*Page 1-5*
*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*
Atsaye take sai kai kawo take acikin daki takasa zama takasa tsayi saboda wani azababben ciwo datakeji amararta dakuma bayanta
Abu kamar wasa amma haryanzu ba wani sauki saina Allah
Kimanin karfe 2:30 na dare Allah yakawomata sauki inda ta santalo kyakkawar yarta kukan yar yadawo da ita dagacikin magagin azabar dakuma radadin ciwon da tasha ahankali ta mike tsaye tareda dakko rezo ta yanke cibi sannan ta mike tsaye tanufi bandaki
“jikinta kawai ta wanke sannan ta dawo dakin yarinyar ta dauka tanufi bandaki da ita
Wanka tamata tareda saka Mata kaya sannan ta tsabtace dakin, zama tayi tareda daukar yarta kwallah ke fita acikin idanuwanta kallon yarta take cikin tsananin so dakauna
Karfe 3:15 na dare tadauki yarinyar ta goyata sannan ta fita “wani kauye ta dosa hanyar kauyen kuwa daji ne ba mutane sosai, can gefen hanyar talabe sannan tasauke yarinyar ta ajiyeta agefen hanyar
Kwallah take zubar wa yayinda itama babyn ke ta tsala kuka ahaka ta juya ta wuce zuciyarta namata kuna
*KEBBI CITY*
Saukowar jirginsu kenan maisuna “azman Air” akatafaren filin jirginnan maisuna “ahmadu bello International Air port” daga kasar “Turkysh” kyawawan samari ne masu jini ajika dakagansu kasan akoshe suke kyawawane na gaske dayan yafi dayan tsayi *”ARYAN DA ANWAR”* kenan matasan samari tafiya suke cikin kasaita da salo irin na masu hannu da shuni sanye suke cikin shiga Mai kyau kuma ta alfarma shadda gizna wacca taji aiki ajikinta kalar light blue saikuma hula kalar baka dakuma takalma suma bakake agogon hannun suma hadadde Kai dakagansu dai kasan sun hadu tafiya suke suna nishadi da’alama firar namasu dadi
Wasu dankara – dankaran motoci nahango guda shida dakuma wasu mutane kusan su hudu da’alama bodyguards ne cankuma sainahango wasu maza su biyar biyu uku daga ciki samari ne biyun kuma da’alamu iyayensu ne
“ganin yayansu sun sakko yasasu karasawa kusa dasu cikin doki dakuma murnar ganin yayan nasu” cikin sauri Aryan da anwar suka karaso suka rungume iyayensu suna murna “welcome back my son’s cewar dadyn *ARYAN* kenan
Haka Ma dadyn Anwar shima sun gaggaisa kannensu sunmasu sannu da dawowa cikin farin ciki daganan kuma suka shiga motocinsu suka wuce izuwa gida
“`SHIN SUWAYE NE ARYAN DA ANWAR??“`
*ARYAN MUSADDIQ* bafulatani na asali haifaffen kasar kebbi kyakkawan saurayi mai jini ajika maiji da naira
“Aryan kyakkawa ne fari mai matsakaicin tsayi jikinsa daidai shi hancinsa dogo dakuma dara-daran idanuwa fuskarsa maidan tsayi ce gashin girarsa acike sumarkansa tamkar ta balaraben asali faffadan kirjine dashi kai atakaice dai kyakkawane na gaske”
Mahaifinsa barrister ne alhj musaddiq mahaifiyarsa kuma Doctor ce hjy hafsa itama bafulatana ce kasancewar auren gida akamasu Aryan su biyu kadai Allah yabama iyayensu shi dakuma kanensa Abdallah kasancewar ba’a kebbi mahaifinsu yake aiki ba shiyasa baanan suke da zama ba suna zamane a abuja city ”
“Kasar Turkey’s itace kasar da Aryan ya zabi yayi karatunsa na digiri acan yanzun ma Hutu sukayi shiyasa suka dawo gida”
Wannan kenan
Mahaifin Aryan dana anwar aminan juna ne wato Alhj mansur kenan, “shahararren dan kasuwa maiji da nera” karfin amintakarsu har tashafi iyalansu hakan yasa Allah yahada jinin Aryan da Anwar tin suna yara suna San junansu sosai atare sukayi primary school, a secondry ne suka rabu daga bisani kuma Allah yakara hadasu a Turkey’s inda Anwar ke karantar doctor shikuma Aryan yake digiri na biochemistry
“Anwar su hudu ne a gun iayayensu Fatima Anwar Ahmad saikuma jawahir mahaifiyarsu hjy Maimuna “
“`wannan kenan“`
“Tin a kofar gida sukadinga jin wani irin farinciki nashigarsu hon akayi alamar sun karaso cikin sauri gateman yazo ya bude aka shiga dasu wani abun mamaki dasuka gani shine duk gidan ancanza masa komai tindaga fentin gidan har komai bakarin dadi sukaji ba “
“Parking akayi na motocin duk suka fito domin shiga ciki cikin sauri bodyguards din suka dinga take masu baya har suka karasa ciki sannan suka dawo “
Ganin iyayensu mata da yan’uwansu azazzaune falo suncaba ado bakarami ba duk na taryansu ne hakan yakara sakasu cikin farin ciki,jawahir ce ta taso da gudunta ta rungume Aryan “oyoyo brother me welcome back ” shima cikin farinciki dakuma kewar yar kamwarsa yadagata sama suka karasa cikin falon
Sannu da dawowa su abdallah suka masu amma basu karba ba saida suka karasa gun hjyr su wato hajy maimuna suka duka har kasa suka kwashi gaisuwa tareda neman albarka kamar yanda suka saba “kawunansu ta shafa cikin murna da farin cikin ganin yaranta “
Su dady ne suka shigo nan aka baje falo aka kara gaisawa tareda yiwa su Aryan barka da dawowa mami ce tace su Aryan suje su watsa ruwa su huta sannan suzo aci dinner dasu
“Wanka sukayi suka canja kaya izuwa jallabiya baka da shotniker wando brown suka saka tirare mai masifar kamshi dayake samarin akwai san kamshi ga tsabata da iya kwalliya
Falo suka fito suka tararda mami da jawahir suna aikin jere danin da kala- kalan abinci dakuma kala- kalan kayan sha dana maku lashe,cikin fewminutes suka gama afara ci
“`wannan kenan“`
“Babyn sai tsala ihu take gaya hanyar ma ba alamun ko tsuntsu balle mutum cikin ikon Allah saiga wata mota hadaddiya ta tsaya wata mata naga ta fito zatayi fitsari daidai gun da babyn take,tsaye tayi chak jin kukan jinjiri awannan dajin da bako tsuntsu atsorace tadinga Jan baya………….
*Page 5-10*
*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*
Cikin sauri ta koma cikin mota tafadawa Wanda suke tare “daalama dai mijinta ne ” fitowa yayi sukaje gun da babyn take cikin tsoro dakuma sanda tamkar barayi
Idanuwansa naga ya rufe yana kiran “yesu almasihu” yana wasu maganganu wadanda Sam banfahimci me yake fada ba da’alama dai ba musulmi bane
Saida yakammala sannan suka bude idanuwansu sukaga yarinyar tayi shuuu harma tafara bacci
“Ahankali yakai hannunsa yadauketa sannan ya kalli matarsa yace mutum ce ba aljani ba”
“Itama kallonsa tayi cike da mamaki hannunta takai tashafa sumar ta sannan tace ” fasto I like her” idan baagane iyayenta ba zan dauketa tinda kaga ma bamutaba haihuwa ba “
“Murmushi kawai yayi batareda yace da ita komai ba yawuce tabi bayansa suka shiga motarsu suka wuce”
Dukkannin kauyukanda ke nan kusa ba inda mutanen nan basu jeba amma basu gane iyayentaba tin tana kukan yinwa hartadaina tayi bacci ruwa kawai matar kebata
Kwanansu biyu suna nema amma shuru hakan yasa suka yanke shawarar daukanta su reneta harzuwa lokacinda zasu gane iyayenta
“`AFTER 12 YEARS“`
*ABUJA CITY*
“Wani dankareren gida nahango ya hadu karshen haduwa”
Kyakkawar yarinya nahango yar kimanin shekaru 11-12 fara ce ba tass ba batada tsayi sosai fuskarta mai fadi ce inda take dauke da yalwataccin idanuwa dara² hancin ta mai tsayi sosai tamkar biro abun rubutun yan boko bakinta karamine sosai daidai na kissing jikinta bashida kiba sosai kuma ita ba ramammiya bace sanye take da wando iya gwuiwa baki da riga ja mai stones da hoton syndirela agabanta sumar kanta andaureta da ribom ja antufke karshen sannan aka sake jelar tasauka har gadon bayanta
“Babyn ta hadu iya haduwa cox zaka sakata sahun farko na kyawawa kwance take akan kujera tana kallo MBC 3 da’alama tanajin dasin kallon “
“Wata mata maga ta fito daga cikin wani daki sanye take da sket iya gwuiwa da riga kanta sanye yake da sumar attachment gun yarinyar naga tayo tazauna kusa da ita tareda shafa fuskarta “
“Dagowa babyn tayi ta kalli ta sannan tayi murmushi ta tashi tasake kwantawa kan cinyar matar tana cewa momy were is my dad nagaji inason naganshi nayi kewarsa over mom “
“Bata gama rufe bainta ba sukaji shigowar motarsa aikwa da gudun tsiya taje tana oyoyo my dady itadai momyn ta binta kawai da ido tana dariya da shaawar yar tata
” yana gama parking yafito cikin nishadi ta rungumeshi dagata sama yayi sai murna take nan itama momynta takaraso suka sumbaci juna tareda yi masa wclm”
“Ciki suka wuce yayi wanka ya chanja kaya sannan ya fito sukaci abinci bayan sun idar yafitar masu da tsaraba inda kusan rabin duk na jenifa baby ne aikwa nantaita murna”
Pastor David john miji ga grace bala uba ga Jenifer wacca suke kira da baby pastor ne Wanda akejidashi awannan kasar jenifa ita kadai suka Haifa hakan yasa suke tsananin sonta kuma suke nuna mata gata sosai a u.s take karatun ta na secondry yanzun ma Hutu sukeyi
“Jenifa tanada kokari sosai ga kyawo mutane dayawa suna cewa basu pastor ne iyayenta ba saisun tambaya suji bahaka bane tin zamanta u.s kawa daya kegareta wacca kusan sa’arta ce saboda kokarinta yasa har malamansu suke ji da ita “
“Pastor David dan asalin kasar kebbi state ne acikin garin zuru aiki ne yakaishi Abuja har yazama pastor “
“`wannan kenan“`
“Yau takasance Sunday don haka pastor suke shirin zuwa church amma banda baby wacca ita koma fitowa batayi ba balle ta shirya ganin haka yasa momynta zuwa dakinta domin ganin ko lfy mamaki ne yacikata jin kofar dakin a rufe “
“Dawowa tayi ta dauki keys taje ta bude kofar ta shiga koda ta shiga saita tararda ita tana bacci murmushi kawai tayi tafito daga dakin “
“Pastor ne yakalleta yace were is my baby”
“Kallonshi tayi tace bacci take I think gajiya ce mubarta har next week kaga zuwa lokacin ta warware”
“To shikenan dama harzance tahuta”
“Murmushi tayi ta dauki Jakarta suka fita”
Satin dadyn Janifer uku da dawowa aka fara yiwa Janifer shirin komawa school saboda hutunsu yakare gashi kuma kasar waje basuda AFRICAN TIME ranar da aka ce adawo ranar kowa zai dawo dole ko doka tahau kanka
“Har u.s iyayenta suka rakata amma dakyar aka rabata dasu lokacin da zasu dawo,kuka kuwa harda majina”
“Shigowarta kenan a hostel dinsu sai sharban majina take taji anrungumeta ta baya my friend tace kawai “
“Dariya ta dinga yi tana kallonta frnd wai yaushe zaki zama big girl any time idan zaki dawo saida kuka haba gsky kidaina kinfa girma “
“Kallonta kawai take batareda tace komai ba”
Karatunsu suke sosai shakuwa tsakanin jawahir da Janifer kuwa sai karuwa take kasancewar dakinsu daya gado ne kawai koda nashi ajinsu ma daya,jawahir ma kyakkawa ce kuma tanada ilimi sosai hakan yasa sukafi shakuwa da Janifer cox ita idan nakasa kokari toh bazata zauna dakai ba
“Sau tari idan jawahir na karatun Al- Qur’an Janifer kanyi shuru tana saurara to yau ma dai hakan ne”
“Kwance take kan gadonta dayake yau weekend ne wasa kawai suke”
“Jawahir kuwa ta idar da sallah tana kan sallaya tana karatun Qur’an “
“Shuru Janifer tayi har jawahir ta kammala sannan ta sakko kusa da ita ta kalleta sannan tace bestie na wai miye wannan kike karantawa yanada dadi sosai bani nima nakaranta takai hannu zata karba “
“Dasauri jawahir ta jaye Qur’an aa bestie miye kike yi haka wannan littafe fa da kika gani ba maitabasa sai musulmi Wanda yake sallah amma ke kings ba musulma bace don haka idan kina so nabaki kikaranta to saidai idan zaki musulunta “
“Tabe baki tayi toh nikam aa “
“To kinga kuwa bazanbaki littafenmu ba nikwa”
“`AFTER 3 YEARS“`
Su Janifer yanzu anshiga SS3 first term don haka yanzu karatu suke sosai
Wata rana ne Janifer na libratory jawahir tazo ta kirata……….
