Bani da Hujja Hausa Novels Complete

Bani da Hujja Hausa Novels Complete

 

 

 

 

 

 

 

 

.

 

 

 

*BANI DA HUJJA!!*

 

By Maimoon

 

Elegant online writers📚

 

Free book

 

1-2

 

A hankali, cikin nutsuwa ya ke sauÆ™owa daga benen, but at the same time, cikin kuzari da taku irin na cikakkun mazaje, Æ™arasowa falon yayi, ba tare da ya ko kalli sashen da illahirin Æ´an gidan ke tsaye cirko cirko ba yayi wucewar sa, da idanu duk suka bisa kowa da irin abinda ya ke saÆ™awa a zuciyarsa, har ya fito farfajiyar gidan wanda ke shaÆ™e da motoci na alfarma, direct wata mota ya nufa mai matuÆ™ar kyau, kalar ash, buÉ—e motar yayi ya shiga sannan ya maida murfin ya rufe yana furzar da numfashi, har lokacin ba’a iya ganin furkarsa, bare asalin yanayin da fuskar ke ciki, saboda p-cap din da ke kansa, da kuma shade É—in idanunsa, sannan da handkerchief É—in da ya sa ya toshe daga hancinsa zuwa bakinsa ya É—aure ta baya. A hankali ya soma driving, har ya fice a gidan bayan mai gadi ya wangale masa tangamemen gate É—in, tafiyar da baifi ta minti ashirin ba, ta kawo sa Æ™ofar wani restaurant, wanda daga samansa aka rubuta AMAIRA RESTAURANT AND CO, sauka yayi tare da nufar ciki kai tsaye, cikin sauri wani ma’aikaci da ke sanye cikin uniform na ma’aikatan wajen ya Æ™araso wajensa, yana gaishesa tare da miÆ™a masa wata leda, karÉ“a yayi ba tare da ya amsa gaisuwar ba ya juya ya fice a wajen ba tareda ya furta ko da kalma É—aya ba. Motar ya koma, tareda barin wajen gabaki É—aya, sai da yayi tafiya aÆ™alla ta mintuna arba’in zuwa awa É—aya, kafin yayi parking a Æ™ofar wani Æ™aramin gida É—an madaidaici, sauka yayi ya tura gate É—in kasancewar babu mai gadin, sannan ya dawo ya shigar da motarsa, ya maida gate É—in ya rufe, ledan ya É—auka sannan ya rufe motar, yana tafiya cikin izza har Æ™ofar palon, makulli ya ciro a aljihunsa tare da buÉ—e kofar ya nufi cikin falon da ke da duhu matuÆ™a, karasawa yayi ba tare da ya kunna fitila ba, har ya kai tsakiyar falon, kafin ya ciro wayarsa tare da kunna haske, É—aki É—aya ne a cikin falon, hakan yasa ya nufi É—akin kai tsaye, wani makullin ya sake cirowa tare da buÉ—e Æ™ofar É—akin ya zura kafafunsa ciki, yana haskawa, kasancewar ya ma fi falon duhu.

See also  Ina So Hausa Novel

Haske ta yayi da fitilar wayarsa, ba tareda ya karasa inda take ba, ya ja ya tsaya daga bakin ƙofar yana ƙare mata kallo.

 

A zaune take, amma ta sanya kanta a tsakanin kafafunta, gashinta da ya gama cukurkudewa ya sauƙo ya rufe daga fuskarta har gwuiwarta kamar wata aljana, baka iya ganin furkarta sam, saboda irin zaman da tayi a cikin ɗakin mai matuƙar duhu.

