Hausa Novels

Bakar Wasika Hausa Novel Complete

Bakar Wasika Hausa Novel Complete

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

Bakar Wasika Hausa Novel Complete

Page -1⃣

 

Matashiyar yarinya ce yar shekara goma sha-bakwai dauke da farantin giɗa tana tsaye jikin window makaranta tana leken daliban da ake yi wa darasi.

Yadda ta maida hankali tana sauraren darasin da ake wa dabiban sai ka rantse da Allah har da ita a cikin daliban. Ilmin zamani na daya daga cikin abubuwan da suke matukar burge Aminatu kuma shi ne kadai abun da ta rasa a yanzu, wanda ta riga ta maye gurbinsa da talla a halin yanzu, a izuwa yanzu ta tabbatar bata da muhalli a ilmin zamani, sai dai shi ilmin yana da muhallin a zuciyarta.

Bakar wasika

“Ba ni gidar goma”

 

Wata dalibar ta fada da kamar rada gudun kar malamin da yake musu darasin ya ji ta, a munafunci ta jefowa Aminatu wata tsohuwar naira goma, sannan ta maida hankalinta gurin Malamin.

Aminatu ta duka kasa ta sauke farantin dake hannunta sannan ta dauki naira goma din ta daga hijabinta ta saka naira goma din cikin hular dake kanta ta gyara hijabinta sannan ta dauki giɗar ta mika mata, yarinyar ta karba da sauri ta boye.

A lokacin ne malamin ya hango Aminatu tana kallon allon da yake koya musu darasin, kusan wannan shi ne karo na barkatai da yake arba da yara na shigowa makarantar talla, wani lokacin har cikin ajijuwa suke zagayawa idan sun ga babu malamai a ciki.

Sai dai tsayawa a nasu ana daukar darasin karatu babu kamar Aminatu domin ko daliban makaranta basa nuna mata natsuwa da maida hankali sai dai su nuna mata iya rubutu da kuma fahimtar darasin yadda ya kamata domin su a kullum suna aji ne, ita kuma sai idan talla ta biyo da ita.

 

“Mtcheesss idan ba makarantun kauye ba ina ake wannan abun? Ace makaranta a bude har masu talla suna shigowa, ko wane aji babu ganbu (Kaure) balle har ma ace an zagaye mana makarantar”

 

Malamin ya fada cike da jin zafin yadda aka wofintar da abun da ya shafi ilmin boko a yanki.

Aminatu na jin haka sai ta duke kasa gabanta na faduwa, daman can yarinya ce mai gujewa fitina da tsoron bacin ran mutane. Dukuduku tai ta fice daga gurin cikin sanda ta koma can bakin kofar makarantar inda suke zama ita da sauran masu talla suna jiran a tashi yan makaranta fito siye siye.

Rayuwar Aminatu rayuwa ce da ta ginu da ilimin addinin da kuma talla, domin bayan noma da mahaifinta yake yi wanda shi ne mafi akasarin mutanen garin galadi suke yi, babu wani abu da aka doraga da shi a gidansu kamar tallar da take, da rana zata kai giɗa makarantar boko, dare kuma ayi mata tuwo, da safe kuma ta fita tallar koko, hakan yasa rabin rayuwarta ta kare a talla. Sai dai ko kadan bata da matsalar rayuwa ta ko’ina domin ita kadai ce mace da mahaifiyarta ta haifa bayan zaratan maza bakwai. Rayuwarta kusan haka rabin rayuwar yan matan garin take ba kowa ya ke damuwa da karatun boko kamar yadda suke damuwa da talla ba, domin talla tana ba su komai cikin har da kayan dakin da ake yi ma yan mata.

Garin Galadi wani yanki ne dake cikin karamar hukumar mulki ta shimkafi, gari ne mai cike da albarka manoma, kusan idan ka ambashi shimkafi kowa ya san gari ne na manoma garin mai cike da albarka da kuma mutanen kwarai. Karamar hukumar Shinkafi tana cikin jihar Zamfara, shiyyar arewa maso yammacin Najeriya. Hedikwatar karamar hukumar tana cikin garin Shinkafi kuma karamar hukumar na da iyaka da karamar hukumar Zurmi Maradun da wasu sassan jihar Sokoto da jamhuriyar Nijar.

 

Garuruwa da kauyukan da suka kunshi karamar hukumar Shinkafi sun hada da Miyasa, Shinkafi, Bwane, Tunga, Fidani, Tubali, da Faru. An kiyasta yawan al’ummar karamar hukumar Shinkafi ya kai 177,811 mazauna yankin da ‘yan kabilar Hausa da Fulani suka mamaye. Yaren Hausa dai ana magana ne da shi a karamar hukumar, addini Musulunci shi ne addininsu.

Karamar hukumar Shinkafi tana da fadin kasa kilomita murabba’i 674 kuma tana da matsakaicin zafin na digiri 34. Karamar hukumar tana da kogin Tafin Kaiwa da ke ratsa cikin yankinta yayin da matsakaicin saurin iska a yankin ya kai kilomita 11/h. Noma wani babban aiki ne na tattalin arziki da al’ummar karamar hukumar Shinkafi ke aiwatarwa.

Sauran muhimman ayyukan tattalin arziki da al’ummar karamar hukumar Shinkafi suka gudanar sun hada da farauta, kasuwanci, kiwon dabbobi, da ayyukan fata.

 

 

*** *** ***

 

Tana zaune a gurin har aka tashi yan makarantar masu siyen gid’ar suka siya, wanda tai saura sai ta dauki farantin ta dora akai ta nufi gida tare da kawar tafiyarta Rumaisa, suna tafe tana kirga kudin gidarta har suka kawo mararabar hanya (Hanyar da ta kasu hudu) a nan sukai sallama kowa ce ta nufi gidansu. Da sallama ta shiga gidan kamar yadda ta saba.

 

“Wa’alaikissalam yar Inna yar Albarka”

 

Inna ta fada tana juyowa ta kalleta fuskarta dauke da murmushi. Sanusi ya wara ido ya zubar da ruwan daya wanke tufafinsa.

 

“Mu da ba yan Inna ba a nuna mana bolar mu”

 

Aminatu ta kyalkyale da dariya kamar ba ita ba, tai saurin aje farantin dake kanta ta mikawa Inna kudin hannunta sannan ta karbi dawon (Fura) da Inna take da inna take kirbi (Daka) ta cigaba da yi tana fada mata ko nawa aka samu yau.

 

“Aminatu Auta, himma dai yar Audu”

 

Sanusi ya sake fada da fuskar zolaya, daman can indai yana gida ya fi kowa zolayarta kamar wata abokiyar wasarshi.

 

“Na ji dai ai ina aiki dai ni ba kamar sauran auta ba ne, kai da baka iya noma fa sai sana’ar tireda”

 

Ta masa gwalo. Sai Inna ta saka dariya.

 

“Fada masa dai yar auta gogar aiki, shi baya iya aikin karfi irin na maza sai sana’ar zama”

 

Aminatu ta wani yi warrr da ido tana jin kirarin da Inna tai mata har cikin ranta, ganin hakan yasa Sanusi sake tsokanarta.

 

“Eyee su igeee anji dadi, Igengen…”

 

Take ta turo baki gaba.

 

“Inna kin ga yana ce min Ige ko?”

 

“To maza nawa aka haifa kamin a haife ki? Kin zama Ige ai”

 

Aminatu ta kalli Inna da kwababbiyar fuskarta kamar zata fashe da kuka.

 

“Inna kina jinsa ko?”

 

“Dan Allah Sanusi ka gama ka fita ka bar mana gidanmu, ya zaka takurawa Auta”

 

Inna ta fada. Sai Aminatu ta gyada kai

 

“Atooo”

 

Dariya yai ya debi ruwa a babbar buta ya zagaya bandakin da ya kasance na kasa kuma iya tsawon habar mutum, (shoulder) domin idan ka mike tsaye gaba daya, za a iya hangoka.

Kamin ya gama wanka Aminatu ta gama kirba dawon har ta kwashe ta zuba wani, Auta ce amman ba kamar sauran ba, domin bata da ƙwiyar aiki, ita dai bar ta da shagwaba da yawan kuka idan an taba ba.

 

“Baka ma wanku ba tsami kake yi”

 

Ta fada tana yatsina fuska kamar gaske. Dariya yai ya shiga karamin dakin dake kusa da na Inna ya shirya cikin wata karamar shadda ta marasa karfi da ta gama shan jiki ya saka hullarsa taɓani ka ji Hadisi, sannan ya fito yana ta kwanbo da talkaminsa na roba.

 

“Wallahi ba kai kyau ba”

 

Cewar Aminatu tana dariya, sai Inna ta taya ta.

 

“Lallai kam kyau ai sai Auta hanci har baka (Baki) sai dai a gwada mata haske shi ma kadan”

 

“Inna Wallahi ki daina biyewa wannan yarinyar, idan ma ta samu miji irina ta more…”

 

Har Aminatu ta bude baki tai magana sai kuma tai shiru ta maida dubanta gurin yayanta Amadu, wanda take tsoro kamar mutuwarta domin idan yana a cikin gidan bata da sukuni ko wani motsin kirki bata yi. Na tsantsiyar yarinya ce, sai dai shigowar Amadu ya saka ta kara natsuwa ta yi tsit a gurin kamar babu ita. Amadu irin mazan nan ne da basa wasa da yara balle kuma ita da take kanwarsa ta biyar.

Wani tsohon babur dinsa Honda ya turo ya karaso inda suke, Inna na nashe dawon a tukunya, Aminatu kuma na zaune gaban turmin idonta kasa.

 

Inna ta daga kai ta kalleshi yana kokarin jingine babur din ta ce.

 

“Ka dawo?”

 

“Eh ya gidan?”

 

“Lafiya Kalau, ya kasuwa”

 

Ya dan yi jimm cike da damuwa sannan ya sauke ajiyar zuciya.

 

“Kasuwa da godiya Inna, amman abubuwan kasar nan sai hamdala, komai kara masa kudi ake, idan baka da wani babban jari yanzu sai kasuwancin ma ya gagareka”

 

“To ya za’ayi kasar ce ta zama abun da ta zama, Allah ya ba mu azzaluman shugaban ni, ba su da tausayi kansu kawai suka sani”

 

Cewar Sanisu yana nufo inda suke, Sai Amadu ya amsa masa.

 

“Wallahi ga rayuwar mutane an maida ta kamar ta dabba, kai har kara ma dabba a yanzu, kuma sun kasa daukar mataki basa ma son ana ji, Nigeria kam ban san yaushe zata gyaru ba”

 

“Allah ya kyauta, ni dai na wuce shago”

 

Sanusi ya sake fada, sai Inna ta bishi da addu’a.

 

“To Allah ya tsare ya bada sa’a”

 

Har ya fice Aminatu bata dago kanta ba, ko da wasa bata son ta hada ido da Amadu, ba ganinsa kadai ba ko muryarsa ta ji sai ta ji gabanta ya fadi.

 

“Inna Ina Lami kike neshen dawo da kanki? (Saka fura a tukunya)”

 

Amadu ya tambaya.

 

“Kai ma ai kasan bata nan, da tana nan ai ba zata bar ni nai wannan aikin ba, ta je ganin dan Kuidu (Kaciya)”

 

Ya shaf kansa.

 

“Na manta ta fada min, abubuwan ne sun yi yawa Wallahi”

 

Ya fada yana nufar bangaren da Iyalinsa suke. Domin irin katon gidan nan ne na kauye mai fili wanda yaya suke dibar bangare suna kafa na su iyalin, bayan shi da yake da mata daya, Musa mai mata biyu ma a gidan yake zaune, sai dai shi ya fitar da kofar gidansa ta can baya sai an zagaya za a iya shiga, Iro da Sanusi ma da ke shirin aure a cikin gidan suka gina gurin da za su aje matansu.

 

 

 

TALBA POV.

 

Yana zaune a dining din har Momy da Baaba suka gama hada abun karyawa. A hankali ya dago yana kallon yadda Baaba take jera kulolin, hannunsa suke da wayarsa. A hankali ya lumshe idonsa ya bude, cike da kasaita ya motsa bakinsa, yana maida dubansa gurin Momy wanda taja kujera ta zauna.

 

“Baaba a fadawa yaran nan su fito su karya”

 

Matar da aka kira da Baaba ta dan risinawa Momy cike da ladabi.