*page 10-15*
*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*
Wata rana ne Janifer library tana karatu jawahir tazo ta kirata koda suka fita saitaga Ashe yayan jawahir yazo shine takirata domin su gaisa
Aikwa dakyar ta iya tsayawa suka gaisa saboda ganin tsananin kyan shi “shikwa ko ajikinsa ” nan yafada masu gidansa saboda sunzo yin wani cose ne na tsawaon shekara biyu da rabi saboda
Aikwa nan jawahir taita murna danuwanta kusa da ita
“Itadai Janifer kallonsu kawai take cox gya din yatafi da tinaninta “
Sun dan jima Suna fira wacca daga jawahir Sai yayanta ne sukeyi amma Janifer kam ko um balle um um ahaka har yar suka rakashi ya wuce suka dawo ciki
Kwance take akan gadonta tinani take Wanda har tayi zurfi acikinsa harma takai ga natasan da mutum akusa da ita ba
Tabata tayi tace bestie sannan ta dawo daga duniyar tinaninda taje
Murmushi tayi sannan ta tashi zaune bestie yadai
Haba tinfa dazu nake kanki amma bakimasani ba meke damunki ne,
“Bakomai tabata ansa kaitsaye daga nan ma saita mike tshige toilet “
Binta kawai tai kallo sannan itama tamike tsaye ta fita
Wata ranar Saturday ne jawahir tace su shirya suje su gaida yayanta Aryan Janifer ko bata mata musu ba ta shirya cikin riga da wandon jeans baki da takalma hill farare Sai gashin kanta data tufke tasake jelar a gadon bayanta duk da bawata kawalliya tai ba amma tayi kyau sosai
Jawahir ma ta shirya cikin shiga mai kyau wandone baki da riga pink amma ta sakko mata har gwuiwarta Sai bakin mayafi datayi Rollin dashi shima baki ne sannan ta dora after dress akai itama dai ba laifi tayi kyau ainun
Atare suka fito Sai zuba kamshi suke har zasu fita Sai Janifer tace bestie bazamuje da hanifa ba
“Ba damuwa idan kina bukatar hakan “
Hostel dinsu suka je bata wani bata lokaci ba suka wuce
Amotar hanifa sukaje dayake itama mahaifinta mai arziki ne sosai hakan yasa ya siyamata mota idan tanaso ta fita saita shiga abarta
“Tafiya suke Suna shan sauti amotar dakagansu kasan sun hadu ainun “
Tinda suka karasa cikin Quarter’s din ake kallonsu saida suka shiga ciki sannan jawahir ta kirasa
Kwatance yamasu cikina saah kuwa Ashe hanifa tasan inda yake din
Suna karasowa shima saigashi acikin tasa dalleliyar Sai suka wuce
Gida ne daidai zaman mai mata daya kasancewar bashida aure yasa yake zama da abokinsa haidar
Falo suka shiga yakawo masu abun sha suka gaisa sannan jawahir ta gabatar mashi da su
“Brother ga friends dina Janifer and hanifa “
“Friends this is my brother Aryan “
OK nan suka kara gaidashi sun dan dade sosai daga bisani yarakasu har mota sannan suka wuce
“Bayan sun shiga mota ne hanifa Sai santin kyan Aryan take wai kamar balarabe yafi jawahir kyau “
Nan ta fada masu ba uwa daya uba daya suke ba
“Aikwa nan hanifa tace no wonder shiyasa yafiki kyau Ashe “
Duk fiardasuke Janifer bada itaba tana nan tana game da wayarta
“Hanifa ce ta tsakureta hey lady what’s rong with u Sai fira muke amma ke kinyi shuru kinga nifa wannan shegen miskilancin naki ya isheni “
“Kallonta kawai tayi tace to mekike so nace ne naga firarnan badani kukeyiba koh “
Jawahir dai rigimarsu dariya take bata any time idan sun hadu saisun yi rigima akan miskilancin Janifer
*********** ***********
Yau Janifer ta tashi ba lfy amma saboda tsananin miskilancin ta taki bari jawahir ta sani har suka shiga class Lessing
“Sai juyi take amma taki yin magana “
“Jawahir ta lura da ita amma ba halin ta kulata saboda teacher na class “
Sai kusan 10:00am sannan aka tashi breakfast dasauri jawahir tazo gunta tana tambayarta meke damunta
“Kai kawai take daga mata amma takasa magana “
Waya ta dauka ta kira nose’s na hospital din school,cikin few minute’s suka karaso aka dauketa
Koda aka dauketa saiga jini akan kujera inda take zaune 🙈dariya jawahir tai “tace hmm su Janifer angirma “
Injections suka mata sannan suka bata magani tasha daganan kuma suka nuna mata yanda zata dinga gyara jikinta har kunya tadinga ji daga bisani suka mata karin drip
“Bacci tayi sannan jawahir tazo ta dauke ta suka koma hostel saidai time by time tana karbar magani kuma tanazuwa adibi lfyr ta “
Wata rana ne Janifer sun fita shakatawa waje suna fira akan karatunsu Sai Janifer take tambayar jawahir
Bestie yanzu idan na musulunta zan iya son duk Wanda nakeso koda musulmi ne kuma zai iya aurena ??
Murmushi jawahir tai tace sosai ma kuwa musulmi namiji zai iya auren musulma mace haka itama zata iya auren Christan amma gsky akwai hadari sosai gwara dai shi ya auri cristan
Amma meyasa kika man tambaya ne
Bestie inasan na musulunta ne naga addininku yafi namu dadi kuma yafishi tsabta
Zanfi kowa farinciki wlh idan kika musulunta amma saidai bestie iyayenki zasu aminta da hakan kuwa ,kinfa San tsananin kiyayya dake tsakanin cristan da musulmi
“Iyayena suna sona sosai kuma nasan zasu so abunda nakeso “
Shikenan badamuwa idan munje Hutu saiki masu magana kiji kinga idan mumdawo sai kawai brother na yamusuluntar dake koh
Dariya sukayi suka tafa sundade suna fira sosai daga bisani suka koma school
**************************
Karatu suke sosai kasancewar exam ta gabato saboda haka bazama ba tsayi sai karatu
Jawahir da yayan ta Aryan saidai shi Waya wani lokacin ma har Janifer tana bawa su gaisa amma daga gaisuwa shikenan
Abubuwa sun dami Janifer sai ramewa take ga yawan tinani amma taki ta Samar da jawahir kodama ta kula da hakan ta tambayeta saitace mata ba komai karatu ne kawai hakan yasa dole ta kyaleta saboda tasan halin kawar ta
Abu kamar wasa kuma sai karuwa yake……………………
*page 15-20*
*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*
Abu kamar wasa amma sai karuwa yake
Yauma dai kamar kullum Janifer ce zaune akan kujera cikin class dinau notebook ahannunta amma Sam hankalinta baya kansa
Tayi nisa sosai cikin tinani haryakai ga batasan ma akwai mutum akusa da ita ba
“Hannunta takai ta dafa ta sannan ta dawo cikin hayyacinta “
Zama tai akusa da ita sannan ta dafa kafadarta
Bestie ahalin yanzu a makarantar nan bakida wacca tafini tin muna yara muke tare har izuwa yanzu da muka mallaki hankalin kanmu
Bantaba zaton akwai wani Abu dazan samu arayu na boyemaki farin ciki ko bakinciki
Amma ke saigashi kina boyeman damuwarki,wlh koki fadaman ko karki fadaman kinada damuwa
Miyasa kike boys man damuwarki nifa tamkar yar’uwarki ce
“Numfashi taja sannan ta gyara zama tana fuskantar jawahir “
“Kallonta tai sannan tace kawata tabbas inada damuwa amma inaga kamar fadar damuwar bazai taimaka man da komai ba kiyi hakuri idan lokacin na fada maki yai zakiji “
But yanzu gsky bazan iya ba kiyi hakuri kawata nasan kina damuwa sosai da damuwata kuma nagode sosai
“Hmm bakomai tinda kince haka Allah ya kaimu lokacin “
Sun jima sosai suna karatu har kusan 12:15am sannan suka wuce hostel saboda jawahir tafara jin bacci sabanin Janifer wacca tini bacci yakauracewa idanunta
******** ******* *******
Su Janifer sun fara exam ta second term saboda haka yanzu ba lokacin Hutu koda yaushe suna wajen karatu
Yau takasan ce Sunday don haka su Janifer basa exam hakan yasa suka shirya fita domin sud’an sha iska
Sun shirya sunyi matukar kyau ‘duk da sun danyi rama saboda karatu “amma baihana suka sha kyau ba
musamman tauraruwar Janifer duk da bawani make-up taiba amma duk namijin da ya ganta tabbas saiya k’yasa
Tafiya suke suna firarsu cike da nishadi da’alamu firar na masu dadi hakan yasa ma Sam basu kula da mutanen da ke gabansu ba
Saiji tai anriko hannunta ta baya juyowar dazatai kawai saitaga wasu mutane suka gani fuskarsu a rufe sunkai su biyar
Atsorace suka fara ja dabaya sukuwa saiyowa cikinsu sukai kan Janifer sukai d’aya daga cikin su ne ya cafko gashin kanta Wanda saboda masifar zafinda taji Saida tai wata kara wacca tadaga hankalin jawahir
Da sauri tazo zata taimaketa sai suka rik’e ta” magiya ta dinga masu “don Allah karku cutar da ita metamaku ne don Allah kuyi hakuri na rok’eku “
” ke kimana shuru ba ita tamana laifi ba mahaifinta ne,shi fasto Wanda yafiye san kansa sam baruwansa da damuwar wani duk da yasan addininmu yahana yin hakan hakan yasa muka yanke shawar kashe wannan yar tasa saboda yafi Santa fiye da komai nasa cewar wanda ya rik’e jawahir”
D’ayan Wanda yarike Janifer shine yadaka mata wani karfe a kanta hakan yabawa jini damar ballewa tamkar famfo
Wata kara jawahir ta buga ta fizge hannunta tai kan Janifer wacca tini ta fadi wanwar a some ba rai,kuka jawahir ta dinga zabgawa tamkar ranta zaifita
“Sukuwa mugwayen sai dariya suketa kyakyatawa “
Hakan yabawa jawahir damar daukan bindigar da suka ajiye, dakarfi ta mike tsaye tareda nuna masu bimdigar idan baku bar nanba zanharbeku
“Ja da baya suke dinga yi da d’add’a ya suka gudu “
Saida ta tabbatar da duk sungudu sannan tai saurin d’aukan wayarta duk ta rude hannayen ta sai makyarkya ta suke tama rasa wa zata kira
Number hanifa ta kira har kira uku amma bata daga ba nan take wata dabarar ta fad’o mata wata nmr tasake kira cikin k’ank’anin lokaci aka daga
Yaya don Allah kazo ka taimakemu kaceci rayuwar k’awata, tana cikin wani hali zata iya rasa rayuwar ta
