
Banzar Mace Hausa Novel Complete
*BANZAR MACE*
*[ƘAZAMA]*
🅿️3️⃣&4️⃣
“`LOVE & ROMANTIC NOVEL“`
*PAID BOOK*
“`STORY & WRITEN“`
*BY*
“`ADAMA UMAR“`
[“`SECRET PEN“`]
wannan littafi na kudine .
Akan naira 150 kacal.
*Araha banza ko ,nayisa bononza saboda murnar anniversary na na shekara 6 shiyasa nayisa araha ,amma zuwa na gama free page ne idan na gama 200 ne*
“`Bonus subscribe idan kika kawo mutum uku suka sqya zan saki a group kyauta“`
DOMIN SANIN YA ZAKIYI KI BIYA TUNTUBENI AKAN
07081940768
SAINA JIKU MANYAN MATA
“Idan kinaso ki burge mijinki shine ki nuna masa duk duniya baa taɓa faranta miki ba kaman kina tare dashi ”
“Haba Uwar ɗaki yanzu wannan kuka da sambatun da yakeyi idan yanayi ɗin nima shin zan dinga yi ”
“Ai basai kinyi kuka ko sambatu ba kawi idan yanayi kina ɗan kakkamashi kina dam shafa kanshi shikenan”
“Ah kenan ina tayasa ”
“Eh mana abunda yake nufi kenan bakya tayasa anaso idan miji yana kwance dake karki sake jikinki kaman wata shanu ki kwanta komaj sai ya miki bayan kuma kema kinajin daɗi kaman yadda idan yana saduwa dake yake nuna miki kema haka zakina nunamai ke idan ta kama ki tashi tahau ki karɓa masa ne ma duk ba yadda baa yi zakuji daɗi. Muamala domin idan kika gane daɗin namiji ai ya shiga uku ”
Toshe fuska tayi tana kwace kanta a hannun me kitson ta ce
”
Yanzu Uwar daki akwai ranar da zatazo in iya yin wannan abun haka wannan ai sai maza nikam ma tsoronsa nakeji don yadda suke tsallen nan nikwm nayi zaa kwashi kqfofinq akaisu ɗori ”
”
Ba ɗori da zaa kaisu na tabbata haka mijinki ya nufi kuma inaso ki sanja kaman yadda ya nema kina taimaka masa domin a aure akwai taimakekeniya ”
“Shikenan aunty zan gwada “.
Haka sukan dinga hira tana bata shawa shiyasa takeson maman mubarak don tana bata shawarwari .
Haka tana kwance tana ta shirita harya dawo ya sameta kallon ta yayi tana kwance tana girgiza waya kallon ta yayi ya ce
”
Ke Maryam yanzune kikq tashi ?”
Juyowa tayi tana gyara zamqn ɗankwalinta ta ce
“Me haɗinka da yaushe na tashi ”
“Babu kawai naga babu abunda yasanja a falon sannan KO a kayak jikinki banga sauyi ba Iran ban manta ba wannan kayan ya kusa sati a jikinki ”
“Kai Shamsu babu ruwanka dani fa ka fita harkata me ruwanka jikinka ko nawa nifa banason sa ido ”
“Kicigaba da abunda kikeyi karki fasa dan Allah ,wlh Maryam randa kika kaini maƙura zanyi maganinki ”
“Idan bakayi maganina ba baka haifuba Shamsu kawai dan kaga ina barinka shine zaka tsaya rainamun wayo toni wasu mata ma ban yadda su tsaya na miji ya zagesu bare ni ”
tsaki yayi ya haura sama kaman bayajin me take faɗa yana kataicin kasancewar maryam a matsayin matarsa wannan wace irin BAZAN MACE ce Allah ya shirya ta yanw tafe yana zancen zuci bai jima da haurawa sama ba ya sakko da jallabiyaya shiga kitchen kallon kitchen ɗi. ya tsaya yi ya kwala mata kira
” maryam!”