Ƙarasowa yayi ga tsaya akanta kafin ya buÉ—e baki a karo na farko ya ce “keeeee” bata É—ago ba, sannan bata motsa ba, hannunsa yasa ya murza goshinsa, kafin ya zazzage ledan hannunsa a Æ™asa, wanda da alama yayi watanni babu shara, allura ya zaro ya haÉ—a, kafin ya saka handgloves a hannunsa, gashin ta ya kama ya ja da Æ™arfi, wanda ya bashi damar É—ago fuskarta, amma sai gashinta ya sake rufe mata fuska, ba tare da ya damu ba ya kama, hannunta, wanda ke É—auke da fararen yatsunta, ya zirara mata allurar, a hankali, ta soma buÉ—e idanunta, kafin ta soma motsa hannunta, miÆ™ewa yayi, cikin murya mai amo ya soma magana ” ga abinci kici, ga ruwa, idan kinaso zaki iya barinsa anan, saboda i have nothing to do with that, but alÆ™awarin da nayi ma kaina sai na cika shi at all means”

Daga haka ya juya ya fice tare da rufe Æ™ofar da makulli, tanajin ya fice, tayi saurin janyo abincin da ya tura mata gabanta, acikin duhun ta soma ci kamar zautacciya, tana ci tana shaÆ™ewa, saboda kukan da take rerawa”.

Yana jinta amma hakan bai sashi waiwayowaba, ya fice tare da rufe gidan gabaÉ—aya ya shige motarsa tare da barin unguwar ma gabaki É—aya.

Har ya iso gida, bai daina tsirtar da yawu ba, yana jin duk duniya babu wacce ya tsana irin ta, kuma ya ma kansa alƙawarin ɓatar da ita har abada.

Parking space ya nufa, a hankali ya gyara parking ya ziro kyawawan kafafunsa, masu É—auke da yatsu masu matuÆ™ar ban sha’awa daga motar bayan ya kashe ta, cikin tafiyarsa ta isa da matuÆ™ar izza da kuzari ya nufi cikin gidan, duk da aransa yana jin Æ´an wahalan har yanzu suna zaman jiran dawowarsa.

Kamar kuwa yadda ya yi hasashe, a falo ya same su, ga baki É—ayan su fuskarsu babu yabo babu fallasa,

Ciki ciki yayi sallama, ta yadda bayi da tabbacin wani acikin su ya ji shi, bai bi ta kansu ba ya nufi sama.

 

“Stop right there!”

See also  Rayuwar Nafisat Hausa Novel

Ya ji an faɗa a bayansa wanda yana da yaƙinin yayansa hamza ne, ba tareda ya bi takan abinda hamzan ya faɗa ba, ya sake cigaba da tafiya, uncle aminu ne ya sha gabansa yana faɗin

 

“Ba ka ji me yayanka ya faÉ—a ba? Ko bai kai ya dakatar da kai ba?, iyakar mu kake so ka nuna mana kamar yadda ka saba? Ina tambayar ka?” ya faÉ—a tare da hankaÉ—a kafaÉ—ar sa, ko gezau bai yi ba, sai idanunsa da suka kaÉ—a suka sakeyin jajur,

 

“Me ka mayar da mu mutanen banza? Muzo wajenka dan mu gana da kai ka sauko ka ganmu, sai ka fita ba tare da kace uffan ba, sannan ka dawo zaka sake hayewa sama, wato ga Æ´an iska koh? Kai waye, me kake jin kanka?”uncle Muhammad ya karasa fada ransa a mugun bace kasancewar yafi dukkansu zafi.

Karin wasu littafai da zaku so

Powered by: www.mynovels.com.ng
Har lokacin bai da alaman zai furta wata kalma, sai ma lumshe idanunsa da yayi yanajin wani mugun raÉ—aÉ—i a zuciyarsa