“Jin muryar kanwarsa abar kaunarsa cikin wani hali yasa hankalinsa yai mugun tashi da sauri yace meya sameku little meke faruwa ne kuna inane “
Yayanah muna a “madsham road ” kusa da babban ginin nan church OK OK ganinan zuwa kujirani kinji ……………………
*Page 20-25*
*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*
Cikin sauri jikinsa har rawa yake yadauki keys din motarsa yafita
Cikin k’ank’anen lokaci yakaraso ganin taron jama’ah agun yasa hankalinsa tashi dasauri yay parking yafito
Harda gudunsa yakutsa tsakanin mutanen jawahir ya hango zaune akasa tana rungume da Janifer sai rera kuka take
Ganin yayanta Aryan yasa tazo da gudu ta rungumesa brother me ka taimaketa wlh zata iya rasa ranta “janyota yay tareda kissing din goshinta ki daina kuka aigani nazo bazata mutu ba kinji “
Hannunsa taja izuwa gunda Janifer ke a kwance tamkar gawa don ko motsi batayi
“Kallonta yay yamarasa ta ina zaifara baiyi wata – wata ba kawai yadauki Janifer tamkar wata smoll baby “
Aransa kuwa sai mamakin rashin nauyin Janifer yake a fuska idan ka ganta zakace masifar nauyi ne da ita ashe bahaka bane
Dasauri jawahir ta bude masa murfin mota na baya yasaka Janifer itama ta shiga tariketa
Nan shima yabude driving site yashiga yatada motar suka bar gun
********** *********
Makarantar su yawuce cox kasar waje sunada tsauraran dokoki bakamar nan ne ba Nigeria
Hospital din makarantar aka wuce da ita nantake aka shiga da ita domin bata taimakon gaggawa
“Kwallah sun kasa tsayawa a idanun jawahir gani take kamar Janifer bazata rayuba sannan tana taisayawa iyayenta ganin irin tsantsar so dasuke nuna mata dakuma tausayin halinda Janifer take ciki wadannan abunuwan suke ta kai kawo akwakwalwar jawahir kuma suke hana kwallah tsayawa daga idanuwanta “
Tin kusan 11:20am ake Abu daya likita uku akan Janifer kowanne yana nashi kokari don ganin sun ceto rayuwarta amma abun yaci tira likitoci sai kai kawo suke acikin dakin
Ganin hakan yasa jawahir ta dauki wayar Janifer ta mikawa Aryan
Kallonta yay saboda baifahimci me take nufi ba
Yaya don Allah ka kira iyayen Janifer kasanar dasu halinda take ciki
“Bai musa mata ba yakarba yay dialing nmbr da yaga ansaka wa my dady “
Cikin few minutes aka daga bayan sun gaisa ne yasanarda shi duk abunda yake faruwa yakuma shaida masa dacewa ayanzu haka tana tiater room
“Baikarasa jin abunda yake fada ba wayar ta kubuce masa sai kasa saboda tsananin tashin hankalinda yashiga “
“Aikwa nan take yanada umarni da’amasu biza zuwa u.s shida momyn Janifer lokacinda yasanar da ita harda suma Saida tai ta tsorata sosai sai kuka take wai kodai ta mutu ne aka cemasu tana nan “
Shidai yakasa cemata komai sai rarrashinta dayake
***************
Abangarensu jawahir kuwa tinda Aryan yaji ankatse wayar yasan akwai matsala amma baifadawa jawahir ba
Kimanin 2:00pm aka kammala yiwa Janifer aiki don haka sai suka fito da ita zuwa dakin hutu
Nan su jawahir suka bi bayansu Saida aka kammala komai sannan suka fito jawahir sai murna take kawarta bata mutu ba
Aryan ganin komai yayi normal yasa yawuce zuwa wajen sallah jawahir ma hostel tawuce domin tayi sallah hanifa ce zaune a dakin tana kula da duk wani motsi nata
“Dadyn Janifer da momynta sun karaso u.s sai hanzari suke sun kagu suga yarsu “
Direct school din suka yo komasaukinsu ma sakawa sukayi anema masu amma sukam saisunga halinda yarsu tilo take aciki
Dawowar Aryan kenan daga sallah sukayi kicibis da dadyn Janifer nan suka gaisa sannan suka shiga atare,ganin halinda yarsu take ciki yasa pastor hanawa momynta shiga saboda yasan idan ma tashiga koke – koke kawai zata dinga yiwa mutane gashi kuma doctor yace tana bukatar tahuta
Nan dai suka zauna jiran farfadowarta har kusan 5:15pm amma bata farfado ba ganin haka yasa Aryan wucewa hargobe kuma idan Allah ya kaimu
8:00pm Janifer ta farfado cikin sa’a cox duk wani Abu da doctor’s suka zata baifaruba kamar loosing memory wai saboda jinin yashiga har cikin kanta buguwar ta kusa ta taba kwakwalwarta
Nikwa nace bata dai taba ba koh to ai dasauki
Komai yatafi normal yanda ake bukata jawahir sai murna take “amma Saida Janifer ta tambayeta ya akayi suka barsu ai ita ta dauka kashesu zasuyi ” nan jawahir tabata labarin duk yanda akayi har izuwa kawosu nan da Aryan yayi
“Wani sassanyar murmushi tayi jin sunan Aryan kuma ma shine da kansa yakawota asibiti ”
********* ********
Yau kimanin kwana uku kenan Janifer ta samu sauki sosai kula kuwa tanasamunta sosai har agun Aryan ma hakan kuwa yana mata dadi bakadan ba wani lokacin abun har mamaki yake bata idan yaje yayo mata siyayya mai tarin yawa har takan rasa bakin yimasa godiya sai iyayenta ne zasuta godiya
Shikwa acewarsa saboda kanwarsa yar lelensa yake mata hakan wato jawahir cox yafahimci sun shaku sosai
“Exam dinsu kuwa saidai akawomata Questions tayi answering anan haka aka dinga mata har suka kammala “
Janifer ansamu lfy ganin haka yasa aka sallamesu nan dadyn ta yashirya masu domin su koma gida tinda sunyi hutu
Ranar da zasu wuce kuwa harda Aryan wajenyin rakiya Wanda jawahir ce tasaka shi yin haka cox itama wani lokacin idan sunyi su Aryan Anwar sukazo daukanta takan rakasu har airport toh itama shiyasa tace suje su rakasu
Bayan sun wuce da 3days suma suka wuce dayake shima yanaso yaje gida din
******************
1month kenan da dawowar Janifer gida ta warke sosai tasami lfy amma sai dai fa ta dakko wata chakawakiya
Wacca tafi karfina wollah
Har yanzu Janifer bata zuwa church kullum idan lokacin zuwa yay saitasami karyar da tai wacca zata hanata zuwa
To yauma dai kamar kullum
“Dadyn ta na a falonsa yana karantar jarida tashigo ta gaidashi cikin fara’ah yakarba “
“Baby yadai me kike sone ko fira kawai kikazo muyi “
Murmushi tai Wanda yake kara mata yake bayyanar da fararen hakoranta yake bayyanar da kyakkawar fuskarta mai dauke da beutypoint Wanda ko murmushi tai saiya bayyana
No dad Questions ne dani shine Nazo natambayeka
“OK site dawn “
Zama tai tana fuskantarsa sannan tafara……………
Wayyo nidai guduwa zanyi bazan tsayaba wollah
*Page 25-30*
*BISMILLAHR RAHMANIR RAHIM*
Zama tai tana fuskantarsa sannan tafara da cewa dad plss idan kasan amsar da zan tambayeka kafada man
“Murmushi yay baby karki damu fadi inajinki “
“OK “
Dad miye AL-QUR’AN ??
Dad miye addinin musulunci ??
Dad what is the difference between Muslim and Christianity ??
“Tamkar saukar aradu haka yaji wadannan tambayoyin nan take zufa yadinga keto masa ta ko’ina glass dinda yake sanye dashi ya cire sannan ya kalle ta “
Janifer ina kikaji wadannan abubuwan sannan ya’akayi kika sansu
Batace dashi komai ba saima shuru data masa
Janifer let me tell u something baidace adinga jin wadannan abubuwan daga bakinki ba karfa kimanta ke yace agareni ni pastor ne Wanda duk fadin Nigeria bawanda baisanni ba kinga kwa Sam baidace wadannan abubuwan adinga jinsu a bakinki ba
Sannan as from today as from to now kada inkara jin wadannan sunaye a bakinki kinji ni kohh yafada da karfi harsaida ta firgita
Eh..eh..dad naji kuma zan kiyaye
Nan ta tashi tawuce dakinta
“Mamakine fall afuskarsa tambayoyi yake jerawa kansa wadanda yakasa samun amsarsu “
Shin ina Janifer takejin wadannan abubuwan itada dake a makaranta kuma akasarda ba musulmi sosai to wayake fada mata shin suwaye kawayenta dawa take zaune a school tambayoyi dai kamar haka yake yiwa kansa wadanda yakasa samun amsarsu
Hmmm yanisa lallai tabbas dole nadauki tsattsauran mataki akan yarinyar nan
******** ******** *********
Hutunsu Janifer yakare don haka aka mata shirin komawa school zangon karshe na kammala secondry school wato ss3
Yau takasance Thursday kuma yaune Janifer zata wuce school saidai wani abunda yake bata mamaki shine a dik sanda zata koma makaranta sai iyayenta sun mata rakiya har can u.s amma sabanin wannan karon
Data yiwa dadyn ta magana sai yace aiki yamasu yawa a office sai daga baya zasu zo idan zasuyi graduation Sam bata ji dadiba amma bayanda ta iya haka ta tattara ta wuce school
Wannan karon kam ta riga jawahir dawowa dan haka ba’amata mitar kukanda takeyi ba idan zata dawo school
Kwanan Janifer biyu da dawowa jawahir ma ta dawo nan aka fara karatu ba wasa saidai har yanzu janifer nada damuwa amma kuma har yanzu taki ta fadawa jawahir damuwarta hakan yasa itama tai banza da ita
Yau kam sunyi baki a hostel dinsu kawayensu ne aikwa nan aka baje anata shan fira amma banda miskila Janifer ita kam littafe ta bude wai dan ace karatu take Wanda daka kula da ita sosai kasan hankalinta sam baya kan littafen
Sai kusan 8:30pm sannan kowa ya koma hostel dinsa
*****************
Ahalin yanzu su Janifer basuda wani ishasshen lokaci karatu suke tukuru ganin sun kusa fara exam dinsu ta karshe saidai Janifer batasan su rabu da jawahir cox sun saba tin ana yarinta harizuwa yanzu da kowa yamallaki hankalin kansa
“Kwance take akasa tarasa meke mata dadi arayuwa Abu daya take tinawa taji dadi tamkar yana akusa da ita amma saidai tana ganin kamar yamata nisa sam ba ajinta bane “
Tana cikin wannan tinanin ne jawahir tashigo ta katsemata shi da cewa Janifer zo Ku gaisa ga yayanmu yazo Aryan
“Wani nishadantaccen murmushi tayi Wanda har Saida hakoranta na gaba suka bayyana “