Ko amsawa batayi ba can bai jimaba sai gata tazo ta kama ƙugu ta ce
“Gani waini me ke faruwa ne kaidai kanada yawan kira kaman wani makaho ”
“Ki duba kitchen ɗin kiduba jikin carbinet ɗin kaman ana tatsan mai a jiki waike Maryam anya bakida cutan hauka kuwa ”
“Kaine mahaukaci wlh nidai ba mahaukaciya bace ehen kuma bazanyi wanke²nba ”
“Eh ke bakyason aiki sannan kince bakyason me aiki to kisani bazan taɓa yadda kazantarki ta rusa gidanan ba dole insawa kaina mafita ni bazan iya rayuwa da BANZAR MACE BA ”
“kaje kadauki ko wani irin mataki da kakeso nidai babu ruwana kuma kasani baka isa ka kawo mata gidan nan ba ”
Girgiza kai yayi ya fita a ɗakin ya haura sama bai jima ha ya fito da makullin mota a hannunsa ya fita yabar gidan ,hakan baisa ta sanja raayi ba ta koma ta dauki wayarta ta ɗaura da chart ɗinta .
Yana fita ya kama hanya ya nufi gidansu yana shiga yakalli Shamsiyya akan kujera tana danna waya ,kusa da ita ya samu ya zauna ya karɓe wayar hannunta ya ce
“wai mesa ku mata kullum bakuda aikin da ya wuce danna waya ne da chart ”
“Ah rufamun asiri hamma ni wlh assignment nakeyi ”
Kallon wayar ya tsaya yi tabbas assignment takeyi ya ce
“Ina Umma ”
“Tana sama wajen Baffa ”
Tashi tayi ta nufi kitchen ta dauko masa abinci da ruwa ta kawo masa ,babu musu ya gyara hannun riga ya fara cin abinci ,yana cikin qbinci Umma ta sauko tana kallon ɗan nata cikin tausayi ganin yadda yake cin abinci babu ko tambaya rabon sa da abinci watakil tun karyawa ,tana mamakin matar Shamsu wannan wace Irin BANZAR MACE CE aure wata biyar amma gaba ɗaya mijinta ya fita a halin da yake ciki koɗan ƙiban angwayen nan ma baiyi ba gashi aikinsa bayida lokacin cin abinci tana tausayinsa sosai ,kasancewar Shamsu tun yana yaro idan aka ɗauki abinci aka bashi to zai karɓa amma koda yunwa zata kashe shi bazai taɓa cewa a bashi abinci ba idan akace mesa baya tambayar abinci sai ya ce Allah ya hallicci mutum kan ai dolene yaci duk wanda bai baka ba kuma ba mafanin ka tambaya to haka ya tashi ya girma kuma tana da tabbacin matarsa ma haka zaina mata shiyasa dazai shigo sau goma zaa bashi abinci sau goma kuma baya musu zaici koba yawa ,ƙarisowa tayi ta ce
“Haa Shamsu kaine tafe ”
Da sauri ya sauka akan kujera ya tsugunna ya ce
“Ina yini Umma ”
“Lafiya kalau Shamsu ya iyalin taka ”
“Tana lafiya Umma ”
“Masha Allah yau bakazo da safe ba ”
“Eh Umma na makarane shiyasa ”
Ayyah Dama akwai abunda nakeso in faɗa maka Baffanku ya ce
“Cikin satinan samuje kauye dan haka ka zaune cikin shiri kuma ka faɗa a company”
“Ba damuwa Umma Allah ya kaimu lokacin da rai ”
Haka tayi shiru tana kallonsu duk da a aladarsu ta fulani dole taji kunyan ɗan fari amma babu yadda ta iya haka ta a jiye alada tana jan ɗanta a jiki don tana tausayinsa sosai haka ta dinga zance zuci daga ci abinci ya koshi ya tashi ya ce
“Umma bari inje zanyi Sallah ta can zan koma company nagode Allah ya saka ”
“To Shamsu Allab ya tsare ya bada saa”
Tana faɗa tana mamakin halin Shamsu kullum ta bashi abinci saiya mata godiya kallon Shamsiyya yayi ya ce
“Maza ki ajiye wayanan ki tashi kiyi sallah”
“To”
yaya tace don inkanaso taga farin fushinsa kaƙiyin salla.