 

“To ranki ya dade”

 

Ya nufi upstairs da sauri, da ido Talba ta bita kamin ya maida dubansa gurin KB da ya fito a daya daga cikin kokafin da suke can dayan bangaren falon.

 

“Momy ina kwana”

 

KB ya fada yana kokarin jan dayar kujera ya zauna, sai Momy ta amsa masa ba yabo ba fallasa, sannan ya mikawa Talba hannu suka gaisa, ya shiga hadawa kansa tea. A tare Amal da Leila suka sauko downstairs din, kai tsaye suka nufu dinning area, Amal da far’arta kamar kullum, Leila kam sai wani sham kamshi take musamman da ta hango Talba a zaune a dinning din.

Amal ce ta riga isa ta zauna tana fadin.

 

“Ya Talba Morning”

 

Ya kai dubansa gareta yana sakar mata murmushi as respond, irin murmushin nan da be saba zama a fuskarsa ba. Bayan ta gaishe shi ta gaishe da KB.

 

“Ya KB Morning”

 

“Morning Amal”

 

Ya amsa yana kai plantain a bakinsa. Leila na zaunawa Talba ya mike tsaye cike da izza, sai duk suka kalleshi.

 

“Ah ah ba karyawa za kai ba?”

 

Momy ta tambaya.

 

“Zan yi breakfast a waje”

 

Ya amsa kamar an amsa dole, already yayi nisa da dinning din. Sai da ya fice daga falon gaba daya sannan Momy ta kalli Leila.

 

“Kun sake yin fada ne?”

 

Leila ta kalleta cike da damuwa.

 

“Momy miyasa kullum ni ce mai laifi?”

 

Momy ta zare mata ido.

 

“Yes tun da ya dawo sallah asuba yake zaune a nan, idan har babu komai to babu abun da zai saka ya zauna tun 6:30 har 9:30 dan kawai kin zauna kuma ya tashi ya ce ya zai karya a waje, zan kaiwa Daddynku abinci yanzu, ki same ni daki anjima”

 

Momy na fadar hakan ta mike tsaye ta dauki wasu tsadaddun kuloli ta nufi kofar da zata sadata da bangaren Daddy.

 

“Ni ma ba zan karya ba”

 

Amal ta fada tana turo baki alamar ranta ya bace sai harara take watsawa Leila kamar ba yayarta ba, sannan ta mike tsaye ta fice daga gurin ta nufi upstairs.

 

“Munafuka, ai daman tun da Yayanki be ci ba ba zaki ci ba Mtschesss”

 

Cewar Leila tana binta da harara. KB ya bi Amal da kallo har ta shiga dakinta sannan ya kalli Leila.

 

“Da gaske fada kuka yi kenan?”

 

“Ai dole mu sake fada kuma mu yi ta fada, na gaji da halin Talba, na gaji, shi ba dan sarauta ba, ko yan sarauta ba su abun da yake, ba baiwarsa ba ce ni, and i hate nonsense”

 

Mikewa tai tsaye a fusace har tana jefa da empty cup din dake gabanta, a take ya fadi kasa ya fashe, kamar zata tashi sama haka ta nufi upstairs. KB ya wara ido.

 

“To ni ina ruwana, can ta matse muku, a takaice dai ni kadai zan karya a yau… Fine”

 

Ya sake bude wata kular ya shiga zubawa kansa ferfesu.

 

 

 

FARUQ POV.

 

 

Ya aje kofin garin dake hannunsa yana kallon dansa.

 

“Ka koshi ko?”

 

Sultan ya daga masa kai yana murmushi kamar yadda shi ma yake masa murmushin. Faruq ya dauke shi ya dora saman kafafuwanta sannan ya kalli Mahaifiyarsa cike da damuwa.

 

“Mama bari mu tafi kar dare yai mana”

 

“Kara ka tafi da wuri kam tun da a kafa zaka je”

 

Ya mike tsaye.

 

“To sai da safe ayi ta mana addu’a dai”

 

“Addu’a ai dole ce Faruq, Allah ya tsare, Sultan sai da safe ko?”

 

“Sai da safe Mama”

 

Sultan din ya fada da muryarsa da be gama kwarewa da iya magana ba. Daukarsa Faruq yai ya fice daga gidan, a kafa ya taka tun daga unguwar dallatu har Gadar Baga, ganin Sultan ya fara bachi sai ya dora shi a kafada Faruq, yana tafe gabansa na faduwa har ya iso gidansa. Sai da ya saka hannunsa aljihu ya lalaba garin kwakin dake cikin aljihun wandonsa da sugar ya tabbatar suna nan sannan ya kwankwasa kofar gidan. Yayi kusan rabin awa a tsaye sannan Rafi’a ta bude masa. Ganin babu komai a hamnunsa yasa ta ja tsaki.

 

“Mtcheesss”

 

Be ce mata komai ba ya saka kafarsa ya shigo cikin madaidacin gidan na zaman mutum daya, sannan ya maida kofar gidan ya rufe. Da sallama ya shiga cikin falon amman ta ki amsa masa sai latsar wayarta take kamar bata san da shigowarsa ba. Be damu ba domin in da sabo ya saba da halin matarsa. Dakinsu ya shiga ya kwantar da Sultan sannan ya dawo falo ya zauna kusa da ita, kana ya ciro garin da ba zai wuce gwangwani daya da rabi ba da surga ya mika mata.

 

“Ga dan abun da muka samu”

 

Daga shi har garin kallon uku saura kwata ta watsa masa.

 

“Gari fa nake gani Faruq?”

 

“Shi ne”

 

Ya amsa mata kamar wani yaronta.

 

“So kake jinina ya tsotse ne? Kara min jinin ma ya gagara? Haba Faruq, na wuni ban ci komai ba kuma yanzu ka shigo min da gari?”

 

Ta masa maganar kamar zata fashe da kuka, ya sauke ajiyar zuciya a hankali.

 

“Haba Rafi’a tun da kika ga na shigo miki da gari ai kin san ban samu komai ba ne, shagon na mu sabuwar unguwa ce ba a samun ciniki sosai, tun da na fita har babu wanda ya zo aski, wannan garin ma sai da na biya ta gida Mama ta siyo min aka jikawa Sultan ya sha sauran ne na kawo miki, Wallahi ni tun karin safe da na yi ban sake cin komai ba, kara ke na bar miki gwangwani biyu na wake…”

 

Be marasa ta mike tsaye tana masa ihu.

 

“Kai ka so Faruq kai kaso zama da talauci, sa’aninka suna can sun gina manyan gidaje wasu na da manyan motoci, su ci mai kyau su saka mai kyau, amman kai dube ka? Suturar kwarai ma ta gagareka, ni kaina da nake matarka ina kunyar a tararda ni a gidan nan, gida duk ya lalace, da an yi magana kace komai zai wuce sai yaushe zai wuce? Shekara biyar fa da aurenmu Faruq, ka dube ni ka gani tsabar kyau Baturiya ake ce min fa! Amman na kare a aurenka, auren kaddara auren cin garin kwaki, dan sunan mai dadi ma baka iya kirana da shi ba, Rafi’a Rafi’a, Fee’ah Fee’ah haka ake kirana ba Rafi’a ba”

 

Ta nufi dakinta a fusace, shi kuma ya lumshe idonsa yana jin zafin maganar da ta fada masa. Yana zaune a falon har 11pm na dare sannan ya tashi ya rufe kofar falon ya kashe wutar ya shiga dakin ya shiga bathroom yai fitsari ya wanke kafafunwasa da fuskarsa sannan ya dawo dakin ya kwanta bayanta, can kuma ya tashi zaune yai ma dansa addu’a sannan ya kashe wutar dakin, ya dawo bakin gadon inda ya saba kwanciya yai tasa addu’ar, ya ciro wayarsa ya aje a gefensa ya kwanta, a hankali ya kai hannunsa ya fara shafata sai ta buge masa hannun ta tashi zaune.

 

“Miye haka? Ka dawo min da garin dan jinina ya tsotse, kuma yanzu ka zo min na maka me? Da safe kuma dan ka ya dame ni da kayan fitsari tun da an gagara sai masa pampas, ga wannan tsinannen cikin wahala da yake jini, haba duk ni kadai? Wai kai baka da imani ne?”

 

“Rafi’a wai miyasa bakinki ba shi da linzami ne?”

 

Ya fada a fusace yana kokarin danne fushinsa.

 

“Shi bakin nawa ai haila yake, kai kudi ka gani idan zan maka duk wannan, su masu kudi ka ga matansu na musu haka ne? Saboda sun ba su komai gurin kwanciya ma dakin yara daban ake amman kai ka hade ni daki daya da yaronka, anjima kace min na taso muje falo ko? To ba zan je ba”

 

Sauka yai daga saman gadon gaba daya ya fice daga dakin, be tsaya a falo ba tsakar gidan ya fita gaba daya ya zauna saman turmi ya daga kansa sama.

 

“Kun faya kun sai kai Allah”

 

Ya fada yana kallon yadda taurari suka kawata samaniya.

Rafi’a na jin ya fitarsa tai azamar dauko wayarta touching, ta dauki keypad dinsa ta shiga contact list tana neman wata number.

MD Saleh a dai dai gurin ta tsaya ta bude sunan ta kwashe numbers din sannan ta maida wayar ta aje, sai tai saving number da Maryam Dahiru Sokoto, kana ta saka wayarta a silent ta kwanta.

 

 

 

 

 

 

________

 

Na zo muku da albishir guess what? A have alot of kayan mata masu kyau gaske, akwai na infection, akwai maida tsohuwa yarinya, akwai set din da ake hadawa for matan da basa gane kan mazajensu, akwai na mallaka kala kala, muna kaza mai magani, tantabaru, akwai kaza mai Yasin, akwai na mallaka sirrine mai karfin gaske. Ina masu son zama madubi a gurin mazanje su? Ina matan dake cewa na gwada ban dace ba? Muna da gumba da garin magani kala kala da na tsarki ga Humra da turarunka kala kala amman fa na kayan mata.

Ga masu bukata za su iya tuntubar number na 08036126660 zan saka miki a mota na aika miki har inda kike da yarda Allah.

 

Serious Buyers please, idan ba ki shirya ba kar mu batawa juna lokaci.

 

*💔 BAKAR WASIKA 💔*

 

 

By Khadeeja Candy

 

 

Page -2️⃣

 

“Akwai abubuwa da yawa da rayuwa bata iya tafiya sai da su, a ciki akwai numfashi ci da sha, da kuma soyayya. Bana jin zan iya rayuwa idan babu kai a kusa ni, zan iya rasa ci da sha kuma na rayu da soyayyarka”

 

Ta nade wasikar da ta gama rubutawa da hausar azami, tana murmushi sannan ta mike tsaye ta maida biron da littafin cikin jakarta ta islamiya ta rataya a jikin kusar dake gurin sannan ta saka hijabinta ta fito.

 

“Inna an gama?”

 

“Auta tun dazun na gama, kin yi sallah dai ko?”

 

Ta saka wasikar a cikin jikinta tana murmushi.

 

“Inna ke ma kin san bana wasa da sallah fa”

 

“Haka ne, Auta Allah ya miki albarka”

 

Inna ta fada Baba da ke zaune saman tarbarma yana sauraren redio ya amsa da Ameen yana murmushi. Sanusi ma dake aikin auna tuwon dawo a bakinsa ya so ma zolayarta kamar yadda ya saba.

 

“Ku na fasa mata kai da wannan kafafuwan nata kamar itace”

 

Aiko kamar jira take sai ta fara kukan shagwaba, musamman ganin duka gatanta suna nan Inna da Baba.

 

“Baba kana jinsa ko?”

 

Baba yayi dariya tare da kai hannunsa ya kashe redio dake gefensa, ya tofar da goron bakinsa. Yai mata alama da ta zo da hannu, kamar jira take sai ta karaso inda yake tana ta turo baki ita ala dole an taba ta.

 

“Auta Mamana, ki daina biyewa Sanusi, shi da yake ragon maza, ke da kike Jaruma, ki daina nuna musu rauninki, kin ga shi kin ga Rilwanu ki daina bari suna saka ki kuka, da an miki aure sai kun yi ta marmarinki”

 

Ta rufe ido da sauri cike da tsantsan kunyar irin ta ya mace bahaushiya. Hakan da tai sai ya kara saka Baba murmushi.

 

“Allah ya miki albarka ya nuna mana lokacin Autata”

 

Kasa amsawa tai da ameen domin Aminatu irin yan matan nan ne masu kunya da kawarda ido ga wasu abubuwan. Sai kawai ta mike tsaye har lokacin bata janye hannunta daga fuskarta.