Nan ta tashi ta canza kaya ta tufke sumarta tadan gyara fuskarta dik da bawani make-up tai ba amma nayi kyau sosai takalma tasaka hill colour din rigarda ke jikinta sannan ta fito
Tafiya take ahankali tamkar mai tausayin kasa harta karaso gunsu cikin ladabi da tsantsar tarbiyya wacca yayi mamakin a ina tasameta ta gaidashi
“Cikin fara’a da sakin fuska ya karba mata tareda tambayar lafiyar jikinta “
Sun dan jima suna fira wacca daga jawahir sai Aryan keyinta daga bisani suka rabu
Yau takasance Saturday weekend ne basu shiga class sai Hutu
Zaune take akusa da jawahir sanye take da wata kyakkawar rigar shan iska iya gwuiwarta Sumarta ta tufke ta gu daya ta sake jelar ta sakko mata har gadon bayanta
Kallon jawahir tai tace bestie inaso muyi wata magana dake amma saikin zauna ba’atsayeba
“Murmushi tai sannan ta zauna kusa da ita inajinki yar’uwata”
Kawata nagama yanke shawara zan musulinta nadade da wannan zancen araina amma sai yanzu nagama shawara inasan nima nazama musulma hala nawa ne ake biya idan za’ashiga
Murmushi jawahir tai sannan tace to Alhmdllh ayau nafi kowa farinciki idan haka ta faru amma kawata iyayenki sun sanda hakan kuwa
Hmmm kawata koda sunsani koma basu saniba nariga dana yanke hukunci, tinda nake bantaba jin karatu mai dadi da zak’i kamar QUR’AN ba sannan tinda nake bantaba ganin addini mai dadi kamar musilinci ba hakan yasa nagama yanke shawarar shiga mulinci koda shine silar barina duniya
Hmmm jawahir ta nisa shikenan kawata insha Allah ma bazaizama sanadin barinki duniya ba
Musulinci idan za’ashigesa ba’a bada ko sisi
Gobe mu shirya muje wajen brother saiki karbi musulinci
“Aa meyasa ke bazaki bani ba nakarba ahannunki “
Murmushi tai no bestie inasan ne ki karba gaban mutane saboda suzama shaidar karbar musulincinki
“OK badamuwa sai gobe din “
Wlh yau kawata farimciki nakeji sosai ubangiji yatabbatar damu akan musulinci ameen suka karba su duka
Nima sainace ameen yh rabbil izzati wal kuwwa
*Page 30-35*
*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*
Tin 10:00am suka shirya tsab saidai jawahir tsoron fitarsu su kadai take tin lokacin da abunnan da’akayiwa Janifer yafaru suka daina fita sukadai
Wayarta ta dakko takira nmbr hanifa cikin sa’a kuwa tadaga nan tace dan Allah idan bakomai take ba tazo hostel dinsu tasameta
“OK ganinan zuwa “
Zaune suka suna jiran zuwan hanifa nan take kuwa saigata
Da zuwanta jawahir tamata bayanin komai
“Murna hanifa tadinga yi tamkar wacca akayiwa albishir da aljannah wlh naji dadi kuma nayi farinciki sosai ubangiji yatabbatar damu akan addinin musilinci “
Ameeeeen suka karba su duka
Dama tsakanin hanifa da Janifer akwai soyayya miskilancin Janifer ne kawai kesa sunayin fada cox hanifa batasan sa
Atare suka jero suka fito saifaman kallomsu ake tindaga kan malamai har students cox sun matukar haduwa dikda lady’s din basasan yin make-up amma sunmatukar haduwa musamman tauraruwar wato “Janifer ” tafiya suke cikin nutsuwa dakuma tsare maidaukan hankalin maikallah
Fitowa sukai awajen school din saboda motar tana daga waje can a gefensu wasu samarine sai faman kallonsu suke suna maganarsu
Daya daga cikinsu ne yake cewa wlh nidai yarinyar can tana birgeni ya nuna Janifer komai nata a nutse tafiyarta tamkar mai tausayin kasa ga diri ga kyau kai komai nata yayi wlh amma saidai kash ba musulma bace
Daya daga cikinsu sai yace kai wlh rufawa kanka asiri mugun yan rainin wayo ne ko kallon namiji nasayi wulakancin kwarai zasu maka kuma ba ruwana wlh nikaga tafiyana ya wuce abunsa
“Tafiya suke har suka isa gun motar suka shiga ta tada suka wuce “
Cikin kankanin lokaci suka isa gidan Aryan sannan sukayi parking suka shiga cikin gidan tareda yin sallama
Yana daga kitchen ya karba sannan yafito ganin little sis dinshi yasa yasaki wani kayataccen murmushi sannan yakaraso suka gaidashi sannan yazauna
Nan take jawahir tasanardashi abunda yake tafe dasu shima kam yayi matukar farin ciki ba kadan ba cox tinsanda yaga yarinyar yadinga mata fatan shiriya Ashe kwa darabon haka agareta
“To alhmdllh Janifer yakira sunanta “
Abazata taji kiran sunanta da yay saitaji kamar ma yafi kowa iya fadar sunan
Ahankali ta dago ta kalle sa Ashe idanuwansa nakanta dagowarda tai saisuka hada ido dasauri ta dauke nata sannan ta karba da na’am
Inafatar bawanda yamaki dole ke kikaji kuma kikagani cewar kinasan kishiga dakanki
“Eh ta karba masa “
To masha Allah inasan kusan cewa musulinci ba’a biyan ko sisi idan za’ashigesa wasu kalmomi ne kawai za’afadamaki saiki maimaita da kanki
“OK “
Idan nafada ki maimaita kinji koh
“Tam tace “
Nan take yafada mata kalimatushhsahada sannan ta maimaita har karshe
Nan suka jawahir suka dauki kabbara alhmdllh yau kintashi daga kawata kinzama yar’uwata a muslinci cewar jawahir data fada tana dariya
“Itama murmushi tai harsaida hakoranta na gaba suka bayyana “
Janifer zan fada maki ma’anar abunda kika fada cewar Aryan kenan
Kin fada cewar tabbas kinshaida kin tabbatar babu abun bautawa da gaskiya sai Allah sannan kikace annabi Muhammad [s.a.w] manzon Allah shin
Kisani cewar Allah shine mahalicci komai bashida da bashida mata kuma bashida iyaye,sannan kisani cewar babu addini mai dadi kamar musilinci babu wani addinin da yabawa mata yamci kamar musilinci
A’da mata abun gado ne
A’da mata ba’abasu ilimi saidai a ajiyesu acikin gida domin aiki kawai
A’da mata binne su akeyi da ransu saboda taoron talauci da fatara
A’da sai anyi zina da mace har tasami ciki sannan ake daura mata aure
A’da giya da chacha da zina sune abun nishadi
“Amma daga zuwan musilinci dik ya kawarda wadannan yaharamta su sannan yace ayi hukunci ga duk Wanda ya aikata su “
Yar’uwa a musilinci ina tayaki farincikin shigowa addini mai tsabta kuma ina maka fatan alkhairi ubangiji ya tabbatar damu a kan gsky
“Ameen suka karba baki dai “
Alhmdllh Janifer ki zabi suna na musilimci Wanda kike so asaka maki kuma acigaba da kiranki dashi har a gobe k’iyama
“Murmushi tai sannan tace brother ka zaba man kawai ni bansan wanne zanzaba ba “
Shima murmushin yamaida mata shikenan nazaba maki sunan kanwata wacca tarasu *ALEEYAH*
Woww brother me suna maidadi bestie na daga yanzu sunanki yatashi daga *Janifer* zuwa *ALEEYAH* cikin farinciki suka rungume juna harda yar kwallar ta jawahir itadai hanifa kallonsu take tana dariya
“To Alhmdllh yanzu little sis aiki yana kanku hakki ne akanku Ku koyamata ibada cox kune yan’uwanta na kusa”
“Insha Allah yayana “
Sun dan jima yana masu yan masihohi daga bisani suka wuce school
********* ********
Tin da suka dawo jawahir da hanifa suka zage dantse wajen koyawa *Aleeyah* addini tindaga wankan tsarki koyon alwala farillolin alwala mustahabbai dakuma sunnoni sallah da rukunanta
Idan wannan ya koyamata wannan sai wannan sancan ya koyamata wannan haka sukeyi har kwata’iya abubuwa dayawa kasancewar *Aleeyah* akwai basira nan take takehaddace abubuwanda suke koya mata
Wani lokacin saisuga tamkar bata fahimta saboda *Aleeyah* akwai miskilanci amma kuma abun mamaki dasun yimata tambaya nan take takebasu amsa abun har mamaki yake basu
Cikin kankane lokaci *Aleeyah* taiya abubuwa dayawa kamar wankan tsarki da alwala saikuma sallah
Aryan yanemawa *Aleeyah* wata makaranta wacca wani ustaz hanafi ya buda saboda sababbin shiga musilinci dakuma wadanda basuda karatu sosai
Tuni tafara zuwa dayake week–end kawai ake zuwa kuma akwai cigaba sosai saboda ahalin yanzu hizif 5 ne cif akan *Aleeyah* abun gwanin ban sha’awa musamman idan tana rero QUR’AN daga bakinta gefen fikhu kuwa shima dai Alhmdllh
Wata ranar juma’ah ne Aryan ya kaisu kasuwa suka zabo tufafe kala – kala musamman tauraruwar wacca tasha kaya kala-kal cox tafiyar kacokam tatace aikwa tai masa godiya sosai harsaida tabashi mamaki
Bayan sun dawo ne suna zaune suna hutawa *Aleeyah* ta dubi jawahir tace
Bestie nah burina na farko ya cika saura d’ayan amma saidai d’ayan shine mai wahala dan Allah kitayani addu’ah
“Hmm insha Allah zan tayaki k’awata Allah ya cika mana burinmu na alkhairi ameen suka karb’a “
*****************
Yau kimanin 2months kenan da musluntar *Aleeyah* suka fara shirin exam
Karatu suke sosai bawasa saboda wannan itace ta k’arshe dan haka babu wasa
Saidai karatunda take zuwa wato islamiyya ya tsaya saboda karatu …………………………
*℘ąɠɛ 40-45*
*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*
A yau farincikin da su jawahir ke ciki baya misaltuwa firasukayi har kusan 10:30pm na dare sannan suka wuce hostel dinsu sukayi shirin bacci
Yau takasance Sunday dan haka tindawuri suka tashi cox gyare gyaren school din akeyi domin shirin bikin wanka sukayi suka canja kaya sannan suka wuce hostel dinsu hanifa suma shiryawa sukai nan suka fita yawo acikin motar hanifa amma fa yau kam *Aleeyah* ce driving aikwa abun yabasu mamaki wai dama Ashe ta iya driving tsabar miskilancinta yasa suka kasa ganewa
“Itadai dariya kawai take masu “
Sunsha yawo ba kadan ba sunzaga u.s dan tinda suke basu taba yawo kamar na yau ba
Bayan sungama yawo ne sunzo wani gu zasu huta suci abinci nan suka hadu da wasu samari su hudu wai sansu suke dayan yace shifa bashida wacca yakeso sai *Aleeyah* wacca ko kallon banza baima ishetaba aikin gabanta tacigaba da yi