Yasa kai ya fita a gidan Umma ce ta juyo ta kalli Shamsiyya ta ce
“Shamsi bakiga raman yayanki yana ƙaruwa ba ”
“Eh Umma nima naga alama gaskiya anya Ummq matarsa tana masa girkj kuwa ”
“Eh nima abunda nake zargi anya matarnan tana kalawa dashi kuma ,gashi Shamsu da shegen zurfin ciki ko zan kasheshi da tambaya bazai taɓa faɗamun damuwar sa ba ”
“Hakane Umma wannan kan ai kunsani halin sane ”
“Hakane yanzu abunda zamuyi idan Allah ya kaimu gobe zakije gidan nasa kumana c i d ”
“Allah ya kqimu”
*********
Bayan sun gama kitso aunty amarya ta tashi zata tafi ta ce
Uwar ɗaki gashi ta ajiye mata omo da sabulai dan kozata mutu bazata karɓi kuɗiba ,murmushi tayi ta ce
“To nagode Aunty amarya ina miki tini akan hirarmu kizama jaruma kiyiwa mijinki abunda yakeso don wasu sun iya amma mazajensu basu da lokacinsu ”
“Haba aunty yanzu akwai namijin da bayason wannan abun ,aini na ɗauka duka mazan haka suke ”
“Himmm kowani na miji da halinsa amma Allah yasawa kowani namiji shaawa ,wani kawai zallar girman kai shiyasa bazai bari kufarantawa juna ba ”
“To Allah ya shirya mai girman kai ,girman kai kam sheɗan ma baisha ba ”
Ta dauki key ɗinta ta fita a gidan tana shiga ta samu mijinta yana zaune a falo tayi dariya ya kalleta ya ce
“Ha’a baby harkin dawo ”
“Eh na dawo mun gama kitson ”
“Haba harkun gama mugani ”
“Ah baby bazan nuna maka ba sai mun haɗu a bed”
Dariya yayi ya ce
“Allah baby na naga babyn tawa tafara kama hanya fa ”
“Eh mana ina tare dakai ai dole na kama hanya ”
“Ok kinsan abu ɗaya ne ya rage miki ”
“Me?”
“Ki kira me lalle ta miki ko baby na ”
“Ah girkin fa ”
Ah zanci sauran na rana jekiyi lalle abunki ya dauko dubu ɗaya ya mika mata ,kallonshi tayi ta ce
“Gaskiya saidai in koma gidan maman mubarak tamun kasan uwar ɗakin nawan komai ta iya ”
“To shikenan ba damuwa sai kin dawo ”
Ta karɓi kudin ta koma maman mubarak tana shara saboda kitson da sukayi ya baza musu gashi dagowa tayi ta kalleta ta ce
“Yadai amarya ”
“Himmmn kedai bari Uwar ɗaki kinsan me yaya ya ce ”
“Ah ah bansani ba ”
Kwashe yadda sukayi ta faɗa mata tayi dariya ta ce
“To shikenan ina da lallen asali ma kuwa da gam bari in dauko in manna miki yanzu zuwa kafun baban mubarak ya dawo ya kamq ”
“Ah uwar ɗaki yabada kuɗi fa ”
Kawo kudin kiga yadda zamuyi dashi ta karɓa sannan ta koma daki ta dauko kayan kalle da wayarta yayar maman lamiru ta kira ta ce yazo shida mubarak babu ɓata lokaci suka zo kallon lamiru tayi ta ce
“Zan aikeku bakin titi yanzu kuje ku dawo kaje kasayon kankana rabin kwallo,kwakwa,madara peak na ruwa ,dabino,ayaba, gyaɗa ɗanya, maza ku kawon yanzu ka rike hannunsa da kyau”
“To saimun dawo”
“Allah tsare ”
“Aunty me zakiyi da wannan kayan kuma ”
“Ke wani haɗin zan miki yau saikin rikita yayanki yasin ”
“Allah Uwar ɗakina ”
“Eh mana”
“Yauwa auntu baki gayamun taya yaya zai gane ina jin daɗiba ”