 

“Wai kunya take, kunya kike kika yarda kina fita zance”

 

Sanusi ya fada yana dariya, a cikin hasken farin watan Aminatu ta watsa masa harara. Ta nufi inda kwallar tuwonta take ta nada ganwo ta dauka ta dora a kai sannan ta mika dayan hannunta ta dauki miyar dake cikin bokitin roba.

 

“Ni na tafi gurin sana’a ta”

 

Ta fada tana kara murda masa baki, Inna dai bata ce komai ba bayan murmushin da tai. Har ta kai bakin kofar fita daga gidan sai Baba ya kirata.

 

“Mamana”

 

Ta juyo.

 

“Na’am Babana”

 

“Allah ya miki albarka”

 

Sai ta amsa tana kallon gefen Sanusi.

 

“Ameen, yan bakinciki sai dai su mutu”

 

Ba Inna da Baba da Sanusi kadai ba, har Rilwanu da Iro da suka shigo yanzu sai da suka saka dariya, domin sun san tatsuniyar gizo bata wuce ta koki, inda Aminatu ta yi habaici ko shagube to ba zai wuce Sanisu ko Rilwanu ba take yi ma.

 

“Mai tuwo a bani na hansin”

 

Ko kallon Rilwanu ba tai ba ta saka kai ta fice tana cinno baki gaba kamar zai zazzago ya zubo kasa. Kusa da Baba suka zauna ko wane ya aje bindigar maharba da manyan wukaken dake hannunsu. Kana ganinsu ka ga zaratan jarumai, tun daga kirarsu har yanayin shigarsu da muryarsu. Domin suna daya daga cikin manyan yan saka na yanki, abu ne mai wahala ka ga gidan da ke da maza uku ko hudu baka samu yan sakai a gidan ba balle kuma gidansu Aminatu da suke da maza bakwai. Ba wuka ba ko bindiga bata huda mahaifinsu balle kuma su da suke shiga dajijikan kauyen neman barayi da kansu.

 

Tana yin nesa da gida kadan sai murmushi ya wanke mata fuska, a cikin abubuwan da tafi kaunar a rayuwarta akwai yan’uwanta, musamman Rilwanu Sanusi da Musa, domin sun fi sauran sake mata, da kuma kyautata. Gashi basa yarda ko da wasa wani ya nuna mata yatsa a waje balle har a taba ta.

A natse take tafiya, tana ta mikawa mutanen data sani kuma suka santa gaisuwa cikin girmamawa, musamman abokan mahaifinta, sai da ta kusa dandali sannan ta rage saurin tafiyarta da alama akwai wanda take jira ko take son hangowa, can kuma ta ja ta tsaya ta juyo tana kallon hanyar data fito sai ta hango masoyinta tafe da saurinsa cikin shigar kananan kaya, murmushi ne ya cika fuskarta, sai ta sauke idonta kasa domin bata jin kunyarta zata barta tai ta kallonsa har ya karaso inda take.

Sai da yai wani gyaran murya ya waiga ya ga babu mai ganinsu sannan ya ce.

 

“Auta”

 

“Na’am barka da dare”

 

“Yau ina fitilarta?”

 

Sai da yai maganar ta tuna da zancen wata fitila, sam ta manta bata zo da ita ba, sai a yanzu ta suna ta bar fitilar a dakin Inna bayan ta gama rubuta wasikar.

 

“Wallahi na manta ta”

 

Ta fada tana dukawa ta aje bokitin miyar dake hannunta, sannan ta saka hannu a cikin zanenta ta dauko wasikar ta mika masa, ya karba da dayan hannunsa dayan hannun kuma ya mika mata tasa wasikar.

 

“Na je gida na karbo miki?”

 

Ta zaro ido.

 

“Kai Baba yana nan fa, ni ban saba aikin maza a gidanmu ba”

 

Yayi yar dariya yana kokarin magana suka ji muryar Sanusi.

 

“Auta…”

 

Ba karamin tsoro Aminatu ta ji ba, domin bata saba tsayuwa da maza har a ganta ba, duk kuwa da kasancewar ta kai munzalin da zata iya yin hakan, amman kunya da tsoron yayyunta ya hana ta yin haka, duk inda ta san idan ta tsaya da wani za a gani ayi mata magana ko fada bata yarda ta tsaya a gurin. Maniru ne ya soma wayancewa ya mikawa Sanusi hannu suka gaisa, Sanusi ya amsa yana musu dariya.

 

“Ka ce na zama yaya daga yanzu”

 

Maniru yayi dariya Aminatu kuma ta duka da sauri ta dauki bokitin miyarta daman tuwon yana saman kanta.

 

“Ga fitilar in ji Inna”

 

Ya mika mata yar karamar touch light din dake hannunsa, sai ta karba da sauri ta juya ta cigaba da tafiya cike da tsananin kunya gabanta sai faduwa yake. Sai da tai nisa sannan Sanusi ya kalli Maniru ya ce.

 

“Maniru idan kana son Aminatu ai gidansu ya kamata ka ta fi ba wai ka rika tare ta a hanya ba, amman irin wannan ai ba lallai ne kowa yai maka fahimta mai kyau ba”

 

“Wallahi Sanusi ina son zuwa, ita take hana ni, sai tace tana jin kunya kuma yayyunta za su iya mata fada”

 

Sanusi yayi dariya.

 

“Shirmen ta ne, ba a aure mu za mu yi, idan ka shirya kawai ka min magana zan sanar da Baba sai a komai cikin mutunci”

 

“Maa Shaa Allah, na gode sosai daman ni abun da nake nema kenan domin na gaji da zageye zageyen nan Wallahi”

 

“Inshallahu zan yi magana da Baba, duk yadda ake ciki zaka ji”

 

Sai da Maniru ya sake mika masa hannu suka gaisa sannan ya wuce yana ta jindadi abun nema ya samu.

Aminatu na daya daga cikin irin yan matan nan da suke da farin jinin siyarda sana’a musamman a dandali duk kuwa da kasancewar ba wani kula samari take ba, amman abu ne mai wahala ta je da tuwo ta dawo da shi sai ta saida kaf wani lokacin ma har ta karbi na wasu ta siyar musu, saboda tsabtarta da kuma dadin miyar Inna. Har ta gama sai da tuwon ta nade komai nata a guri daya Wasikar da Maniru ya bata tana cikin jikinta, a dayan bangaren kuma tana ta tunanin yadda zata shiga gida, domin ta san abu ne mai wahala ace Yayanta Sanusi be fada cewar ya ganta da Maniru ba, ba fada kadai ba wata kila har doka sai ta sha a gurin Yayanta Amadu. Da gangan ta ki yarda ta je gida da wuri duk kuwa da kasancewar ta siyar da tuwonta a cikin lokaci, sai ta zauna a gurin tana ta kallon mutane fuska ba yabo ba fallasa, ba zaka iya karantar damuwarta ba, sai dai hakan kuma be isa ka fadi cewar tana cikin farinciki ba.

Har kusan 11 na dare bata tafi gida ba tana zaune a gurin sai ta fakaici idon mutane sai ta matse yan kwalla da suke cika mata ido, sai kuma ta dan turo baki, sai kallon mutanen dandalin take sai ka rasa wa take turowa bakin. Ganin babu sarki sai Allah yasa ta mike tsaye ta dauki robar ta dora a kai tai ma abokan sana’arta sallama, ta fara tafiya kamar bata son zuwa, ta san inda bata je ba sai an aiko nemanta kamar yadda ake idan ta dade bata dawo ba, dan haka bata da wata mafita data wuce ta koma gida.

 

 

 

 

 

TALBA POV.

 

Yana shakimce cikin mota har Ali ya iso gurin motar ya bude front seat ya shiga ya zauna yana kallon abokin nasa

 

“Lafiya dai?”

 

Talba yaja wani dogon numfashi ya sauke sai huci yake, har ya bude baki zai yi magana sai kuma ya shiru ya maida dubansa wani gurin. Ali na ganin hakan yai dan murmushi.

 

“Leila ta tabo ka kenan?”

 

Talba ya kalleshi da idanuwan dake nuna bacin ransa karara kamar yadda fuskarsa ma ta kasa boye bacin ransa.

 

“Wai yarinyar nan ni zata wulakanta?”

 

Magana yake kamar wuta na fita a bakinsa. Ali ya masa kallon natsuwa.

 

“In I’m not mistaken ka sake mata maganar auren kenan?”

 

Shirun da Talba yai ne ya tabbatarwa da Ali eh ce amsar tambayar.

 

“Amman ta wace siga kai mata maganar?”

 

Talba ya watsa masa wani banzan kallo.

 

“Kamar wani karamin yaro zaka tambaye ni wace Siga nai mata maganar?”

 

“No baka gane ba ne Talba, su fa mata yan lalabawa ne, kai kuma sai kace komai da karfi da isa zaka yi ba haka ake ba”

 

Talba ya watsa masa wani kallo.

 

“Okay kamar ba baka san ni ba kenan? So kake na je na same ta ina lallashinta ta aure ni?”

 

“No kai baka gane ba, Talba wannan lokacin ya wuce da zaka dinga tirsasa mace ta yi maka abu any how, na san Leila tana sonka amman kai din ne wani iri”

 

“Kai Ali duk fa mace da zan aura alfarma zan mata, ba dai ita ta min ba, ina da kudi ina da kyau ina da ilmi ina da addinin da har a kasar waje za a iya bani aure balle a nigeria a nigeria ma a gidanmu”

 

“Ka ga matsalar ka ba, wani irin alfarma tun da har kuna son junanku? Kar fa ka manta Talba Leila a waje tai karatu kuma wayayyiyar mace ce mai son burgewa, Talba dan kalaman nan na soyayya baka san kai mata ba, dan morning text din baka tura mata, balle har ka kirata ku yi fira, ko ka dauke ta ku fita, mata suna son wannan”

 

“Ba zan yi ba, ina namiji zan wani zan wani rika lallaba mace, idan ma zan mata sai an yi aure, amman ba a yanzu ba ai sai ta raina ni, besides muna gida daya zan rika mata haka?”

 

“To miye a ciki, ai an san aurenta zaka yi tun da an muku baiko, kai komai sai kace na zafi zaka yi, idan ka sake mata ba shi yake nufin ka bata umarni ta ki bi ba, dan Allah ka kirata yanzu ka bata hakuri”

 

Kamar wanda aka cewa cire ranka ka bata haka Talba yai ma Ali wani irin kallo na mamaki da tsoro a lokaci daya.

 

“Ni Mu’azzam Auwal Shimkafi zan kira mace na ce dan Allah ki yi hakuri? Macen da ba uwata ba? Malam dan Allah fitar min a mota”

 

“Talba mata fa sai da haka, kuma ka canja hali dan Allah”

 

“Ita ma ai bata iya kalaman soyayya ba, bata san ta kira ni ta gaishe ni ba ko ta turon sakon soyayya, kai ni bana jin ma akwai ranar da Leila ta taba kallona tace kana da kyau simple word bata taba fada min ba, sai ni zan fada mata? Ba yi wannan macen da zan zauna ina bude mata sirrin zuciyata ba har ina rarrashinta”

 

“Wannan ji da kan babu inda zai kaika Talba, idan ka sake mata ka nuna mata kauna dole ita ma zata sauko fa”

 

“Malam na ce ka fitar min a mota…!”

 

Yanayin yadda yai maganar ya isa ya sanar masa ba da wasa yake ba, kuma ya san halin abokinsa idan ransa ya bace baya jin rarrashin sai dai hakan ba zai hana anjima ya kira shi yace yana son wani abu ba ko kuma su gadu a guri kaza. Salun alum ya bude motar ya fita yana murmushi da mamakin irin halin Talba.

 

“Ina fada maka matsalata kana wani kokarin ba ni laifi, an fada maka mata haka ake musu ne!”

 

Magana yake da kansa yana tukin cikin bacin rai, domin be san inda zai je ba a yanzu kasancewar yau weekend kuma gashi safiya ce be ma karya ba.

 

 

 

@12:44pm

 

Leila na zaune tool din mirror Momy tana zana mata abun da ya faru.

 

“Kawai sakonsa na gani a wayata wai na fito waje yana son magana da ni, Momy babu ko irin shaukin nan Wai Ke fito waje ina son magana da ke, haka dai na daure na fita, na same shi a balcony ya kusan 30 be ce min komai ba, sannan wai ki yi fixing date na auren mu, Imaging babu ko dan shauki sai wani ji da kai”

 

“Ke kuma kika ce masa me?”