Jawahir ce tace yar’uwa dan Allah ki kulasa mana wulakanci fa ba dadi
“Hmm lallai jawahir kamar bakisan halin *Aleeyah* ba kike mata wannan magiyar cewar hanifa “
Ai naga wulakanci ne ba dadi shiyasa
Itada cin abincinta take koma kulasu batayiba balle har tabasu ansa,harta kammala cin abincinta sannan tace “yar’uwata sanin kankine ni samari basa gabana inada Wanda nakeso so banga dalilinda zaisa nakula wadannan kananun yaran ba “
Kallon mamaki suka mata akwai Wanda kike so atare suka hada baki wajen fada hanifa tace yanzu awannan miskilancin naki zai bari kiso namiji hmm mundai ji amma badan munyardaba
“Kawa barta ma munyarda din toh Waye shi ya sunansa dan wace kasa ne Waye mahaifinsa “
Murmushi tai tace dukanku wlh kumsansa amma saidai bakusan shi bane kuma ahalin yanzu bazaku saniba sai nan zuwa gaba
“Zuwa gaba kuma muda zamu rabu yaushe ma zamuyi tinanin haduwa balle musan wannan labari zance kawai kike dama bakyason musani bakidaukemu yan’uwanki ba wlh cewar hanifa “
No bahaka bane wlh insha Allah ma zamu hadu har mucigaba da zumuncinmu kuma har kusan masoyina
“To Allah yasa cewar jawahir “
Suka amsa da ameen
Bayan sunci sunsha sannan suka wuce domin komawa school,suna cikin tafiya wayar jawahir tai ring koda ta duba Aryan ne nan ta daga
Hello yayana
“Na am little sis kuzo gasu Abba sunzo harda Ahmad amma Anwar baizoba aiki yamasu yawa a office “
Ayya to gamunan zuwa toh saikunzo
Kallon su tai tace su dady na da momy na sunzo muwuce can kawai OK
Tuki take cikin jin dadi cox u.s ba cinkoson ababen hawa kamar gida Nigeria har suka karaso sannan tai parking suka fito
Atare suka shiga jawahir sai zumudi take na ganin iyayenta aikwa da gudunta taje tarungume mami my mami I miss u
Dariya take tace I miss u my autana ya alhji dan Allah duba yanda karatu yamaida man ya dik ta rame sosai Abba dariya yai yace nagani saima tafi kyau ahaka
OK hakama zakace kenan
Saida ta gama sangarta sannan ta tina da su *Aleeyah* dariya tai tace mami ga kawayena nan wannan *Aleeyah* wannan kuma hanifa
Gaidata sukayi cikin girmamawa itama ta karba cikin fara’a
Nan suka baje akaita shan fira misalin karfe 5:15pm su *Aleeyah* sun gama sallar la’asar bacci sukayi shiyasa suka makara tana kwance wayarta tai kara takai hannunta ta dauko tana dubawa wazata gani my daddy dasauri ta tashi
A’uzubillah tafada afili Wanda harsaida su jawahir sukaji menene yan’uwa dady na ne yakirani kila ma wlh sunzo to daga mana ahankali ta daga tareda yin bismillah
“Hello my dear dother “
“Yes my dad “
Gamu munkaraso u.s dimm taji gabanta ya fadi yanzu haka ma juna masaukinmu
“Ook.. dad ganinan zuwa “
To saikinzo nan ta kashe wayar suka kalli juna yanzu yazamuyi kenan
Hanifa ta kalleta karki damu yanzu kutashi muje mugaidasu saikice masu makaranta tahanamu kwana a wani waje inba school ba kinga shikenan koh
Woww gsky kawa kina kawo wuta wannan shawarar tayi wlh cewar jawahir kutashi mutafi
Nan suka shirya suka wuce a wani hotel ne suke, dasuka k’arasa sai takira dadyn ta yafito yana ware mata hannayensa ma’ana taje garesa ahankali ta karasa tashige cikin hannayensa azahirin gsky tayi missing din iyayenta amma saboda kasancewarsu ba musulmi ba yasa take jin ma kamar batayi missing nasu ba
Nan su jawahir suka gaidashi ya karba cikin daurewar fuska cox ba’ahaka yaso yaga k’awayen yarsa ba nan yamasu jagora suka shiga ciki da gudu taje gun momynta tafada jikinta mommy na I really miss u itama cikin dariya tace me too my baby tin dazu mukazo amma bangankiba ina kikaje ne
Munfita ne nida friend’s na
But baby yanaganki da wadannan kayan ajikinki dik ina kudi da kayanda nake turo maki dasu zakisaka irin wadannan kayan
No mom dik suna nan kawai dai inasonsune kuma su friends dina suka sama that’s way nima nasaka
Shikenan amma dai kidinga saka naki
OK mom this is my friend’s jawahir and hanifa
Nan suka gaidata ta karba fuskarta ba’asake ba nan dadyn ta yashigo Sundan jima sannan sukace wucewa zasuyi nan dadynta yace ita ai anan zata kwanan dakyar tasamu suka kyaleta suka wuce school
“Hmm tab kawa lallai akwai Jan aiki agabanki wlh cewar hanifa “
Wlh kuwa Allah dai yasa kifi karfinsu Ameeen suka karba daganan school suka wuce kowa yay gaban kansa
******** *******
Yau Monday yauce ranar bikin su *Aleeyah* school din tasha ado tamkar wani wajen biki
Tin 8:00am Aryan hazo ya dauki su *Aleeyah* zuwa wajen make-up da saloon da kuma lalle kasancewar ba yanzu za’afara biking ba
12:30pm aka kammala masu komai dayake ba mutum daya bane ke gyaran hakan yasa aka kammala masu da wuri …….
*℘ąɠɛ 35-40*
*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*
Karatu suke sosai bawasa saboda wannan itace exam ta k’arshe dan haka babu wasa
Saidai karatunda take zuwa wato islamiyya ya tsaya saboda karutun exam
********** *********
K’wanci tashi ba wuya awurin ubangiji yau saura kwana biyu su *Aleeyah* sufara exam
Zaune suke suna cin abinci saishan fira suke akan exam dinda zasu fara jawahir ce ta kalli *Aleeyah* bestie lfy dai naganki so silent
Murmushi tai bestie banajin dadi ne wlh
“Meke damunki ne “
Marana ke ciwo tin jiya da dare nake jinsa nadauka zai daina shiyasa amma gashi har yanzu baidaina
“To aikwa bamuga ta zama ba muje ki karbo magani saikisha kinga exam muke fuskanta dan haka yakamta muzama ready
” OK bara mukammala cin abinci saimuje “
Bayan sun kammala suka wuce ta karba tasha sannan suka dawo hostel
Alhmdllh su jawahir anfara exam cikin sa’a saidai fa sunashan wuya cox karatun kasar waje ba dai yake dana nan gida ba saboda haka yasa suke zage dantse domin fito da result mai kyau
Yau ma dai sai 4:15pm suka fito saboda haka agajiye suke suna cin abinci kowa yanemi wajen hutuwa a k’wancenda suke ne sukeshan fira *Aleeyah* kece bestie wlh tinanin ranar rabuwarmu nake dake na saba tin muna yara har izuwa yanzu damuka mallaki hankalin kanmu
Fatana Allah yakara hadamu wani lokaci kuma yahadamu a aljannar firdausil a’ala ameen suka karba
“Wlh nima kawata ina wannan tinanin haka Allah yake lamarinsa gashi muba yan’uwa ba amma Allah yahadamu zama kuma harmuka zama kawaye tamkar yan’uwa “
Nan dai sukaita jimamin ranar rabuwarsu har bacci yadaukesu
Yau kimanin 3weeks da fara exam dinsu *Aleeyah* dik ta fada ta rame ga karatu ga tinani
Yaudai basu exam danhaka jawahir tace su shirya su fita mika kafa daganan suje su gaida yayansu Aryan *Aleeyah* taji sosai koba komai zata dan rage yawan tinani da damuwa
Sun shirya tsab cikin shiga maikyau jallabiyya ce baka da Rollin din mayafi red colour sunyi kyau matuka dikda ramar da *Aleeyah* tai amma hakan baihana bayyanar kyanta a fili ba
Aryan yay murnar ganin k’annensa cikin shiga mai kyau hakan yamatukar burgeshi hakan yasa shima ya shirya yaje dasu yawon shakatawa awurare daban -daban na hutawa aik’wa sunci sunsha harda tsaraba daga nan yawuce yakaisu school sannan shima yawuce
************ *************
Alhmdllh gobe takasance ranar farinciki agun su *Aleeyah* saboda gobe ne zasu zana jarrabawa ta karshe ta kammala secndry ss3 kenan saboda haka yau cikin farinciki suke sosai ko bacci sunkasayi sai shan fira suke suna tina baya wato lokacinda sukazo suna yara idan sun tina wannan su tina wancan susha dariya
Saidai fa a dayan bangaren basa farinciki idan suka tina fa rabuwa zasuyi kuma basusan ranar da zasu sake haduwa ba cox duk ba’a kusa suke ba *Aleeyah* na abuja jawahir na kebbi inda hanifa kuma take a yola bafulatana ce
Kowannensu yasan kasar da dan’uwansa yake amma basusan ainihin inda yake da zama ba
Kimanin 12:30pm suka fito daga exam school din dik ta hargitse koina sai celebrating ake su jawahir nacan zaune suna kallo dik sanye suke da uniforms saidai su sunsaka abaya a sama
Wasanni ake kala – kala gwanin birgewa gwanin ban sha’awa nan school din tasaka ranarda zata masu biki ai kwa sai murna suke
Ranar Monday itace ranar da aka saka domin yin shagalin bikin kammala secondry nasu *Aleeyah*
Yau takasance Thursday tin 10:20am Aryan yazo ya dauki su jawahir sukaje kasuwa sukayo siyayyar kaya wasu hadaddun abayoyi da jallabiyu hade da takalma saikuma kayan cosmetics ne yasaya masu wadanda zasu saka ranar bikin
Hukumar makarnta ta shaidawa kowanne uba daya kawo dansa cewar ranar Monday zatayi bikin yaye dalibai
Aryan yakira gida ya shaida masu komai sun tsara yanda yakamata tindaga masaukinsu har komai ma
Dadyn *Aleeyah* ma yakirata ya shaidamata suna nan zuwa nan ta nunamsu farincikinta da irin missing basu da tai amma saidai azahiri tsoro da fargaba ne fall afuskarta nan yake shaida mata tarin kyaututtukan da zai mata idan har tazama best student amakarantar ta nunamasa farincikinta sosai daga bisani suka rabu ta kashe wayar
Juyowa tai tadubi jawahir fuskarta ba walwala yar’uwata dady na da momy na zasuzo bansan ya zanyiba inatsoro wlh
“Kafadarta da dafa yar’uwarta ki cire tsoro ko fargaba azuciyarki karfa ki manta Allah yana tare da mai gaskiya “
Murmushi tai tace hakane yar’uwa ta
Nan suka wuce hostel dinsu hanifa cox yanzu ba karatu sai fira dakuma shirye – shiryen biki …………………….