“Yauwa idan yanayi kina rirriƙe damtsen sa kina shafa gashin kansa a hankali har zuwa keyansa sannan kina dan dan shishita kaman wanda tasha yaji to wannan kenan mataki na farko ,sannan idb yayi ya gaji saiki tashi kema kihau saikiyi haka akeyin abun bari inbarki haka karkizo kiyi wani abun saiki fara bashi tsoro nafiso yaga komai ma kaman shi ya koya miki ”
“Shikenan aunty Allah yasa in iya masa kunyace dani kaman me ”
“Babu kunya tsakanin mata da miji”
“Ko aunty ”
“Eh ”
Suna cikin hirar saiga su mubarak sun dawo da ledodi a hannunsu ta karba dama ta gama manna mata lallen ta yanka musu nasu ta basu suka koma gidansu lamiru ,cup ta dauko ta zuba kankanan a ciki sannan ta dauko kanan fari a daki ta bubbuga guda uku ta zuba a ciki ta yanka kwakwa a ciki da dibino ta bubbuga gyaɗa saida taɗan fara ruwa ruwa sannan ta zuba da zuma da peak milk da dukka kayan haɗin ta tura aka sayo kankara sannan ta zuba mata ta ajiye mata ta ce
“To gashi maza ki shanye tas ”
Tun kafun ta gama magana sai dauka tana ta sha tana suɗe baki saida tasha ta koshi ta juyo ta ce
“Uwar ɗaki baki sha ba ”
Dariya tayi ta ce
“Ah ah kedai kisha.kawai nikam bazan sha ba ”
“Haba maman mubarak meyasa kikemun hakane dan Allah kisha ko kaɗan”
“Karba tayi tasha lidayi biyu ta mika mata ”
Tana rayawa a ranta nida banda miji meya kaini shan kaya. daɗinan idan bata manta ba rabonta da mijin yau wata uku .
Washe gari da misalin karfe 12;09 ta diro gidan yayanta tana knowking ɗin kofan buɗewa tayi tana miƙa daga gani yanzu ta tashi daga bacci murmushin dole tayi ganin shamsi dan ta tsani wannan yari yar kinibibice da ita kaman me kariso falon gidan tayi tana kallon falon yadda yayi kaca² ……..
To muje zuwa free page uku ne kudaure kubiya 150 babu yawa baifi karfin kowa ba
na kuke ku matso kusa
Yabon gwani ya zama dole
Ina ƴan kasuwa
Ina masu saida kayan kitchen
Ina masu bukatar logo,invitation card ,invitation vedio ,sticker,kai harda marubuta irina ga dama ta samu
Shahararre ,fasihi,kwararren ,professional desiger yaro matashi maiji da baiwa ,koda ka iya sai kanada baiwar yi ,baiwar daga ilahi take ,ku garzayo wajen


Name: | [Banzar Mace Hausa Novel Complete] |
---|---|
File Type: | Download Novels as .TXT .PDF .DOC (WPS) .HTML |
Uploaded By: | www.mynovels.com.ng |
Category: | Hausa Novels Documents |
Tags: | #Hausa Novels Documents #Hausa Novels Books Complete Hausa Novels #Hausa Novels #Hausa Novel #Romantic Hausa Novels #Sabbin littafan hausa |
Novel Price: | Free |
Last Modified: | October, 2022 |
Idan Kuna Bukatar Hausa Novels Audio Ku Shiga anan Kana ku danna Subscribe a tashar My Novels TV
Zaku iya sauke Manhajar Android ta My Novels anan Domin samun littafan Hausa maras adadi

Zaku iya shiga WhatsApp Group namu na My Novels anan domin samun Littafan Hausa Maras adadi

Domin samun littafai a saukake su shiga group namu na Telegram

Leave a Reply