulani Maryama É—auke kanta gefe tayi tana faÉ—in, ” Ki tabbatar da kin kiyaye abinda kika faÉ—a domin ni ginshiÆ™in dutse ce kowa yayi karo dani shi ka faÉ—i, idan kunne yaji gangar jiki ta tsira ” Jakadiya haÉ—iye yawu tayi mai É—aci saboda jin haushin maganar Fulani, cikin zuciyarta Æ™wafa tayi ta ce, ” Tunkafin ahaifi uwar mai sabulu balbela ta ke da farinta, Fulani Maryama dani kike zance wallahi duk wannan wulaÆ™ancin da kike mun akwai lokacin da zan farke miki laya. ”

 

” Muna godiya Ubangidana maganin kuka na dukda yau ce rana ta farko da zan fita daga kogon dutsen bada biyan dukkan buÆ™ata ba, amma ni mai bin umarnin ka ce akan duk abubuwan daka gindaya mun, tsafi ya dafa hatsabibancin ka ya cigaba da wanzuwar har Æ™arshen zamani ” Fulani Maryama ta faÉ—a tana karÉ“ar layun da ya bata.

 

Cikin jindaÉ—in kirarinta ya ce, ” TaÉ“ewa ta tabbata ga mai yin shirka kije tukwicin aikinmu na ga cikin bayin Masarautar ku kamar yanda muka saba duk lokacin da kuka ziyarce mu, zan Æ™ara miki tuni idan kun wayi gari da mutuwar wani bawan babu ku babu cin kayan sadakar inba haka ba zaku bishi, ku fice daga kogon dutse kuna masu ambatan sunan mu ” yana gama faÉ—a ya É“ace daga gurin, Jakadiya da Fulani tashi suka yi suka fita, suna zuwa bakin kogon dutsen Fulani ta kuma runtse idonta tana karanta É—alasiman tsafin, atake haske ya kuma mamaye su suka É“ace daga gurin.

 

Lokacin da suka koma cikin Masarautar tuni dare ya tsala babu motsin komai sai kukan tsuntsaye da Æ™ananan dabobbi, Fulani karÉ“ar Salman tayi dake hannun Jakadiya sannan ta ce mata, ” Ƙuda wajen kwaÉ—ayi akan mutum ina fatan baki manta maganar boka ba ” rissunawa Jakadiya tayi ta ce, ” Ina ankare ya shugaba ta ”

 

 

_UMMOU ASLAM BINT ADAM_

3 thoughts on “Anya Baiwa Ce Hausa Novel”

Leave a Comment

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Scroll to Top