*℘ąɠɛ 45~50*
*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*
Around 12:30pm aka kammala masu komai dayake ba mutum daya bace ke gyaran hakan yasa aka kammala masu da wuri
Hmm masha Allah zokagansu gwanin birgewa bama kamar tauraruwar tasha kunshi irin na yan India sumar kanta tasha mayuka kala-kala sannan aka tufkeshi gu daya fuskarta tasha make -up ga tsaleliyar rigarta jallabiyya wacca Aryan yasiyamasu had’e da Neil dinta red colour takalman ta ma red colour ne sai zuba uban kamshi take
Shi kansa gogan Saida ya yaba kyanda tai jawahir kuwa takasa yin shuru sai maganar kyan *Aleeyah* take
“Yar’uwa wlh tinda nake bantaba ganin kinyi kyau kamar na yau ba Ashe dama shiyasa kike k’in yin make-up koh saboda kinsan kyanda kike idan kinyi “
Murmushi tai tace wlh bahaka bane nidai daman make-up baidameniba shiyasa kawai
Nan dai aka kammala masu komai Aryan yazo yadaukesu suka wuce school
School din tacika sosai cox bayan makaranta kadai bane harda bakinda aka gayyata dakuma iyayen yara,nandai aka fara gudanarda bikin shikin nishadi dakuma farinciki abun yaburge mutane sosai
Anbawa yara kyaututtuka inda jawahir ta karbi lambar yabo wajen kokari da himma wajen karatu hakama hanifa ta karba nata dakuma sauran dalibban
Saida aka kammala bawa kowa sannan sukace zasu fitarda gwana jaruma daga cikin aikwa nan kallo yadawo dan ganin wacece wannan
Sunan Janifer David john aka kira cikin mamaki ta mike tsaye domin fita taje nan su jawahir suka dauki kuwa iyayenta kuwa sai farin ciki suke momynta harda yar kwallah ta farinciki
Bayan ta karasa nan ta karbi lambar yabo ta best student bakaramin jin dadi taiba bayan nan kuma suka bata ta mafikwazo kula da karatu dakuma mafi ilimi daga cikin yara
Bayan godiya ga ubangiji harda kwallah saida ta fitar saboda farinciki cikin dalibai kusan 6000 ace Kaine the best aciki ai wannan sai godiyar ubangiji
Bayan anbata nan sukace sunaso tabada takaitaccen tarihinta batayi kasa aguiwa ba tanasu cikin kankane lokaci takuma kara da nuna godiyarta gun iyayenta dasuka tallafa mata suka bata goyon baya harta kawo wannan lokaci sannan tace bazata taba mantawa ba da kawayenta wadanda sukayi rayuwar makaranta mai cike da jin dadi dakuma farin ciki sannan takara da yin godiya ga ubangijinta daya aramata rai da lfy harta kawo wannan lokaci daga karshe tayi godiya ga makarantarsu
Hotuna kala -kala sukayi tareda yan’uwa dakuma abokan arziki inda yan jarida sukayi caaa agun *Aleeyah* saida aka yi hostel da ita
Sunsha hotuna *Aleeyah* jawahir dakuma hanifa har basa kirguwa sannan sukayi da iayayensu iyayen hanifa ma sunzo dayake ita kadai ce agun iyayenta shiyasa suke masifar santa
Bayan ankammala komai kowa ya watse wajen yayi tsitt nan yan makaranta suka fara tafiya kowa saiwucewa yakai zuwa kasarsu sai bankwana ake da musayar nmbr wasu harda kuka saboda ansaba shekara da shekaru
Agunsu *Aleeyah* ma hakane duk sun hada kayansu kowa anzo daukansa nanfa kuka yace salamu alaikum rungume suke da juna tamakar ba tafiya zasuyi ba hanifa ce suka fara wucewa dakyar aka rabasu sai kuka suke
Bayan su hanifa sun wuce sai jawahir suka wuce tare dasu *Aleeyah* dayake filin jirgi daya zasu wuce lokacinda jirginsu jawahir zai tashi aisaida su Abba sukayi kamar sunayi sannan suka raba su kuka kuwa harda majina *Aleeyah* na kallonsu har jirgin su ya daga tanata masu bye bye tsaye take takasa zama zuciyarta namata kuna shikenan wai sunrabu da jawahir da hanifa kuma basusan ranar haduwarsu ba nan wasu kwallah masu zafin gaske suka dinga bin kuncenta
Zaune take tarasa meke mata dadi har jirginsu yatashi zuwa Abuja 8:15pm suka iso gida dakinta ta wuce saboda tasan lokacin sallah yayi saida ta tabbatar ta rufe dakin da key sannan tafara sallah bayan ta karasa tasaka kayan bacci tafito domin cin abinci
Duk suna falo dadynta na kallon news momynta kuma na dannar laptop kusa da momynta tazauna tadora kanta kan kafadar momyn
“Murmushi tai baby kinfito “
Kai kawai ta daga alamar eh
Muje kici abinci nasan kinajin yinwa,nan suka wuce taci abinci sannan tawuce dakinta ta kwanta
Haka rayuwa tafi gaba da tafiya idan lokacin sallah yay saitashige dakinta ta rufe sannan tayi sallah idan karatun QUR’AN kuma zatayi sai idan sun wuce wajen aiki sannan tayi ahaka rayuwa taci gaba da tafiya waje daga take samun matsala shine wajen saka kaya shiyasa bats cika fita ba
Wata ranane *Aleeyah* na sallah cikin dakinta sam tamanta bata sakawa kofar key ba kawai saiga momynta tashigo ai tsaye tai tamkar gunki tana kallon yarta tana sallah kuma ko ajikinta bata yanke sallar ba har momyn taje ta shaidawa dadynta shima yazo
Takaici bakinciki haushi dakuma danasani ne suka hanasa yin magana juyawa yayi yafita cikin kankanen lokaci yadawo hannunsa rike da belt kanta yay yadinga zuba mata bako sassauci dukanta yake iya karfinsa yana cewa Janifer kin zalinceni kin cucemu duk ina tarbiyyarda muka baki zakizo ki watsa mana kasa a ido tabbas bazan barkiba saina kasheki
Dikda irin dukanda yake mata amma hakan baisa tayanke sallar da takeyi ba momynta ce tazo ta kwace belt din ahannunsa kadaina dukanta hakanan tabbas Janifer ta cucemu cutarda bazamu taba yafemata ba
“Tana yin sallama tacire hijab dindake wuyanta nan jikinta yadinga rawa cikin tsoro tadinga ja dabaya am sorry dady kuyafeman dan Allah “
Ko saurarenta bayayi nan yasaka wata igiya mai karfin gaske ya daureta tareda gadonta daga yau bake ba fita kuma bake ba wannan addinin dakika dauko
“Dan Allah dady kayi hakuri kayafeman “
Tini momynta tafita daga dakin cox bazataniya kallon abunda ke faruwa ba
Kimanin 3weeks kenan banda azaba da masifa ba abunda yake ganamata dikta fita hayyacinta tini yahana momynta shiga dakin saboda ita ke kaimata abinci sallah kuwa saidai tayita anan
Shi acewarsa dole saita fada tadaina wannan addinin na musilinci ita kwa taki tafada
Azaba kala-kala yake mata abinci say daya ake bata ruwa kuwa sai takwana batasha ba duka zagi diktashasu
Watarana ne dai yaga ba sarki sai Allah dole ya kwanceta ammafa dik tafita hayyacinta tayi baki ta rame sosai
Wata ranane duk sunfita aiki ba kowa sai ita kadai aikwa nan ta tashi tasaka key tabude tafito ba kowa ai kukan tsintsaye ahankali tafito falo saidai a rufe yake nan tadauko takalman ta hill tasaka tsinin tafasa glass din window ahankali ta fito wajen fitowa harta yanke a yatsa amma saboda tsoron karaganta batama damu ba dukda jini na zuba amma hakan baidameta
Burinta kawai tafita daga gidan gudu take bata Batama San inazataje ba ahaka har tazo cikin wata unguwa bakowa tsitt nan tasami wata bishiya tazauna tana hutawa saboda shessheka da haki ko magana bats iyawa ……………………
*℘ąɠɛ 50-55*
*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*
Burinta kawai tafita daga gidan,gudu take batama San inazataje ba ahaka har tazo cikin wata unguwa bakowa tsitt nan tasami gun wata bishiya tazauna tana hutawa saboda shessheka da hak’i ko magana bata iyawa
Ahankali tadawo nrml nan tadan kwanta damin tahuta kamin tasami dabarar yi bata ankaraba bacci yayi awon gaba da ita anan
Hadari ya hadu dayake lokacin damina ne kankace me ruwa yafara sakkowa cikin bacci taji yayyafi ajikinta aikwa ba shiri ta fara tashi tarasa yanda zatayi gashi batasan kowa ba a unguwar tsaye take kwai abakin bishiyar har ruwa yadinga tafowa da karfin gaske ga cida ga tsawa gaya *Aleeyah* shegen tsoro ne da ita amma dikda haka saitaji ma tsoron yatafi
Tsaye ruwa saidukanta yake can saita hango wani gida bakin gate din gidan asamansa akwai wani rufing nan take tayi sauri taje tadan fake anan sai makyarkyata take da rawar sanyi
Ruwa ake bako kaukautawa ita kuwa tanan gun sai rawar sanyi take tasaka kanta acikin kafafunta fuskarta a rufe kuka take na takaici da nadamar samun iyaye irin nata wani bangaren kuma adduah take ga ubangiji daya kawo mata dauki acikin rayuwarta
Fada take acikin zuciyarta “tabbas nasan Allah baka manta daniba ya ubangiji na ka kawoman dauki dakuma sauyi na alkhairi “
Ahankali taji andafata cikin sauri tadago wa zatagani mutane karfafa guda hudu saikuma Aryan dayake tsaye agabanta cikin mamaki yakira sunanta *Aleeyah* meya kawoki anan cikin wannan lokaci bata iya amsa masa ba saima karkarwar sanyi datake ganin haka yasa yace sushiga gida
Sallama yay suka shigo atare mahaifinsa ne tsaye yana jiran shigowarsu inda mahaifiyarsa kuma ke zaune akan kujera
Mamaki ne yakamasu lokacinda sukaga *Aleeyah* abbane yace wannan ce “eh Abba itace Ashe ma mutum ce ni wlh nazaci ma ba mutum bace “
Allah sarki kekuwa baiwar Allah meyafito dake ahannun iyayenki awannan lokaci
Ahankali tace Abba labari ne maidan tsayi amma dai abunda zan iya cewa shine idan har nacigaba da zama da iyayena to tabbas watarana zasu kasheni
“Subhanallah kisa kuma “
Eh
*Aleeyah* batayi kasa a gwuiba nan take tabasu labarin dik abinda ya faru tin daga musulintarta har izuwa yanzu datake tsaye a gabansu
“Tin abban Aryan yana a tsaye harsaida yakai zaune saboda tsananin mamaki “
Tabbas yarinya kinyi namijin kokari kinyi abunda bakowanne da zai iyaba saboda tsoron halin iyayensa amma ke dikda haka kin jajirce kinyi wannan shi ake kira da
يخرجل حيامنل ميت
و يخرجل ميت منل حي
Wato fitarda rayayye daga cikin matacce
Dakuma fitarda matacce daga cikin rayayye
To wannan shine fitarda rayayye daga cikin matacce,Allah ya fitardake musulma daga cikin kafirai tsintsar kafirai masu riko da cristanci fatanmu ubangiji yakara maki San addinin musilinci kuma yatabbar dake acikinsa
Ameen suka karba
Nan yatambayeta ya sunanki tace masa *Aleeyah* masha Allah *Aleeyah* tabbas kinzo inda zaashare maki hawayenki wannan gidanane wadannan kuma iyalina ne idan har zaki iya zama damu toh bazamu taba jiya maki bayaba insha Allah
“Murmushi tai tareda fitarda kwallah Abba nagode sosai dakuka ceci rayuwa ta kuma Allah yabiyamuku bukatunku na alkhairi yasa kuyi kyakkawan karshe “
Ameen yata kidaina kuka daga yau insha Allah kuka agareki yazo karshe fatan ubangiji yabamu hakuri da juna sannan kidaukemu tamkar iyayenki ga yan’uwanki nan Aryan dakuma
Abdallah
Nan ya kalli Aryan yace masa son kuma kudauketa tamkar yar’uwarku kaji koh
“Insha Allah Abba “
Shikenan nan ya jiyo ya kalli hjy wacca ita sam ma hankalinta baya kansu yace hjy bakice komai ba
“Hmm alhj kenan to me zance bayan kagama yanke shawara kaida yayanka “
Murmushi yay yace bakomai Aryan jeki kanuna mata dakinta
OK Abba muje koh little sis
Nan suka hau sama sai cikin dakin da akace shine nata gsky ya hadu sosai komai nasa a tsare colour dinsa kuma purple ne gado saikuma wardrobe da mirror toilet sai karamain fridge nan dai ya nunamata komai
Murmushi tay tace yaya nagode sosai da yanda kuka karrama ni “bakomai little sis Allah yabamu hakurin zama” ameen tace
Bayan ya fita tay wanka tacanza kaya sannan tai sallah tana zaune tana lazimi saiga Aryan yashigo ya zauna bakin gado little sis lazimi akeyi
“Murmushinnan dai data saba shitasake masa eh ”
Toh ingama afito muci abinci kekadai ake jira
“Toh ganin zuwa “
OK nan yatashi yafita
Kwance tashi ba wuya awajen ubangiji yau kimanin 2weeks kenan dazuwan *Aleeyah* gidansu Aryan balaifi komai natafiya nrml saidai fa tanasamun matsala a gun ummansu Aryan dakuma kanensa Abdallah sam basa sake mata fuska kamar Aryan da abbansa
Hjy hafsa da Abdallah halayyarsu daya basa San talaka basa shan inwa daya da talaka sannan bata San kowa yarabi alhj tafisan daga ita sai yayanta halayyarsu ta banbanta data Aryan da abbansa
Sukam akwai San mutane basu dauki duniya abakin komai ba sannan basuda aboki kamar talaka shiyasa Idan sukaje kebbi toh fa basuda hutu wannan yazo wancan yazo harsai aljihunsu yakare sannan suke dawowa hakan yasa kuwa ake sansu ake yaban halayyarsu sabanin hjy hafsa da Abdallah
Kwanci tashi ba wuya yau kimanin 1month kenan da zowar *Aleeyah* agidansu Aryan sun shaku sosai da Abba balle kuma na hannun dama Aryan Wanda ko abinci baya iyaci inba *Aleeyah* ta girkashiba hakama Abba duk wata kulawa *Aleeayh* tana samu a gunsu saidai fa tanashan wuya ba karama ba a gun umma bata mata wasa sannan bata batafuska ga danbanzan aiki dikda sunada ma’aikata kala-kala amma haka zatace saidai nata takeso
Dikda azabarda takesha agunta amma bata taba kuskuren fadawa su Abba ba dikta rame tayi baki Idan kaga ta huta to dare yayi saiko Idan weekend ne tasan abba yana gida dan haka saita kyaleta harsai weekend yakare
Yauma dai kamar kullum kitchen take tana wanke wanke kwallah na zuba daga idanuwanta azuciyarta take fada “hmm rayuwa mai sauyi wai yau ni *Aleeyah* nice ke wanke wanke harda girki harma da wankin kayan wani ” kwallah keta zuba daga idanunta ahaka harta kammala sannan tafara dora girki……………………
*℘ąɠɛ 55~60*
*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*
Girki take sam bata kula da Aryan a bayantaba,tsaye yake yana kallonta yana murmushi waigowarda zatayi kawai suka hada ido wata iriyar kunya taji takamata ta sunkuyarda kanta tareda yimasa sannu da zuwa,
“Murmushi yay little sis sai aiki kike kekadai duk ina masu aiki da kike aiki kekadai “
Murmushi tai aa ninace zan iya inaso ne na iya girka dakyau shiyasa
“To shikenan bara naje falo kikawoman ruwa nasha “
OK !!!