 

Momy ta tambaya tana harararta.

 

“Na ce nasa ba zan yi ba, ni ban tashi aure yanzu ba”

 

“Ki ba shi hakuri”

 

Ta kalli Momy kamar tai magana sai dai ganin babu wasa a fuskar Momy yasa ta mike tsaye ba tare da tace komai ba ta fice daga dakin cike da bacin rai. Dakinta ta shiga ta dauki key din motarta da jakarta da wayarta, ta fito babu mayafi ta sauko kasa kamar zata tashi sama, daman ta saba fita babu mayafi abu ne mai wahala ka ganta da mayafi a jiki komai kankantarsa.

Tana fitowa ta nufi gurin da motarta take ta bude ta shiga tai yi warming dinta sannan ta danna horn da karfi mai gadin na ganin hakan yai saurin bude mata gate. Kamar wata mai gasar tsere haka ta fito daga cikin gidan da mugun gudu ta hau titi tana jin kamar ta fasa ihu. Sai da tai nisa sannan ta dauki wayarta ta kira Adam.

 

“Besty kana ina?”

 

“Ina gida ya akai? Kamar kina cikin damuwa”

 

“Ina ciki besty mun yi fada da Talba?”

 

“Mtssss wai me ke damun Talba ne?”

 

“Ina na sani, ban san abun da yake takama da shi ba, indai kudi ne ni ma ina da su, ilmin ina da shi kyau ba za a min gori ba, amman sai wani nuna isa da ji da kai”

 

“Wallahi kam yan kalaman soyayya ma ace ba zaka iya yi ma mace ba, idan an yi auren ya kenan?”

 

“Shine abun da nake magana a kai, ni kuma sai na nuna masa ina da tsada ni ba kamar sauran mata ba ne, dole na ja masa aji, yadda yake jin ba zai iya min kalaman soyayya ba ko ya dauke ni mu fita ko ba ni hakuri haka ni ma ba zan taba yi masa ba”

 

“Hakan shi ne daidai, kara ya san darajarki a dole ya sauko idan yana sonki”

 

“Shine ai, shi kawai abunda ya dauki mace ya mata umarni ta bi ya juyata yadda yake so, ni kuma sai na nuna masa na fi karfin haka Wallahi”

 

“Yanzu dai kwantar da hankalinki ki samu ruwa ki sha, ki fita waje ki sha iska zan zo na dauke ki mu fita”

 

“Har na ma fito gida amman bari na koma”

 

“Okay but ki yi murmushi pls”

 

Ta yi murmushin mai sauti kamar yadda ya bukata, sannan ta aje wayar, ta juya ta koma inda ta fito. Kamar yadda ta fito haka ta koma gidan da gudunta ba da damuwa da titi ko sauran motoci burinta dai ta aikawatar da abun da take so. Horn biyu tai kamin tai na uku Mai gadin ya bude mata gate ta shiga cikin gidan da mugun gudu ta faka motar a inda ranta ya so ta fito ta nufi kofar falon, door bell ta danna da karfi kamar zata balla shi sannan taja ta tsaya tana tsaki, shiru ba a bude ba har sai da ta sake danna door bell din sau biyu ta hada da knocking. Sannan Baaba ta bude mata.

 

“Wallahi tallahi kika sake barina a tsaye a waje ina knocking, abincin ki ya kare a gidan nan Baaba”

 

“Wanke wanke nake yi Leila shiyasa”

 

“Na dai fada miki”

 

Ta fada cikin tsawa, ba dan Baaba ta yi saurin kaucewa ba da Leila tureta zata yi ta wuce. Baaba ta maida kofar ta rufe sannan ta juyo cikin falon cikin rashin jindadi zata koma Kitchen din sai ta ji muryar Momy dake tsaye stairs.

 

“Baaba a rika kula mun dauke ku aiki ne kawai saboda mu huta, a daina batawa yarana rai”

 

Baaba ta daga kai ta kalli Momy sannan ta daga mata kai cikin da ladabi.

 

“To Hajiya Inshallahu za a kiyaye”

 

Sannan ta sadda kanta kasa ta nufi kitchen din cikin rashin kuzari.

 

 

 

 

FARUQ POV.

 

Kallonta ya tsaya yi da dayan biyu kamin ya amsa gaisuwar da tai masa, domin ba kasafai take gaishe shi da safe ba sai idan tana son wani abun ko kuma ta lura aljihunsa da dan nauyi.

 

“Lafiya Kalau an tashi lafiya?”

 

“Alhamdulillah, sai yunwa da nake ta ji tun jiya”

 

“Toh Allah ya buda mana kofafin samu”

 

“Amin…”

 

Ta amsa tana kallon Sultan dake motsawa alamar zai farka daga bachin da yake.

 

“Na ce wai ba zaka kira abokin nan naka ba, ka roki shi dan wani abu?”

 

Ya girgiza mata alamar aa.

 

“Ba zan dauna kullum ina bin abokai ina rokonsu ba, bakin da Allah ya tsaga ba zai hana shi abun da zai ci ba, kuma ni ma na yi karatun idan mu kai hakuri komai zai wuce”

 

“Matsalar kenan Faruk girman kai, kana da girman kai, yanzu haka zamu zauna mu wuni da yunwa gashi idan ka fita baka dawowa sai dare? Ga ni da ciki ga Sultan?”

 

Yayi shiru yana jin yadda kansa yake sara masa saboda maganganun da Baturiya ta fara masa.

 

“Shiyasa na ce zubar da cikin nan zan yi na huta, kai ma ka huta domin na san ko ragon suna da wahala a samu a yanka masa wannan bakin talaucin da muke fama da shi”

 

Ta fada cikin kukanta na munafurci. Sai ya kalleta a raunane.

 

“Zubar da ciki ba zai kawo mana Mafita ba Rafi’a miyasa ba ki da tunani ne wai?”

 

“To ni dai gaskiya yunwa nake ji, tun jiya fa ban ci komai ba, kuma anjima na nan ga Sultan ma”

 

Wani dogon numfashi yaja ya sauke ya mike tsaye ya fice daga dakin cike da damuwa. Binsa tai da harara.

 

“Ni dai Wallahi na gaji da wannan bakar rayuwa, Allah kadai ya san yadda masu kudi suke ji, su kwanta a mai kyau a ci abun da ake so, ni ko na kare a nan duk kyau na”

 

Ta fada tana mikewa tsaye tare da bin bayansa, sai da ta tabbatar ya fita sannan ta dawo ta dauki wayarta ta shiga contact list dinta ta kamo number da tai saving jiya. Maryam Dahiru Sokoto ta aika mata kira, ringing tai har ta tsinke ba a daga ba ta sake kira nan ma ba a daga ba.

 

“Ka ji yan gayu sai ayi ta kira basa dagawa…”

 

Whatsapp dinta ta bude ta shiga gurin numbers ta kamo number wanda ke dauki da hoton wani matashin da ba zai wuce sa’an mijinta hakimce cikin mota. Sai da ta gama kallon hoton sannan ta shiga aika masa sako.

 

‘Assalamu Alaikum, ranka ya dade fatar an tashi lafiya, ya aiki ya Madam da yara. Ranka ya dade sunana Fee’ah matar Faruq abokinka, na kira baka daga ba shiyasa na yanke shawarar turo maka sako. Wallahi muna ciki matsala, yau kusan kwana nan mu hudu ba mu girka komai ba, shi ma idan ya fita haka yake dawowa saboda shagon da aka bude sabon gurin ne cikin wata sabuwar unguwa ba kowa yake ta aski ba, yanzu haka Sultan kuka yake, ni kaina dauriya kawai nai saboda da na, Dan Allah ka taimake mu kamar yadda Allah ya taimake ka, na duba na ga a cikin abokan Faruk babu mai tausayinsa da son taimaka masa irinka, na so Faruq yai maka magana da kansa amman yace nauyi yake ji, yanzu haka be san na dauki number ka ba, domin idan ya sani ina ciki matsala. Ka huta lafiya Allah kara rufa asiri’

 

A rarrabe ta tura sakon har tana gadawa da emoji din rokon da kuka. Sannan ta duba last seen dinsa tun jiya da dare, tana jin motsin turo kofar gidan tai saurin aje wayar ta kwanta kasa. Faruq ne ya shigo dakin rike da bakar leda har biyu a hannunsa. Ya aje mata dayar a gabanta ganin hakan yasa ta tashi zaune tana kallon 200 dari biyun da ya mika mata.

 

“Ina ka samo?”

 

“Ke dai ka bar”

 

“Dan girman Allah Faruq ka daina mana cin bashi kana kara mana kanskanci a unguwa kamar kan mu farau talauci”

 

“Ba bashi na ci ba wayata na bashi jingina”

 

Bata ce komai ba ta karbi dari biyu kana ta bude ledar tana duba taliya da makaroni dake ciki sai maggi da mangyada.

 

“To wannan ledar fa?”

 

“Mama zan kaiwa”

 

Yana fadar hakan ya juya ya kalli dansa dake sharar bachi sannan ya fice ba dan ranta ya so ba.

 

“Mu ba mu wadatu ba amman sai dauka ka kaiwa wasu, mtchhhh”

 

Ta karasa tana jan tsaki.

 

“Kuma Wallahi sai na zubar da cikin nan haka kawai zan zauna ga talauci ga wahala da kurciyata da kyauna”

 

Ta fada tana mikewa tsaye ta dauki ledar taliyar ta fito waje domin sarrafawa. Kallo daya zaka masa ka karanci damuwarsa abubuwan duniya sun taru sun masa turr kamar ya zagi arziki kamar komai yake juye masa, gashi yayi degree amman aiki ya gagara duk inda yai applying shiru ba wani motsi. Da tunani kala kala mai achaba ya sauke shi unguwar Dallatu wato gidan mahaifiyarsa, sai ta ciro naira dari a mika masa sannan ya ratsa cikin gidanje har ya isa kofar gidan ya tura ya shiga da sallamarsa. Kanensu biyu mata da suke tsakar gidan suka amsa masa suna masa sannu da zuwa, bayan ya amsa musu ya nufi dakin Mahaifiyarsa ba karamin faduwa gabansa yai ba ganinta a kwance domin ba al’adarta bace yawan kwanciya musamman a irin wannan lokacin.

 

“Mama lafiya dai? Ko jikin ne?”

 

“Da sauki ai Alhamdulillah”

 

Ta amsa masa tana murmushin karfin hali.

 

“Wani irin da sauki ga ki kwance? Kai Innalillahi Wa’inna illahirraji’un”

 

Jin furuncinsa yasa ta yunkura ta tashi zaune tana kallonsa.

 

“Ina Sultan?”

 

Kasa amsawa yai sai kallon mahaifiyarsa yake, yana jin kamar ace yana arzikin da zai iya kaita Asibiti, domin ba yau ciwon ya fara ba.

 

“Mama ko dai maganar auren Aisha da akai ne jiya ya tada miki hankali? Idan ma fasa aurenta zai yi ai ba wani abu ba ne zata samu wani”

 

“Har aure nawa za’ayi ta fashi ne Faruq? Haka zamu ta zama ana fashin aure saboda talauci? Kuma yaran nan sai girma suke, sai gulma ake mana a unguwa”

 

Ta tambaya idonta tab da hawaye, Faruq yayi saurin kawarda nasa idon yana sauke ajiyar zuciya, domin kukan mahaifiyarsa na daga cikin abun da ya fi tsana a rayuwarsa.

 

 

 

 

________

 

Na zo muku da albishir guess what? A have alot of kayan mata masu kyau gaske, akwai na infection, akwai maida tsohuwa yarinya, akwai set din da ake hadawa for matan da basa gane kan mazajensu, akwai na mallaka kala kala, muna kaza mai magani, tantabaru, akwai kaza mai Yasin, akwai na mallaka sirrine mai karfin gaske. Ina masu son zama madubi a gurin mazanje su? Ina matan dake cewa na gwada ban dace ba? Muna da gumba da garin magani kala kala da na tsarki ga Humra da turarunka kala kala amman fa na kayan mata.

Ga masu bukata za su iya tuntubar number na 08036126660 zan saka miki a mota na aika miki har inda kike da yarda Allah.

 

Serious Buyers please, idan ba ki shirya ba kar mu batawa juna lokaci.