Hamza ne yayi Æ™wafa yana kallon uncle muhammad cikin magana da Æ™arfi ya ce “Dad ka gani koh na faÉ—a maka wallahi ba zai ce mana Æ™ala ba, uwarsa ce ta koya masa duk wannan halin, gaba É—aya”ya faÉ—a yana huci tare da kallon sa har lokacin yana tsaye Æ™iÆ™am, sai dai wannan karan yayi folding hannayensa a Æ™irji yana sauraron duk abinda suke cewa, jin Hamza ya ambaci umminsa yasa ya É—ago da mugun sauri ya dube sa, “Æ™arya yayi ne? Uncle Aminu ya faÉ—a yana kallonshi , a yanda idanunshi suka kaÉ—a sukayi jajir wallahi har tsoro zasu baka, jikinsa har wani É“ari yake, cikin jin É—aÉ—in zai tanka Hamza ya sake faÉ—in “Oh sorry, the mistress ya kamata ince, dan na tabbata tana can tana cin mazan mutane, matar da ke zaman kanta, waya sani ko kaima abinda kake yi kenan shiyasa ka keÉ“e kanka, ka rabu da family house ka dawo gidanka kai kaÉ—a……” Kasa Æ™arasawa yayi jin numfashin shi na shirin rabuwa da gangar jikinsa, sakamakon wani irin shaÆ™a da ya mai, ya haÉ—a shi da bangon É—akin ya shaÆ™e da iya Æ™arfinsa, zuciyarsa har wani racing take yi, handkerchief É—in da ya sa ya toshe fuskarsa da shi ne ya zame ya dawo Æ™asan wuyansa, ya subhanallah wani irin kyakkyawa ne, wanda ko me za ka kalla a jikinsa sai ya matuÆ™ar baka sha’awa, tun daga idanunsa da sukayi mugun ja, wanda kana gani kasan ba asalin kalarsu ba kenan, zuwa dogon hancinsa, da lips É—insa da sukayi masifar pink suna rawa tsabar bacin rai, har zuwa cikakken gemu da sajensa baÆ™i siÉ—ik da ya Æ™ara ma fuskarsa wani irin jahilin kyau da kuma cikar kamala, har zuwa hannayensa da ya sa ya shaÆ™e hamza da su masu É—auke da wasu irin yatsu masu matuÆ™ar birgewa.

See also  Yan Abuja complete

In a very shaky voice ya buÉ—e baki yiya ma Hamza magana cikin warning yana Æ™ara shaÆ™esa da iya Æ™arfinsa, “Don’t you dare, stay in ur limit, ummina……” Sai kuma ya kasa Æ™arasawa bakin sa ya shiga rawa sosai, Hamza da yaji Æ™amshin lahira, idanunsa duk sun firfito waje gabaki É—aya har wani yawu yawu yake

“ABDUL JALEEL” uncle Aminu da uncle muhammad da ya ga ana Æ™oÆ™arin hallaka masa É—a suka shiga kiran sunan sa dan da alama baya cikin hayyacinsa, “kashe shi zaka yi? Baka da hankali ne JALEEL, ka sake shi na ce” sam babu alamar ma yana jin su dan yanda jikinsa gabaÉ—aya yake rawa, da Æ™yar suka iya raba shi da wuyan Hamza, wanda zuwa yanzu yake Æ™oÆ™arin shurawa, wani wawan mari uncle Aminu ya sauÆ™e mai a fuska, yana faÉ—in lallai wuyanka ya isa yanka, ba shakka Asiya ce ta raine ka, to bari kaji dan uwarka ka faro abinda bazaka iya ba, kuma mun baka nan da wata bakwai (7) ka nemo mata muyi maka aure ko kuma kaga mata a gidannan, dan wallahi baka isa kana yawo kana fasiÆ™anci da yaran mutane a garinnan ba, kana É“ata mana suna, idan mu baka jin tsoronmu sannan baka É—auke mu komai, to tabbass zaka ji kira daga mai kankat wato mahaifinka UMAR kuma na tabbata kasan haduwarku da shi, dan gwara mu mara mutuncin yaro, É—an iska,”

Daga haka ya kama hannun Hamza da uncle Muhammad ke bama ruwa ko ta kansu bai bi ba, idanunsa sunyi jajir suka fice a gidan gabaki É—ayansu suka barshi nan tsaye.

 

 

 

 

Ku nuna ƙaunar ku akan wannan littafi, ya banbanta da sauran, akwai rikici mai ƙara rikitar da ƙwaƙwalwa da rikita-rikitar soyayya me rikitar da tunani ita ke wanzuwa a cikin sa.

Kudai ku cigaba da bin mu.

Yanda kuka karbi labarin shi zai bani dama da ƙarfin gwiwar cigaba.

 

Don’t forget, share and comment.

 

# Maimoon ce.

Leave a Comment

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Scroll to Top