Yana fita kuwa tahada drinks a tire tareda cup sannan ta gyara girkinta tayanda bazaiyi komai ba hartadawo sannan ta fita izuwa falo ;
Koda taje kuwa bata sameshi ba dayake dai tasan idan baya falo toh kuwa yana dakinsa dan haka kaitsaye saitawuce dakinsa ,
Zata shiga ne sai sukayi kicibis da umma cikin hanzari tsoro dakuma fargaba tayi saurin ja dabaya
Ke…ke wace irin wawuya ce jaka Mara hankali baki ganine zaki nemi ki kadani wai bama wannan ba ina zakine ??
Cikin in inna tace dama….dama …..yaya Aryan ne yace nakawomasa ruwa kuma nazo bangansaba shine zankaimasa dakinsa kuma dan Allah umma kiyi hakuri wlh bankualadake ba ;.
Yiman shuu karki kara kirana da umma niba ummankibace wato k’ilakancin naki yazo har kan d’ana koh toh wlh bari kiji tin wuri Kisan inda dare yamaki dan d’ana bazai taba auren sabon tuba ba kilaki kazama talaka yar kauye wato kinaga dadin bakinda kikayiwa Aryan da abbansa har yayi tasiri akansu muma zaki manashi koh toh wlh kinyi kadan
Kuma kisani Aryan yafi karfinki kilaki kawai bakauyiya talaka yar kauye ,Aryan hadaddiyar budurwa zai aura sabuwa gall ba sauran wasu ba sannan yar masu ji da naira ba wacca kudin albashin ubanta dadai da kudin breakfast dina na rana daya ba sannan wacca take cikakkiyar musulma ba sabon tuba ba wacca tagama sheke ayarta a titi ba
Ina mai jankunnenki sannan ina mai gargadinki da kifita daga sabgar yarona dan yafi karfinki ,tin lokacinda kikazo naga kina wani shisshige masa yayana yayana to wlh kisan inda dare yamaki tinkan nasaka aman waje dake ;
Zaki wuce kibani wuri kosai na mazga maki mari !!!
“Ahankali takama hanyar dakinta kwallah nazuba daga idanunta tafiya take tamkar kazarda kwai yafashewa aciki “
Tanashiga dakinta tafada kan gadonta nan tafara rera kuka zuciyarta namata kuna kwallah take zubarwa maizafin gaske aranta take fada “wa nice kilaki talaka yar kauye sabon tuba wacca taga sheke ayarta akan titi ” nan kuka yaci karfinta haka tadinga rerashi hartagaji tabawa kanta hakuri
Ganin babu sarki sai Allah yasa ta tashi tashiga toilet ta dauro alwala tafito tasaka hijab nantafa nafilfili tana kaiwa ubangiji kukanta,yi take hartagaji sannan tazauna tana lazimi shigowarsa ya katsemata laziminda take ;
“Little sis tin dazu naketa jiranki amma shuru kokinmanta dani ne “
Murmushi tai tace kashh dan Allah kayi nashafa’a ne amma bara nadauko ma akwai a wannan fridge din
“No barshi kawai nasha ai dama fita zanyi shine nace bara nazo idan da wata matsala ne “
Aa wlh bakomai Allah yakiyaye hanya
Ameen yace sannan yatashi harzai fita kuma ya dawo “sister naga idanunki sun kumbura sunyi ja sosai kinyi kuka koh kuma kinsan nahana yin hakan a aduniya ba abunda natsana kamar kukan mace kuma kinsani “
Ehh!!! Amma ba kuka naiba idonane keman ciwo shine fa yay ja amma ba kuka naiba
“Shikenan nafita sainadawo “
OK Allah yakiyaye yakuma tsare,ameen ya karba sannan yafita ;
Haka rayuwa tacigaba da tafiyarwa *Aleeyah* yau da dadi gobe babu
Wata rana ne *Aleeyah* na garding tana shan iska ganin ta kammala aikinta yasa tafito koazata sami saukin abunda ke damunta QUR’AN ne ahannunta tana karantawa Wanda Abba yasiyo mata ne,tayi nisa sosai da karatu haryasa batama San yazo kusa da itaba saida yay gyaran murya
Ahankali ta dago kanta tasakarmasa murmushi harsaida hakoranta suka bayyana Wanda shike kara birgesa da ita,sannu da fitowa yaya
“Shima murmushin yamaidamata yawwa malama karatu ake “
Ehh !!!
Masha Allah nan yazauna suka fara fira dikda firar shikadai ke yinta amma hakan yanamasa dadi dan yanaga a hakanma saitafi sakewa sosai ;
Tanajin dadin firar dashi hakan yakarawa burinta girma nason sanardashi sakon zuciyarta tabbas bazanyi kasa a gwuiba zan sanarda Aryan sakon zuciyata hakika natabbar da cewa Aryan shine Wanda zuciyata tadade tana mafarki amma zurfin ciki yahana na fahimci haka to yanzu ai ga dama tasamu
Hakika na yaba da halayyar Aryan amma saidai natabbatar da mahaifiyarsa bazata taba amincewa ya aureni ba bata Ankara ba kawai saitaga kwallah nafita daga idanunta Wanda sam bata sandazuwansuba kuma takasa controlling nasu ;.
” kallonta kawai yake cox tin dazu yasan hankalinta sam baya garesa tayi nisa cikin tinani danhaka baiyi mamakin ganin kwallah daga idanuwanta ba “
Sauri tai tagoge kwallar ta dukarda kanta kasa
Bata fuska yai yasha kunu tamkar baitaba dariya ba yace ” kinfi kowa sanin ba abunda natsana a duniya kamar kukan mace dan Allah *Aleeyah* meke damunki miye matsalarki ko gidanmu ne ake bata maki rai “
Ko daya wlh Aryan Kaine ke damuna kuma kaman alkawari hazaka gujeni ba koda nafadamaka damuwata
Hmmm!!! Ya nisa nayi maki indai har hakan zaizama silar kawarda damuwarki
Aryan nadade ina dakon sonka azuciyata amma kuma sai nakasa sanardakai wlh Aryan kainakeso inasanka nadade inasanka dan Allah karka gujeni ;
“Mamakine fall a fuskarsa yakasa magana saima shuru dayai”
Shuru ne yaratsa gun nawasu lokuta kamin yace “shikenan naji maganarki kibani lokaci izuwa nadawo daga u.s kinsan bamu kammala corse dinda mukaje yi ba yanzun ma nazone nashaidamaki gobe zamuwuce insha Allah “
Da sauri ta dago ta kallesa zaka tafi kuma ??
Ehh!!! Insha Allah
Ahankali ta dukarda kanta kasa batareda tace komai ba hakasukacigaba da zama har akayi kiran sallah sannan yatashi ya wuce masallaci itakuma tashiga gida ;
Around 8:30am su Abba da abdallah suka je rakiyar Aryan airport amma sam *Aleeyah* batasaniba har suka dawo sannan Abba yake fadamata aikwa taci kuka bakokadan ba harsaida idanuwanta suka kumbura haka dai ta hakura
1week datafiyar Aryan Abba yawuce Ghana aikwa *Aleeyah* taci kuka nan komai yajagulemata nan umma da abdallah suka bude sabon shafin wulakanci agareta dik zatabi agabansu ta wuce to zasucemata sabon tuba koh kilaki abunda ta tsana takuma kyamata Allah kawai take kaiwa kukanta ;
Zaune take a kitchen tayi tagumi saiga inna tashigo sam batasan dashigowartaba inna itace mai wanke wanken gida amma zuwan *Aleeyah* gidan umma tace tadaina yi ita tacigaba da yi,zama tai akusa da ita sannan ta dafa kafadarta tace “yar nan sannu koh gsky kina kokari wai nikwa nace laifin me kikayiwa hjy take maki wannan wulakancin koda yake ba sabon abu bane halintane wulakanta dan Adam sam bata son talaka batashan inwa daya da talaka amma saidai ke naga sam bakida kama da masu Neman balle nace aiki aka daukeki “
Murmushi tai tace inna ni wannan sam baidameniba naga ai ni mace ce yakamata nakoyi aiki kobakomai watarana gidan wani zanje saboda haka bandaukeshi amatsayin wai anatakurani ba ;
Hmmm!!! Toh shikenan nikwa sainaga kamar bakidace da aikatau ba amma Allah yazaba mana mafi alkhairi
“Ameeen tace “
Rayuwa mai sauyi yay *Aleeyah* takoma goro ko abunsaya dik ta lallace ta rame tayi baki banda wahala ba abunda take sha ga zagi ga kyara ga wulakanci idan ta wuce sukirata da kilaki sabon tuba yanzu yakai harma masu aikin gidan tasakasu suma sudinga kiranta da sabon tuba ;
Yauma dai kamar kullum *Aleeyah* na kwance a dakinta kwallah ke fita afuskarta can taji ana kwala mata kira cikin sauri harda gudu tafita me zata gani dukkannin mutanen gidan kowa a tsaye sai kallon ta ake atsorace takarasa tace umma gani ;.
Dakarfi ta dakamata tsawa ina sarkata take dubu dari hudu nasaita wlh saikin fito man da abuta,atsorace tace wlh ummu bandaukarmaki sarka ba banma San kin ajiyetaba
Karya kike Mara kunya fitsararriya dukwani Wanda yake gidannan anbincikeshi amma ba’aganiba nan Abdallah yace umma muje dakinta watakilma acan ta boyeta aikwa nan sukai dakinta ;
Itadai binsu kawai sai kwallah dake fitadaga idanuwanta,nansuka shiga binciken dakinta dubi na farko akaga sarkar cikin wardrobe dinta, wani wawan mari Abdallah ya sauketa mata harguda biyu wadanda suka sakata tadinga ganin jiri Saura kadan takai kasa belt dinsa ya zuge yadinga dukanta tin sunan cikin dakin har suka fito falo baidaina dukantaba ;
Jin sallamar da sukayi yasa suka juwa domin ganin maisallamar ….
*℘ąɠɛ 70-75*
*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*
Yau saura kwana d’aya su wuce kebbi sai shirye shirye suke,’……
Around 8:15am suka kama hanyar kebbi Abdallah ne ke driving d’insu, *Aleeyah* sai Kalle kallen garuruwa take coz tinda take bata Ta’ba irin wannan tafiyarba,,,….