 

riginator=ZCqcO2wXIv6pkkxIr3do4ng1%2BTHhzoVPTPFtpfDcb1ftHOVsldMflpG2lAwd5aYtrehJ12WEeerjWSVNDZunKAH9QpxhI0A%2BzJsYI6RrshbTOZsoLUXljeZDCPaDNtKr

 

 

*💔 BAKAR WASIKA 💔*

 

 

By Khadeeja Candy

 

 

Page -3️⃣

 

Shigowar Daddy ne yasa Momy ta cire farin gilashin idonta tana murmushi.

 

“Ranka ya dade an fito?”

 

Kusa da Amal ya zauna yana murmushi.

 

“Allah ya yarda”

 

Ya fada yana karewa katon falon kallo ganin Momy ce kawai sai Khadija da kuma Kabir, abun da ba kasafai yake gani ba, ya saba every weekend yana zuwa falon Momy ya zauna tare da ita da kuma yaransa, kowa ya fadi bukatarsa ayi hira a bawa juna shawara, ayi nishadi. Sometimes kuma shi zai kira su a bangarensa a tare a can.

 

“Daddy barka da wuni”

 

“Yauwa, Son”

 

Ya amsawa yana yi ma kowa kallon tsanaki, ciki har da yar autarsa Amal da ta wani hade rai.

 

“Hajiya ya ga falon ku kadai? Ina sauran yarana suke?”

 

Momy ta kalli Kabir dake kallonta sannan ta kalli Amal kamin tace komai Kabir ya tari numfashinta.

 

“Daddy yaranka biyu fushi suke da juna, kasan Angry Birds ne”

 

Daddy ya kalli Momy.

 

“Since when?”

 

Kabir zai sake magana Daddy ya dakatar da shi ta hanyar daga masa hannu, wanda hakan ke nuna kai tsaye Momy yake son ta amsa masa tambayarsa. Momy ta sauke ajiyar zuciya.

 

“Ni ma dazun nan na sani…”

 

A tsanake ta labarta masa abun da ya faru ciki har da fadan da tai ma Leila.

 

“Amman baki fada min ba? Taya zaki bar Mu’az ya fita ba tare da yayi breakfast ba? And baki dama ki san a wane hali yake ba?”

 

Momy ta lumshe ido ta bude tana murmushi.

 

“Wani lokacin kana maida Talba kamar wani karamin yaro, ya san yadda zai kula da kansa Alhaji”

 

“Ko da Mu’az zai shekara dari matukar ina raye to shi yaro ne a gurina, a shirya mana abincin rana tare”

 

“An gama ranka ya dade”

 

Ya mike tsaye sai Amal ta kalleshi.

 

“Daddy ni ma fa kaga ina fushin nan amman baka ce komai ba”

 

Sai a lokacin Daddy ya tuna da tana gefensa sai ya kalleta yana murmushi.

 

“Amal sorry wata taba ki?”

 

Ta nuna Kabir sai Kabir yai saurin daga hannayensa sama ya mike tsaye.

 

“Na ma bar muku falon”

 

Kamin Daddy yace komai ya nufi kofar fita daga falon da saurinsa yana murmushi.

 

“Mu yi masa uzuri amman yau kawai next idan ya sake tsokanarki zamu raba gari da shi”

 

Daddy ya fada yana kallon kyakkyawar yarsa. Sai ta sakar masa murmushi.

 

“Toh Daddy”

 

“Good”

 

Cewar Daddy yana ciro wayarsa ya kira Talba, ringing daya yai picking kamar daman can kiran yake jira.

 

“Hello Daddy”

 

“Mu’az kana Ina?”

 

Ya kalli katon office din da yake ciki kamar mai son tantance inda yake.

 

“Office Daddy”

 

“Me kake a office? Yau Weekend?”

 

“I don’t know…Getting some fresh air”

 

“Baka fada min kana da damuwa ba, mu da kai ba abokai ba ne? Ba ma boyewa juna abu?”

 

Wani irin kasaitaccen murmushi ne ya bayyana a fuskarsa, ya mike tsaye daga inda yake zaune ya nufi windows.

 

“Daddy ba irin wannan ba you know dan crisis ne kadan”

 

Daddy ya tabe baki yana juya fuska kamar  Talba na gabansa.

 

“Uhm.. Ka dawo gida yanzu zamu yi lunch tare”

 

“Okay Daddy Allah kara maka lafiya, i love you”

 

Daddy yayi murmushi ba tare da yace komai ba ya sauke wayar, sannan ya nufi wata kofa a dayan bangaren falon wanda zata sadashi da bangarensa.

 

“Ita Leila ba ya bace kenan? Da ba zaka kirata ka tambayi inda take ba?”

 

Daf da zai wuce Momy ta yi wannan maganar sai ya juyo ya kalleta, sannan ya dauke kai ya bude kofar ya fice.

Sai da ya rufe kofar sannan Momy ta tabe baki ta kai hannunta ta dauki wayarta ta kira Leila, sai da wayar ta kusa yankewa sannan Leila ta daga.

 

“Leila kina ina?”

 

“Gidansu Madina”

 

Ta amsa murya can ciki.

 

“Ki dawo da wuri, and make sure kin ci abinci”

 

“To Momy”

 

Momy ta sauke wayar sannan ta mike tsaye ta nufi kitchen.

 

Misalin 2:30pm Talba ya daka motarsa harabar Daddy, ya fito ya nufi bangarensa kai tsaye hannayensa duka biyu zube a alhaji, tafiya yake kamar wanda baya son shiga bangaren, haka yake idan yana fushi be cika son ya rabi mutane ba ko kuma mutane su rabe shi, a tunaninsa tare da kowa zasu ci abinci, domin Daddy ya saba zuwa bangaren Momy ya zauna a ci abinci rana tare ko na dare wani lokacin har da na safe, sai dai yana yin haka ne kawai ranar kun Assabar da Lahadi. Domin ranar weekend ba ya fita ko’ina sai idan fitar mai dalili ce kamar daurin aure ko wani abun, wannan al’adar ba shi kadai ba har yaransa sun saba da ita, every weekend zaka samu kowa a gida sai mai dalilin fita yake fita.

Ya samu kusan dakika 40 zuwa 50 sannan ya danna door bell din kofar falon Daddy, babu bata lokaci Amal ta bude masa kofar.

 

“Ya Talba”

 

“Lil Sis… Waye da waye a ciki?”

 

“Just me and Daddy”

 

Ya sakar mata murmushi sannan ta shiga cikin falon, tun da ya hango dinning din babu komai a kai ya tabbatar daga shi sai Daddy za su ci abincin. Kai tsaye ya wuce karamin Falon Daddy inda ya saba zama. Yana shiga ya samu Daddy zaune saman kujera yana amsa waya, sai ya zauna a inda aka jera manyan kuloli ya dauki plate biyu ya zubawa Daddy shimkafa, ya zubawa kansa a dayan plate din sannan ya bude miyar dake ta kamshin naman kaji ya zuba ma kansa kadan domin ba ya son miya tai yawa a abinci ya zubawa Daddy ta jera kofuna biyu ta zuba musu lemu ya hada komai sannan ya dauki na Daddy ya dora masa a dan karamin center table dake gefen kujera da Daddy yake kai. Sannan ya koma ya dauko na shi ya dawo kusa da Daddy ya zauna a kasa, ya soma cin abinsa yana kallon katuwar plasma dake karamin falon, Bayan Daddy ya gama wayarsa ya kalli Talba.

 

“Na lura har yanzu baka san ka girma ba Mu’az, ya kamata ka koyi hakuri da iya danne fushi, idan ina kiranka na damu da inda kake, wata rana bana nan, domin akwai rayuwa akwai mutuwa, na san kana kokarin ganin ka kawarda damuwa a zuciyar wasu musamman yan’uwanka, amman kai baka san yadda zaka yi ka cire kanka a damuwa ba, sai dai ka karawa kanka”

 

Talba ya dakatar da cin abinci da yake yana sauraren Daddy ba tare da ya kalleshi ba.

 

“Ka daina fushi da abinci idan ranka ya bace, And su mata ba a fushi da su, lallabasu ake, idan ka san wahalar da na sha kamin ya auri Amina sai ka ji ka tsani matar nan, amman haka na daure dan marayan Allah da ni har Allah ya ba ni ita”

 

Talba ya kalli Daddy yana murmushi mai sauki.

 

“Haba Daddy”

 

Daddy ya kalleshi yana dariya.

 

“I’m telling you my friend”

 

Daddy ya kai hannunss ya fara cin abinci.

 

“So haka zaka yi hakuri kai ta lallabata, mata soyayya suke so da kulawa, no matter how rich they are, anya ma kana kiranta da safe ka ji ya ta tashi? Like hello Baby how was your night?”

 

Talba ya saka dariya sosai har yana kwantawa jikin kujerar dake bayansa. Daddy ma Murmushi yai.

 

“Yes… Gida daya muke da Hajiya kuma a guri daya muke kwana amman kana gani kullum sai na gaishe, ni ban san abun da yake damun ku yaran yanzu ba, mu a da kunya da rashin wayewar addini ya saka iyayenmu da mu kanmu ba su yi wasu abubuwan na more rayuwar aure ba, amman ku a yanzu ga ilmin addini da na zamani a arha ga wayewa amman kuke ta zaman matsalar zamantakewar aure, ban san miye matsalar matasan yanzu ba”

 

“So that’s mean nine mai laifi kenan?”

 

“Kai ne mana, taya zaka samu mace kai tsaye da irin wannan maganar, bana jin yadda kake zaunawa kai hira da ni kana yi da ita ma, kawai kai gaka boss, gaskiya you’re not romantic at all”

 

Daddy ya karasa yana wani yatsina fuska, wannan karon dariya sosai Talba yai har muryarsa tana fita kamar ba shi ba, dariyarsa ce ta saka Daddy murmushi mai sauti.

 

“Trust idan baka canja ba, za a iya kasa ka”

 

Ya daga kafadunsa alamar be damu ba.

 

“Then ai zan samu wata da gudu ma”

 

“Hakan na nufin ba wani son Leila kake ba, because idan kana son ta you won’t said that”

 

Ya dan yi shiru kamar mai nazari.

 

“No i love her Daddy kawai dai ina sonta, but i won’t tolerate nonsense”

 

Daddy yayi Murmushi yana dafa kafardarsa.

 

“Idan so ya zurfafa a zuciyarka, baka san lokacin da za ayi maka nonsense ba kuma ka dauka, a lokacin zaka zama wani stupid, fool, za a fada maka baka ga tana maka kaza ba, kace ka ji amman kana sonta ba zaka taba ganin laifin abun da take maka ba, mark my words”

 

Talba yayi murmushi irin murmushin nan dake nuna ban yarda ba, ranar ma ba zata zo ba.

 

“Yanzu ka gama cin abinci kaje ka samu Leila duk inda take ka dauko ta ka dawo da ita gida, kuma ka bata hakuri”

 

“No no no Daddy kasan ni bana ba wanda yake kasa da ni hakuri”

 

“Ba sai kace mata sorry abun da nai ban kyauta ba, no ka mata abun da zata ji farinciki sai ta manta da komai simple”

 

Ya dan yi jimm yana jin kamar an dora masa katon aiki.

 

‘Maybe i can try’

 

Ya fada a ransa a fili kuma sai ya amsawa Daddy da.

 

“Okay Daddy, for the sake of you”

 

Daddy yayi murmushi yana jinjina lamarin dansa.

 

FARUQ POV.

 

A gidan Mahaifiyarsa yai wanka sannan ya fito ya nufi gurin abokinsa, dake unguwar. He got lucky yana gida, yana sallama masa ya fito, bayan sun gaisa Faruq ya gabatar masa da abunda ke tafe da shi.

 

“Shamsu, na zo neman wata alfarma ne a gurinka”

 

“Allah yasa zan iya Faruq”

 

Faruq ya busar da iskar bakinsa.

 

“Wallahi ina cikin matsaloli ba ma daya ba, kasan matsalar kasar nan, mutum zai yi karatu amman aiki shiru, ga dan shagon da na kama sabuwar unguwa ce ba mutane sosai”

 

“Wallahi kasar ce har ka rasa yadda zaka misalta ta, abubuwan sai a hankali, idan baka yi karatu ba abun ya dame ka idan kuma ka yi aikin ya gagara”

 

“Shine nake son na fara koyon irin sana’arku, duk da ba iyawa nai ba amman dai idan nayi tare zan iya da yarda Allah”

 

Shamsu ya masa wani kallo na mamaki, a tunaninsa zai ranci kudi ne a hannunsa, sai ya ji yana masa maganar sana’arsu, ba Shamsu kadai ba kusan duk wanda ya ji mutum mai degree zai yi sana’ar gini zai yi mamaki, domin muna a zamanin da masu degree da kuma mutane suke ganin ba ko wane irin aiki ne ya dace da su ba, wani abun ana ganinsa kamar kaskanci ne, ace kana da degree kuma kai yi shi.

 

“Faruq zaka iya sana’ar gini kuwa? Kai da kai karatu? Kuma jikinka be saba da aikin wahala ba”

 

“Shamsu kenan, wanda ya tashi a area kamar wannan kuma dan talaka zai ce be saba da aikin wahala ba? Ya kake magana kamar ba san gidan da na fito ba?”

 

“To abun ne da mamaki Faruq naga kai ka yi karatu ka ni ban yi karatun ba”

 

“Ka aje komai a gefe ka duba bukatata idan zai yiyu”

 

“Inshallahu, sai dai ka san aikin mu tasowa yake ba wai kullum ba ne sai idan ta samu, inshallahu da mun samu zan kiraka a waya tun da ina da number ka”

 

“To na gode sosai sai na jika”

 

Ya mika masa hannu sukai musabaha, Shamsu ya koma cikin gidansa cike da mamaki, Faruq kuma ya nufi titi cike da damuwa.

 

FEE’AH POV.

 

“Gaskiya kina da kyau sosai”

 

“Thanks”

 

Shine reply din da tai ma mutumen da facebook bayan ta tura masa hotunanta masu kyau, kamar yadda ya bukata.

 

“A ina kike da zama a Gusau?”

 

Wannan karon tashi tai zaune tana tunanin irin karyar da zata masa, domin bata fada masa cewar tana da aure ba, duk kuwa da kasancewar bata dora hotonta a profile picture ba, sai hoton sunan Allah data saka as her profile picture dinta.

 

“Gida dari”

 

Ta bashi amsa.

 

“Na san gurin idan na shigo zamfara inshallahu zan neme ki mu gaisa”

 

“To Allah ya nuna mana”

 

Ta bashi amsa tana murmushi, kamin ta sake shiga profile dinsa ta duba komai nasa, ciki har da gurin da yake aiki da kuma hotunansa, kana ganinsa ka ga wani hamshakin mai kudi mai connection da yan siyasa, domin yadda ake masa fadanci a profile ma ya isa ya sanar da hakan. Murmushi ta sake yi sannan ta dawo inbox din ta duba tambayar da yai mata ta biyu.

 

“Are you on whatsapp?”

 

“Yeah”

 

Ta bashi amsa da sauri tare da rubuta masa number wayarta ta tura masa.

 

“Okay Thank You so much Baturiya”

 

Ta sake fadada fuskarta da murmushi tana jin sunan har cikin ranta. Sannan ta fita facebook din ta shiga whatsapp, few massage ta samu ciki har da reply din da MD Saleh yai mata, shi ta fara budewa da sauri jikinta har rawa yake kamin ta gama karantawa.

 

“Subhanallahi, Allah ya wadata, turo account number dinki”

 

Mikewa tai tsaye ta daka wani uban tsalle ta dire tsabar murna da jindadi sannan ta tura masa account din tana masa godiya.

 

“Alhamdulillah”

 

Ta furta sannan ta shiga group chat dinsu na makaranta, ta fita ta leka na matan aure ta fita ta shiga na novels nan ma bata dade ba ta fita ta bude chat din Ramlee.

 

“Kawata kin yi ciniki, wani ya ga Hotonki a wayata ya matsa na nemo masa ke”

 

Tana gama karanta sakon kawarta Ramlee ta zaro ido tare da sakin baki a lokaci daya, domin ta san sana’ar kawarta, tana da connection da manyan masu kudi tana hada su da mata kyakkyawa kuma masu siga kamar yadda ita ma take hulda da su, sai dai duk iskanci Baturiya bata taba aikata alfasha ba, za dai hadu da mutum har su gaisa ko kuma ta yi masa nata wayon ta waya ta samu yan canji, amman bata san tai mu’alama da maza ba, bayan Faruq babu wanda ya taba saninta a ya mace.

 

“Gaskiya aa Ramlee ni dai ina jin tsoro ba zan iya ba, amman idan kin san irin wanda zan yi ma wayo ne na ci kudinsa ba sai mun hadu ba, ba matsala”

 

Ta mayar mata da amsa duk da kasancewar Ramlee tana Offline a lokacin, sannan ta kashe datan ta aje wayar ta mike tsaye ta fito waje.

 

“Sultan zo nan yau zamu ci kaza”

 

Ta fada tana zaunawa jikin kofar falon tana mikawa danta hannu fuskarta cike da murmushi kamar yadda zuciyarta take fal da farinciki saboda kudin da za a turo mata, Sultan din ya rugo da gudunsa yana murna.

 

“Abba zai siyo mana ne”

 

Ta shiga kabe masa riga tana fadin.

 

“Ba nace ka daina cewa Abba ba? Ka rika cewa Daddy, yayan talakawa ne suke cewa Baba ko Abba, yaran masu kudi kuma su ce Daddy ka ji?”

 

“To Daddy ne zai siyo mana?”

 

“Aa adashen zan kwasa yau sai na siyo mana, amman karka fadawa Daddy ka kaji? Har da lemun kwalba zan siyo mana”

 

Sultan din ya shiga murna yana jindadi yau za su ci kaji, rabon da su ci nama har ya manta.

 

AMINATU POV.

 

A bakin kofar shiga gidansu ta hadu da Sanusi tsaye yana latsar karamar wayarsa.

 

“Ya Sanusi”

 

Ya kalleta sai kuma yai dariya.

 

“Igee ai sai ki fada mana cewar kin fara fita zance, mu shirya yi miki aure”

 

Ta cinno baki gaba.

 

“Ni dai dan Allah ka daina, Allah yasa ba ka fadawa Inna ba ko Baba”

 

“Ban fada ba, amman dai zan fada masa, Baba ma baya nan”

 

“Ina yaje?”

 

“Gwaggo ta Makka aka aiko bata da lafiya sosai, shi ne suka je tare da Junaidu a babur”

 

“Yanzu?”

 

“No tun dazun”

 

“Allah ya bata lafiya shi kuma ya dawo da ita lafiya”

 

“Inna tace naje na dubo ki, idan kin shiga ki ce ni na zo da ke”

 

“Wallahi ba zan fada ba”

 

Ta fada tana nufar cikin gidan.

 

“Ni kuma zan fada mata cewar kin yi saurayi”

 

“To na bari”

 

Ta yi saurin fada har tana dawowa baya, sai ya saka dariya ya biyo bayan kanwarsa suka shiga cikin gidan tare. Kamar Kullum inna na zaune tsakar gidan tana jiran dawowarta, domin bata bachi sai ta saka yarta a ido.

 

“Oyoyo Auta yar albarka, an siyar ko?”

 

Aminatu ta aje kwallon tuwon da bokitin miyar da plates din roba a gaban ina tana sauke gajiya.

 

“Eh Inna wai Baba ya tafi gurin Gwaggo?”

 

“Eh an aiko bata da lafiya, aka ce mai rabon ganawa da ita ya zo”

 

“Allah ya bata lafiya”

 

Ta fada cike da damuwa, sannan ta ciro kudin cinikin ta mikawa Inna, sai da Inna ta kirga kudi ta ga sun cika sannan ta cire wadanda ta saba bata tana sakawa a asusu ta mika mata.

 

“Ga na ki”

 

“Na gode”

 

Ta fada bayan ta karba tana kallon Sanusi zuciyarta sai raya mata take zai fadawa Inna maganar, sai har sukai yar hira da zasu yi suka gama bata ci ya dauko zance ba, hakan yasa ta ji dadi sosai. Bata bude wasikar da Maniru ya bata, da fitilar da take zuwa talla ta haska wasikar da ya rubuto mata da hausar ajami, tana karantawa sai murmushi take tana jindadin yadda ya jera mata kalaman soyayya da kwantar da hankali.

 

Bayan ta gama karantawa ta rumgume wasikar a kirjinta, can kuma ta tashi ta saka a cikin littafanta na Islamiya kamar yadda ta saba, sannan ta gyara gurin kwanciyarta ta kwanta. Inna kam bata kwanta ba sai da ta gama komai ta kintsa komai kamar yadda ta saba sannan ta kwanta tare da rage fitilar kwai dake dakin, hasken ya rago sai dai bata kashe gaba daya ba saboda Aminatu na tsoron duhu sosai, bata bachi babu fitila a kusa da ita.

Misalin 12am gidan yayi tsit domin kowa ya nemi gurin kwanciya ciki har da yan awaki da tumakin da ake kiwo, can cikin bachi Inna ta soma jiyo hayaniya, tare da karar babura hakan yasa ta ta tashi zaune tana sauraren jikinta na bata ba lafiya ba, domin kowa ya san matsalar kasar a yanzu, balle kuma su da suke kauye. Aminatu kam sharar bachinta kawai take bata ma san ana yi ba, jin ihu da kuma fadar Innalillahi a makota yasa Inna ta nufi inda Aminatu take ta shiga tashinta.

 

“Auta Auta”

 

Ta fada murya can kasa kasa, a hankali Aminatu ta bude ido ganin Inna yasa ta tashi zaune.

 

“Inna…”

 

“Shiiiii”

 

Inna ta mata alama da tai shiru. Wanda hakan yai daidai da banko kofar gidan ta kwano a shigo, ga wata uwar fitila mai shegen haske da suke ta hasken gidan da ita.

 

“Innalillahi Wa’inna illahirraji’un”

 

Inna ta furta gabanta na bugawa da mugun karfi, Aminatu ta mike tsaye da sauri kamar wanda ta rude, Inna ta shiga duba dakin tana jin kamar ace akwai wata hanya da zata bi ta fita, a rikice ta nufi gadonta.

 

“Shiga nan Auta shiga shiga”

 

Da sauri Aminatu ta nufi karkashin gadon na karfe ta shige, zuciyarta na wani irin zillo kamar zata fito, Inna ta nufi kofa domin duba sauran yayanta sai dai kamin ta isa kofar suka shuri kofar da mugun karfi ta cire suka shigo cikin dakin kamar an aikosu. Baya baya Inna tai tana fadin.

 

“Innalillahi Wa’inna illahirraji’u”

 

“Rufe mana baki dan ubanki”

 

Yanayin yadda yai maganar da karayar halshe kadai ya isa ya sanar da cewar gayu ne suka hauro garin a yau, wato bandits abun da ba a taba ba, domin duk wani hargitsi da ake fama da shi sai dai su ji a makotan kauyukan ko kuma a hanya abun ya rutsa da yan garin, amman ba a taba shigowa cikin garin ba. Ba Inna kadai ba har Aminatu dake karkashin gado sai da ta saka hannayenta ta rufe bakinta. Ta ko’ina jikin Inna rawa yake, ganin manyan makaman da ke hannunsu.

 

“Ina mijikin yake?”

 

Kasa magana tai bakinta sai rawa yake kamar jikinta ga wani gumi dake karyo mata.

 

“Wato ke ce uwar yaran ga yan iska ko?”

 

Nan ma Inna kasa cewa komai tai sai ambaton Allah take a zuciyarta, hannayenta duka biyu rike da bakinta.

 

“Innalillahi”

 

Inna ta jiyo muryar yayanta a tsakar gidan, wani irin abu ne ya ziyarci zuciyarta sai ta ji kamar ace akwai abun da zata iya yi ta ceci yaranta.

Dun dun dun ta ji tashin bindiga kamin ta tantance komai ta ji muryar Sanusi yana kuka.

 

“Wayyo Allah na, la’ilaha illahu, Innalillahi”

 

A lokacin ne hawaye ya cika idonta, irin hawayen da kowace uwa take yi idan ta kasa taimakon yayanta.

 

“Wayyo”

 

Ta jiyo ihun matar Amadu, bata san da inda kuzari ya zo mata ba har ta iya tambayarsu kamar ta rikice.

 

“Me muka muku?”

 

“Tambaya ma kike? Ba kun aje yan sakai a gidanku ba, wai masu yaya ko? To yau sai mun kashe su sai mun muku wulakanci”

 

Inna ta hade hannayenta biyu tana kuka tana rokonsu.

 

“Ku dubu girman Allah ku yi hakuri, ku kashe ni kar ku kashe yarana dan Allah…”

 

Bata gama rokon ba, wani ya karaso kusa da ita ta fisgi rigar jikinta.

 

“Cire wannan rigar ai har ke da kike uwarsu ba zamu bari ba”

 

Sai a lokacin Inna ta kara firgicewa, ta fara bin fuskokinsu da kallo tana ganin komai kamar a mafarki.

 

“Cire cire”

 

Sai ta rika jin kamar ba hausa suke mata ba, gaba daya ta rasa gane abun da suke nufi, bata fahimci manufarsu ba har sai da suka barge rigar dake jikinta suka kama zanen shi na suka fisge suka jefar da shi can gefe, suka mata tsirara a gabansu. Aminatu dake karkashin gado ta yi saurin kara rufe bakinta wasu irin zafafa hawaye na sauko mata, saurin rumtse ido rai hango mahaifiyarta tsirara a kwance yaron da be wuce sa’ar danta na biyar ba ya fara keta mata haddi!!

Ba mutum daya yai ba, ba biyu ba, ba uku ba, ba hudu ba, haka suka jera su goma sha daya suka yi mata yadda suke so, sannan suka fita suka barta kwance kamar tsumma. Abun ka da uwa suna fita ta yi karfin halin rarafawa ta isa inda zanenta yake da idanuwan da take jin kamar kukanta ya kare a yau. Ta dauki zanen da hannunta amman yadda zata sarrafashi ta daura ta suturta jikinta ne ta manta sakamon jin ihun Sanusi, cikin rashin kuzari zuci da na jiki ta isa jikin kofar tana kallon yadda yan bidigar majiya karfi, suka danne Rilwanu a kasa, dayansu ya kunna babur dinsa ya hau ta kan wuyansa ya tsaya.

 

“La’ilaha Illahu”

 

Inna ta fada da wata irin muryar da bata taba sanin tana da ita ba, tana mika musu hannu. Ba su kulata balle su fasa abun da suke, ba su saukar da babur din a wuyansa ba sai da suka tabbatar ransa ya rabu da gangar jikinsa, daman haka suke ma irin su Rilwanu masu aikin sa-kai domin kare rayuwarsu da kuma ta al’ummarsu, idan suka halbeka da bingida suka ga bata tashi ba, sai su gwada adda, idan ita ma ba tai ba sai su saka dutse ko babur. Bayan sun kashe Rilwanu suka fashe rumbun hantsen dake gidan suka saka Iro a ciki suka kunna masa wuta, tare da hatsin. Wani irin ihu yake yana neman ceto amman babu wanda zai iya kawo masa dauki.

 

“Kaico Kaico kaico”

 

Inna ta fada tana kallon yadda danta ke ci da wuta, ga kuma wani a kwance, wani irin shiga da fita numfashinta ya rika yi da karfi, tana jin wani abu na mata yawo a ciki, gaba daya sai ta nemi dan sauran kuzarin nata ta rasa, a bakin kofar ta fadi kwance yawu da majina suna zubo mata a lokaci daya, cikin karfin hali ta dan dago kanta ta juyo ta kalli Inna Aminatu take boye, sannan ta juya tana kallon yadda suka dauko katon dutse suka daga sama suka saki a akan Amadu da yake da wasu barayin suka danne a kasa ko motsi baya iya yi, kamar yadda sukai ma Amadu haka wadancan barayin da suka zagaya gidan Musa suka masa, domin duk wanda ya san yayan Mai Damma ya san wuka ko bindiga bata hudasu, ya sha kuma ba bawa yaransa, ba dan komai ba sai dan kariyar irin wannan ranar, sai dai ayau shan be amfana musu komai ba, ba su kadai ba har da sauran mazan gari da bindiga bata fasawa, sukan kashe su da babur ko dutse, balle kuma Rilwanu da Iro da sukai kwarin suna a garin saboda aikin sa-kai da suke.

Sanusi kam sai yai kamar ya mutum ganin nasa mai sauki ne, domin da babur sauka hau kafarsa dan kawai su gana masa azaba, baya ambatar komai sai Allah, ba a gidan Mai Damma kadai ba, a garin gaba daya haka suka ci suka shude babu wanda ya kawo agaji, suka ci karensu babu babbaka yadda ransu ya so sannan suka bar garin bayan su kwashi abinci da mata cikin har da matan Musa da matar Amadu.

 

 

 

________

 

Na zo muku da albishir guess what? A have alot of kayan mata masu kyau gaske, akwai na infection, akwai maida tsohuwa yarinya, akwai set din da ake hadawa for matan da basa gane kan mazajensu, akwai na mallaka kala kala, muna kaza mai magani, tantabaru, akwai kaza mai Yasin, akwai na mallaka sirrine mai karfin gaske. Ina masu son zama madubi a gurin mazanje su? Ina matan dake cewa na gwada ban dace ba? Muna da gumba da garin magani kala kala da na tsarki ga Humra da turarunka kala kala amman fa na kayan mata. Akwai dan wata bakwai.

Ga masu bukata za su iya tuntubar number nan 08036126660 zan saka miki a mota na aika miki har inda kike da yarda Allah.

 

Serious Buyers Please idan ba ki shirya ba kar mu batawa juna lokaci.

 

I just published “04” of my story “BAKAR WASIKA”. adeejaCandy&wp_originator=gvBvvJY%2Brh7%2BfdxLjDxcLbTx9rDGdNBA0sMHgr3XMPr%2FqwZ4sIWJ88oZCr4nOa%2BILP0eBQ%2FKRLIQm73M62araHO6%2BoJXjoYprLv7YGhRYyguc1ysae3vRDycS1qvuqiM

 

*💔 BAKAR WASIKA 💔*

 

 

By Khadeeja Candy

 

 

Page -4️⃣

 

“So yanzu ka yarda zaka bata hakuri kenan”

 

Talba ta girgiza kai.

 

“Kai no never ni fa ba zan taba ba wanda yake kasa da ni hakuri ba”

 

Ali ya kalleshi.

 

“Amman ka ce Daddy yace laifinka ne, kuma kaje ka bata hakuri”

 

Yayi shiru kamar ba zai ce komai ba, sai kuma ya shafa kansa ya sauke numfashi a hankali.

 

“Yeah ba wai yana nufin na ce tai hakuri ba, ni yanzu so nake ka kirata ka bata hakuri kuma ka dauke ta ku je yawo ta wayance Shikenan komai ya wuce, amman karka ce ni na ce ka bata hakuri fa”

 

Ali ya rausayar da kai yana kallon abokin nasa cike da mamaki.

 

“Miye a ciki dan kace tai hakuri? Ko kuma ka dauke ta kuje yawo, faduwa kai?”

 

Sai Talba ya amsa masa kai tsaye.

 

“Yes, taya zaka bawa mace hakuri macen ma wanda take kasa da kai, ni me fa Ali”

 

“To wai idan kuka yi aure kuka samu matsala, kuma kai kake da laifi…”

 

Kamin Ali ya karasa Talba ya tari numfashinsa.

 

“Sai ta ba ni hakuri”

 

Ta fada da iyakancin gaskiyarta, domin har ga Allah be ga dalilin da zai saka shi bawa wanda ke kasa da shi hakuri ba, kuma mace sai dai shi a ba shi. Ali yayi murmushi.

 

“Yanzu dai for the sake of Daddy zaka yi”

 

“For the sake of him na zo har ina rokonka da kai, idan ba haka ba babu abun da zai saka na roke ka ma”

 

“Look Talba I’m not her boyfriend, ban san kalaman da zan mata ba, kuma ba ni nai mata laifin nan ba”

 

Talba ya mike, ganin hakan yasa Ali ma ya mike tsaye.

 

“Fine, amman tare za mu je, kana driving ina baya”

 

Talba be ce masa uffan ba ya nufi kofar fita, wanda hakan ya tabbatarwa Ali cewar ya yarda kenan. Sai da Ali ya shiga yai sallama da Samira sannan ya fito ya samu Talba a cikin motarsa. A hankali Talba yake tukin har suka fita daga cikin gidan suka hau titi.

 

“Kirata ka tambaye ta tana ina”

 

Ali ya masa wani kallo.

 

“Kiran ma? Talba wai kai zaka bata hakuri ko ni? Just ka kirata ka tambayi tana ina ma you can’t?”

 

Ko kallon gefen Ali Talba be yi ba balle ya tanka masa.

 

“Fine”

 

Ali ya fada sannan ya zaro wayarsa ya shiga contact dinsa ya nemo number Amal, domin baya son batawa kansa lokaci tambayar Talba number ta zai iya ce masa baya da ita ma. Ringing biyu ta dauka.

 

“Hello”

 

“Hello Lil Sis ya kike?”

 

Ta yi murmushi jin ya kiranta da sunan da Talba yake kiranta.

 

“Na’am Ya Ali ina lafiya”

 

“Good number Leila nake so”

 

“Okay zan turo maka yanzu”

 

“Thank You”

 

Ya aje wayar yana kallon abokinsa tare da mamakin halinsa. In few minutes Amal ta turo masa number, a take ya kira Leila, abun ka da mai jin kai sai da wayar ta yi ringing ta katse bata daga ba, har sai da ya sake kira, wannan karon ma sai da ta kusan yankewa sannan ta daga kuma tai shiru tana sauraren mai kiran, daman can haka take babu yadda za’ayi ka kirata kuma ka yi expecting ita zata fara maka magana, sai da Ali ya saka wayar a speaker sannan ya fara magana.

 

“Kanwata Leila kina lafiya?”

 

Jin muryar Ali yasa ta dan sake domin ta san waye shi.

 

“Ali ya weekend?”

 

“Alhamdulillah kina ina?”

 

“Ina gida dari gidansu Madina”

 

“Okay gani nan zuwa”

 

Be jira abun da zata ce ba, ya aje wayar ya kalli Talba.

 

“Idan munje ta fito kai zan bata hakuri sannan na baku guri ku yi magana”

 

Talba ya masa wani kallo irin really!

 

 

*** *** ***

 

Leila ta aje wayar tana tabe baki.

 

“Waye?”

 

Madina ta tambaya tana gyara kwanciyarta.

 

“Ali wai gashi nan zuwa?”

 

“To ko ya san abun da ya faru tsakaninku ne?”

 

“Maybe ai Talba baya boye masa komai”

 

“Kin gani na fada ya damu fa”

 

“Ya damu amman be kira ni ya bani hakuri ko ya aiko min da sako ba? Ni I don’t think Talba yana so Madina”

 

“Yana son ki mana Leila”

 

Madina ta fada sannan ta sauka saman gadon ta kama hannun Leila.

 

“Zo nan let me show you something”

 

Gaban madaubin dakin ta nufa da ita ta tsayar da ita gaban madubin.

 

“Kalli kanki da kyau Leila ki fada min abun da kika rasa”

 

Leila ta kurawa kanta ido a madabin tana kallon irin baiwar da Allah yai mata ta kyau daidai gwargwadon.

 

“Kyau?”

 

Madina ta tambaya sai Leila ta girgiza kai.

 

“Kudi? Lafiya? Kima, gata ko kuma me?”

 

“Ba ko daya”

 

Leila ta amsa.

 

“Kina da kyau da babu namijin da zaki yi tayin kanki ya ce miki aa ko waye shi kuwa, mahaifinki na da arziki da zai iya siya miki rai idan ana saidawa Leila, kina da kima, ga gata ta ko’ina, kuma duk wannan tarin baiwar da take tare da ke sai zuciyarki ta raya miki Talba baya son ki?”

 

Leila ta juyo tana kallon Madina

 

“Za ki iya fada min dalilin da ya saka yake min haka?”

 

Madina ta yi murmushi ta koma saman gadon ta zauna.

 

“Saboda Talba, na daya daga cikin irin mazajen nan masu matukar tsada da wahalar samu, kin ga duk wannan abubuwan da kike da su, Talba na da damar da zai iya cewa ba ya son ki idan har baya son ki, kuma ta zauna, domin kin san mutun ne da baya boye abu a ransa idan be masa ba, kuma babu wanda ya isa ya cilastashi, idan har baya son ki kai tsaye zai fada, amman be amsa cewar baya son ki ba ya amince”

 

Leila ta dan yi sama da ido.

 

“Haka ne but…”

 

Madina ta tari numfashinta.

 

“But Talba yana da matukar tsada Leila, Talba wani irin murdadden mutum ne mai wahala sha’ani, yadda kike takama da kyau yana da kyau, yana da dukiya, yana da duk wani abu da ake so a jikin namiji, yana da arzikin da yake jin zai iya tankwara komai yadda yake so, yana ganin tun da yana da komai dole a bi shi”

 

“Shi ne matsalarsa ai”

 

Leila ta fada tana zaunawa kusa da kawarta.

 

“Yeah ya kasa yarda cewar akwai abun da kudi basa siye, a nan ne kawai yai kuskure”

 

Leila ta yi murmushi.

 

“Ni kuma zan gyara masa wannan kuskuren, sai na nuna masa banbanci da sauran mata, dole ne ya san cewar ina da kima da daraja, kuma dole ya koyi yadda zai yi rayuwa da ni, all those four years of dating, ni nake bashi hakuri ko da ni ce da gaskiya, ina binsa kamar wani sarki da baiwa, all those years ni nake masa text how are you, so so so this, idan ya bar kasar nan ni zan kira shi na tambayi lafiyarsa, ko na masa sako, amman ko da rana daya Talba be taba daga waya ya tambayi ya nake ba! Idan na yi kwaliya be taba ce min kyau ba, be taba replied sakona ba, be san yai min kyauta irin ta masoya ba, balle har ya dauke ni muje yawo, ba zan taba yarda na aure shi a haka ba, now it’s my turn, dole ne ya canja”

 

Ta karasa yana yawo da idonta a dakin. Madina ta kama hannunta.

 

“No Leila mutane irin Talba suna da wahalar sha’ani, kuma suna da shaukin kai ga wanda ya iya zama da su, kar garin gyara ki ballo wata barnar, idan kin bashi hakuri a inda kike da gaskiya ai ba laifi ba ne”

 

“No dole ne ya gyara, yana son soyayya amman be san yadda zai nuna ta ba? Be san yadda zai biya ta ba? Ban taba kiran sunansa a gaban idonsa ba sai na sakaya, amman shi be taba gwada kirana da suna mai dadi ba”

 

Ta karasa tana murmushi.

 

“I’m such a fool”

 

Ta kai dubanta gurin wayarta da ta soma ringing. Hannu ta kai ta dauki wayar sannan tai picking.

 

“Hello?”

 

“Kanwata ga mu harabar gidan”

 

“Okay”

 

Ya mike tsaye ba tare da tunanin komai ba ta nufi kofar fita.

 

“Talba ne?”

 

“Ali dai Uhm Talba zai zo nan?”

 

Ta fada tana mere baki sannan ta fice, hango Motar Talba harabar gidan ba karamin mamaki ya bata ba, domin ko a mafarki bata taba saka ran zai zo ba, kuma bata zaton Ali ya aro motarsa ne. Tun kamin ta sauko entrance din ta canja tafiya, kamar wata hawainiya haka ta rika takawa kamar bata son karasawa kusa da motar.

Da gangan tai haka domin ta san a cikin abubuwan da Talba ya tsaya akwai jira, ko bata masa lokaci for nothing, mutum ne da yake daukar lokacinsa da muhimmanci sosai, dakika daya ko biyu idan ka kara, zai iya rushe ko miye a tsakaninku, hakan yasa yana girmama lokacin wani da ra’ayinsa.

Kamin ta iso Talba ya cika har ya kusan fashewa, ba karamin jihadi yai ba na bawa zuciyarsa hakuri har ta iso. Ali dake front seat ne ya sauke gilashin motar yana murmushi, Talba kam ko inda take be kallo ba sai taba wayarsa yake kamar his life depends on it. Kallo daya Leila tai masa ta dauke kai tana amsa gaisuwar da Ali yake mika mata.

 

“Lafiya Kalau”

 

Ta amsa tana kokarin juyawa. Sai Ali ya bude motar ya fita.

 

“Ina zaki je?”

 

“Ciki zan koma, baka fada min tare da wani zaka zo ba”

 

Kallon mamaki Ali yai mata, ganin ta yi abun da bata saba ba. Wani irin tafasa zuciyar Talba take kadan ya rage ta kone, bude motar yai ya fito a fusace ya zagayo inda take tsaye.

 

“Na zo nan ne, saboda Daddy ya saka ni, ba dan ra’ayina ba, na fi karfin daukar wulakancin mace ko wace iri ce, na fi karfi na bawa na kasa da ni hakuri wannan ranar ba zata taba zuwa ba…”

 

Ali ya rasa inda zai saka kansa, sai kawai ya koma cikin mota ya zauna, shi da ya zo sasanci sai kuma a sake yin fada a gabansa. Talba na gama fada mata haka ya juyo ya dawo cikin motar yadda ya rufe ganbun motar kadai ya isa ya sanar da bacin ransa.

Kamar wanda akai wa gorin tuki haka yai ribas ya rika danna horn, Mai gadin ya bude masa gate da sauri, ya firgi motar kamar wanda ya shirya bakuntar lahira.

 

“Wannan wace irin soyayya ce Talba me ke damunka, wai anya kana son Leila kuwa?”

 

Da mugun karfi Talba ya taka burki, he got lucky babu motoci da yawa a titin.

 

“Fitar min a mota”

 

Ya fada ba tare da ya kalli Ali ba. Ba sabon abu bane gurin Ali ya saba nasa haka idan ransa ya bace ko suka samu tsabani, sai dai baya hana anjima ya neme shi.

 

“Kana da matsala Wallahi kana da matsala, wannan mugun fushin ban san inda zai kaika ba”

 

Ali ya fada cikin bacin rai.

 

“Ka san bana son ana min ihu”

 

“Mtsssss”

 

“And i hate tsaki”

 

“Ba zan fita daga motar ba”

 

Ali ya fada yana gyara zama. A take Talba ya bude motar ya fita ya barta kunne, ganin hakan yasa Ali yai saurin fita ya zagaya driver side ya cigaba da tukin yana mamakin rayuwar Talba.

Gefen Titi Talba ya dawo ya tsaya, a ganinsa kaskanci ne ya shiga napep balle kuma ya hau babur zuwa gida, not just that even tsayin da yake a gafen titi ba girmansa ba ne, wayarsa ya ciro ya kira direban gidansu.

 

“Ka zo ka dauke ni zan turo maka location ta whatsapp yanzu”

 

Shine kawai abun da ya fada ya kashe wayar ya kunna datarsa ya shiga whatsapp dinsa ya tura masa location din, sannan ya maida wayar aljihu yana kallon titi, har lokacin zuciyarsa zafi take masa saboda Leila ta kira shi da wani, how on earth zata kira shi da wani?

After like 15 min direban ya iso, da kalle kalle har ya hango inda yake ya faka masa motar, Talba ya bude ya shiga ba tare da yace masa komai ba, shi ma direban be yi kokarin yi masa magana ba domin ya san Talba baya son yawan gaisuwa da kuma kallo, idan kuma kana son bata masa rai to ka cika shi da surutu.

Suna isa gida ya bude motar ya fita ya nufi bangarensu, wato shi da Kabir sai dai kowa side dinsa dabam, kai tsaye bedroom dinsa ya shiga ya jefar da wayarsa kan gado ya cire rigarsa da agogo ya shiga bathroom, sannan ya ciri jean din dake jikinsa ya kunna shower ya tara jikinsa yana kallon kansa a katon madubin dake facing dinsa a bathroom din, kamin ya dukar da kansa yana kallon zanen sunansa da tattoo dake kirjinsa wanda babu wanda ya san da shi sai shi kadai, can kuma ya dago ya lumshe ido.

 

 

 

AMINATU POV.

 

 

Kusan ko wane gida dake garin an taba, wasu an kashe wasu an kwashe duka da dabobi, wasu an tafi da yayansu da mata, wasu kuma anyi ma matan fyade, sai dai ba kamar gidansu Aminatu ba, domin wulakancin da akai wa mahaifiyarta ya wuce na kowa mutum goma shadaya a lokacin daya, kuma aka kashe yayyayunta hudu, aka kona rumbun hatsinsu, aka raunata wasu, aka kora dabobinsu.

Ba gidan kadai ba garin gaba daya tsit yai duk kuwa da kasancewar barayin sun yi iya barnar da zasu yi sun tafi, amman tsoro ya hana kowa fitowa, sai kuke kuke kake ji a gidanje, sai dai gidansu Aminatu ya fita dabam da baka jin kukan kowa, har asuba Aminatu na boye karkashin gado, mahaifiyarta kuma tana zaune a bakin kofar idonta a bude amman bata iya komai kamar an zare mata lakka a jiki haka take ji, Sanusi kuma na tsakar gidan a sume. Kamar macijiya haka Aminatu ta fito karkashin gado, ta janyo zanen gadon dake kan gadon karfe dan bono na Inna ta nufi Inna dake kwance tsirara tana kawar da idonta tana kuka har ta karasa kusa da ita ta kulluba mata zanen. Sannan ta juya ta koma inda fitilar kwai take ta dauka ta kara haskenta, ta taka kamar mai koyon tafiya ta fito waje. Wani rawa jikinta ya fara yi hango rumbun abincinsu na ci da wuta, sai kuma ta juya a hankali ta sauke idonta kasa ta kalli gawar Iro, da ta Amadu, ga kuma Sanusi shi ma dake kwance, kafa na zubar da jini, gaba daya ilahirin jikinta ne ya fara rawa kamar yadda bakinta ma yake yi.

 

“Ya… Ya… Ya.. Ya..”

 

So take ta kira sunan daya daga cikinsu amman ta kasa, hawaye sai aikinsu suke a fuskarta. Ta saki fitilar numfashi na fitar mata da karfi, wani kuma na shiga da sauri. Juyowa tai ta kalli Inna dake kwance bakin kofar har lokacin idonta na zubar da hawaye, sai wulakancin da akaiwa mahaifiyarta ya fado mata a rai, komai ya zame mata sabo.

 

“Me muka musu?”

 

Ta tambayi kanta tana wani irin kuka na fitar hankali, sai kuma ta ruga da dugu gurin yayanta Sanusi ta taba shi. Sai kuma ta juya ta kalli yayanta Amadu dake kwance kai a fashe, take ta girgiza kai.

 

“Ba da gaske ba ne aa, wannan be faru ba, yan’uwana ba su mutu ba, ba ayi ma mahaifiyata fyade ba, wadandan nan mutanen ba su zo ba, komai be faru ba”

 

Ta tashi da sauri ta ruga da gudu daki ta koma gurin kwanciyarta ta kwanta taja abun rufa ta lullube ta kame guri daya ta runtse ido, da gaske so take ta farka daga bachin, so take komai ya zama mafarki. Sai a lokacin Inna ta samu kuzarin motsawa ta fashe da kuka.

 

“Allah ka isar mana ga bayinka Allah….”

 

Ta fada tana kara fashewa da wani irin kuka mai ban tausayi ta taba zuciya. Jin kalamanta ne yasa Aminatu ta saka hannayenta ta toshe kunnuwanta ta kara runtse ido ta kwara wani irin ihu da muryar da bata taba sanin tana da ita ba.

 

“Aaaaaaaaaaaaaaaaaaaaa”

 

Ba makotansu kadai ba, har gidan dake tsakaminsu dashi gida biyar ne sai da suka ji ihun Aminatu.

 

 

 

>>>>>>>>>>

Anya Leila zata kai labari kuwa na cewar sai ta koyawa Talba darasi?

 

Nikan nace Ali yana hakuri da wannan aboki nasa mai wuyar sha’ani da jin Kai😕😠😡

 

Allah sarki Aminatu, ko da yake mahaifiyarta ce abar tausayi. 😭😭😭

 

 

________

 

Na zo muku da albishir guess what? A have alot of kayan mata masu kyau gaske, akwai na infection, akwai maida tsohuwa yarinya, akwai set din da ake hadawa for matan da basa gane kan mazajensu, akwai na mallaka kala kala, muna kaza mai magani, tantabaru, akwai kaza mai Yasin, akwai na mallaka sirrine mai karfin gaske. Ina masu son zama madubi a gurin mazanje su? Ina matan dake cewa na gwada ban dace ba? Muna da gumba da garin magani kala kala da na tsarki ga Humra da turarunka kala kala amman fa na kayan mata. Akwai dan wata bakwai.

Ga masu bukata za su iya tuntubar number nan 08036126660 zan saka miki a mota na aika miki har inda kike da yarda Allah.

 

Serious Buyers Please idan ba ki shirya ba kar mu batawa juna lokaci.

&lj

3 Comments

Leave a Comment

error: Content is protected !!