Tin suna fira harsu *Aleeyah* sukayi bacci saboda nisan hanya harsai da Anwar Takar’bawa Ahmad driving saboda yagaji shima, around 4:40pm suka iso kebbi acikin unguwar G.R.A road bayan government house,,,’…..
*afuwan readers nayi mistake wajen sunan k’anen Anawar Ahmad ne ba Abdallah ba k’anen Aryan shine Abdallah amma yanzu nagyara muje zuwa*🏃♀🏃♀
Gidane wanda Takar’bi sunansa gida dakagansa kasan tamanin nerori aka zube wajen k’erashi, jira nake naga gateman yazo yankd’e Masu gate d’in kawai sainaga gate yabud’e dakansa ahe wannan new modern ne ba irin Wanda nasani ba
Wayaga d’ank’auye yaje burni O.G a London tab da akwai k’auyanci
Bayan gate yagama bud’ewa saiyashiga yaje inda ake parking sannan yatsaya suka fito, kallon gidan *Aleeyah* keyi tsabb alokaci d’aya taji yaburgeta saida Anty Mimi ta Ta’ba ta sannan tadawo da hankalinta “murmushi ta mata tace muje koh” nansuka kama hanyar shiga gida kamin su isa saiga mutanen gidan sunfito suna murna cukin farinciki mami “wato mahaifiyarsu Anawar” tazo tana tarbansu nansuka gaidata cikin girmawawa sannan suka gaida Abba wanda yafito yanzu, Anty Mimi ce tace aa mami ina auta ne bangantaba kobatasan da zuwanmu bane..? murmushi tai tace auta ba lfy tanacan kwance a d’aki eyyah gaske dai babgantaba,,,….
Atare suka wuce izuwa cikin gida a falo suka baje anak’ara gaisawa mami sai kallon *Aleeyah* take kamar tanaso tatina inda ta Ta’ba ganinta saidai ta kasa kuma bata mata magana ba, sakkowa take tareda yin sallama jin sallamar ne yasa *Aleeyah* d’agowa wazata gani bestieee tafad’a cikin mamaki itama d’in tsaye tai cikin mamakin ganin nunansu ai *Aleeyah* batasan lokacin taje suka rungume junansu ba,,,…..
Nan kallo yakoma kansu, dukansu kuka suke nafarinci *Aleeyah* ce keep magana “jawahir banta’ba zaton zamusake had’uwa ba yar uwata nayi kewarki wlh baked’an ba” nima haka yar uwata ashe darabon zamusake ganin juna hak’ik’a narabu dake ne kawai amma wlh dik wani tinani nawa yanakanki inama zanganki nataimake wajen tseratarda addinin ki a kullum cikin fargaba nake narashin sanin yanda zaki k’are da iyayenki alokacin da suka gano gsky,’…
Murmushi tai sannan taja hannunta suka zauna akusa da mami, nan jawahir ta kalli iyayenta da yan uwanta wad’anda suka saka a duhu sannan tace mami abba wannan itace wacca nake baku labarin ta, mami ce tace wlh tind’azu kallonta nake inaso natina inda nasanta amma nakasa, jawahir tace saidai nakasa gane ina kika had’u dasu Anty Mimi…??,
Murmushi *Aleeyah* tai tace jawahir labari ne mai tsayi Anwar ne yaisaurin cewa “nine nabigeta da mota akan titi shine said’auketa nakai ta hospital d’inmu bayan ta farfad’o ne sainace tafad’aman address na gidansu saboda iyayenta susan halinda take ciki nanne take shaidamin cewa batada iyaye kuma batasan kowa ba intact ma batasan wane Hali rayuwarta take cikiba shine sai nataimaketa nad’auketa nakaita gidan Anty Mimi,,,……….
Jwahir tace bro k’arya tamaka tanada iyaye saidai akan wani daliline yasa tace maka hakanan, murmushi *Aleeyah* tai Wanda dakagansa kasann ma’anarsa sannan tace ka gafarce ya Anwar yanzu zansanardaku gskyr labarina nan tafara basu labarin komai har’izuwa zamanta a gidan Anty Mimi,’…
Shuru yaratsa falon sai sheshekar kukan jawahir da *Aleeyah* kakeji sai akarasa mai magana acikin falon tini idanun Ahmad sun kid’a barekuma na Anwar Anty Mimi da mami kuwa tausayi da takaici yahanasu ko motsin kirki balle magana,,,…..
Abba ne ya nisa sannan yafara magana “”hak’ik’a tabbas *Aleeyah* kincika cikakkiyar jaruma saboda da’ace bakida k’arfin imani hak’ik’a dazaki iya komawa kafirci saboda irin wannan halin rayuwar dakika fad’a dik asanadin kin kar’bi addinin musilinci, Mami ce taisaurin cewa “”wlh alhj hajiya hafsa tabani mamaki matuk’a ashe haka halayenta suke aishi d’a nakowane wlh tabani kunya musamman nakasancewar uwa sune mutane nafarko datafara kasancewa dasu musulmi bayan su jawahir maimakon ace tasakata ajiki tayanda zataji babu wani addini dayafi musulinci dad’i amma ina sanzuciya yahana tirr damasu hali irin na hajiya hafsa “”
Abba yace shikenan alhmdllh tinda dai batamayi tinanin kimawa addinin suba dikda irin uk’ubardatasha yanzu dai muyi batun warware matsalar tukunna,,,…
Anwar yace dama Abba jurakawai nake muzo inaso zanmaidata School tacigaba da karatu tare da jawahir bayannan sannan muje musasanta da iyayenta,’.
To dakyau hakan ma yafi saidai ai takardunta basanan kaga dole dai saimunje Abuja saboda komai ayishi cikin nutsuwa bada rigima ba, *Aleeyah* taji dad’i sosai da irin nunamata k’aunardasukayi aikwa nan taitamasu godiya harda kuka nan jawahir ta jata suka haye sama dayake gidan hawa biyu ne,,,…..
******** *******
*U. S*
Kwance yake yarasa meke masa dad’i yayi zurfi sosai cikin tinani har akashigi baisani ba kafad’arsa yabuga sannan yadawo daga duniyar dayaje tashi yai zaune sannan suka gaisa “”haba Aryan wai meke damunka ne dik karame kayi bak’i kanisanta kanka da mutane haba meke damunka ne nadad’e ina tambayarka amma Kai’i kasanardani abunda ke damunka yau kwana biyu kenan banganka awajeba shine nace bara nazo naji ko lafiya nayi kusan 15minute’s atsaye amma bakamasan nazo ba haba meyai zafi ne haka “”
Hmm….!!! yanisa Faruk nakasa gane abunda zuciyata takenufi nakasa gazgata ta nan yafada’amasa komai, dariya yadinga masa sannan yace wai dama akan wannan yar k’aramar ne kawani bi dik kadamarda kanka,’…
Kallonsa kawai Aryan yayi batareda yace masa komai ba “”Aryan gsky zuciyarka take fad’a ma tabbas son *Aleeyah* ne yakamaka shine yamaka shigar bazata nidai abunda zance shine Allah yataimaka yafada’a yana dariya””
Murmushi Aryan yayi sannan yace haba faruk taya zanyarda da haka bayan ni banta’ba cemata inasanta ba “hm aikwa gwara ma kayarda idan basanta kake ba miyasa kake tinaninta meyasa kadami kanka akanta meyasa kake mafarkinta meyasa kadamu kasan halinda take ciki kuma meyasa kakeson kaji muyarta”…..??
Wad’ann dika basa samuwa idan dai harbasnta kake ba kaga ni Karma ka shiriritani kaima dai yakamata kabar wannan zancen katashi zuwa shiri jibi mubar masu k’asarsu zuwa tamu,,,….
Tashi yai tsaye yace wlh ma ni wannan k’asar dik taisheni nadamu nakoma alhmdllh dai tinda munfito da result mai kyau u.s kuma bye bye ita da sake ganinmu bakusa ba,’..
Murmushi faruk yai yace aidole kace taisheka tinda *Aleeyah* batanan, dariya sukai suka tafa sannan yawuce nasa gida,,,….
Around 10:00am agogon Nigeria jirginsu Aryan yataso izuwa kasarmu ta gado Nigeria saikusan 1:30pm sannan suka sauka, umma da Abdallah ne suaje taryansa a air port yaji dad’in ganinsu sosai daganan suka wuce izuwa gida,,,…
***** *****
Farinciki bashi misaltuwa acikin zukatan su *Aleeyah* da jawahir yau kwanansu biyar da zuwa mami tasaka *Aleeyah* gaba tana koyar daita ilimi tini tasakasu haddan hizifi 10 kasancewar mami malama ce ta addinin islama sam batawa yaranta wasa da ibada har islamiyya Abba yasaka aka gina mata shiyasa tafi zama a kebbi, ‘..
Kyawawan halayenta da kyawawan d’abiunta ne su Anwar suka biyo yawan son ibada son mutane ga yawan son kyauta, Sam abin duniya baya gabanta duk su Anwar ahannunta sukayi karatu harsuka sauke,,,…
Jawahir ce kwance tana tilawa *Aleeyah* kuma na gefenta d’aure take da towel fitowarta kenan daga wanka…………….
*℘ąɠɛ 75-80*
*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*
Jawahir ce kwance tana tilawa *Aleeyah* kuma na a gefenta d’aure take da towel ajikinta fitowarta kenan daga wanka,’……
Mai tashafa sannan tasaka kaya suka wuce zuwa islamiyya 6:30pm suka dawo bayan sundawo mami tawuce kitchen dasu saboda mami sam batayarda ba wai ace yara mata basu aiki hakan yasa atare take shiga kitchen dasu,,,….
Girki sukayi masu shegen dad’i harkala uku bayan Sun kammala ne suka fito lambu suka wuce suna firarsu sunashan iska kawai sai aka sakko da ruwan sama aikwa nansuka dinga wanka aciki su *Aleeyah* sarakunan son ruwa dik Sun jik’e, Mami ce tafito tana nemansu sabosa bataji hayaniyarsu ba kawai saita hagesu acikin lambu kira ta kwala Masu wai yarannan kunacikin hayyacinku kuwa bakuko tsoron mura yakamaku, jin kiranda mami ke kwala masu yasa sukazo dagudu *Aleeyah* sai dariya take d’akinsu suka wuce suka canja kaya sannan suka fito d’akin mami suka wuce tana Masu fira,’….
Yau takasance Thursday su *Aleeyah* basa zuwa islamiyya Elham ce ahannunta tana mata wasa kursum kuma tana gun auncle d’inta Anwar dik suna a falon kasancewar yanzu sukayi breakfast dayake AL’adarsuce baysn break saisunzauna falo sunsha fira kamin kowa yaje zuwa aikin gabansa, fira suke amma hankalin Anwar nakan *Aleeyah* dik wani motsi nata a idanunsa yake tini Ahmad yakula dahakan saidai baiyi magana ba “”Abba yace su Anwar su koma Abuja idan aka sauke masa kayanda aka turo masa daga India shima saiyazo shi dasu mami”” nandai suka shirya yanda tsarin zai kasance dagabisani kowa yawuce zuwa aikin gabansa,,,……..
******* *******
Liyafa aka shirya tamusamman saboda dawowar Aryan da isowarsa yashiga wanka bayan yafito yashirya sannan yafito waje umma da Abdallah ne a falo zaune shima zama yai suka k’ara masa sannu da dawowa daganan suka wuce dining, bayan yaci yak’oshi sannan yake tambayar umma *Aleeyah* nan aka rasa mai magana ita da Abdallah ganin haka yasa hankalinsa tashi “”umma dan Allah kufad’aman ina *Aleeyah*….??”” cikin ‘bacin rai umma tace Aryan wakabawa ajiyarta ne dazaka dinga damuna da tambayarta waya sanamata k’ila ma takoma wajen kilakancinta Kai kazo Kana tada hankalinka Akanta,’.
Idan ransa yayi dubu to ya’baci jin mummunar kalmar da mahaifiyarsa takira abar k’aunarsa da ita kilakanci yasake maimaita kalmar “”haba umma meyasa zaki jefi *Aleeyah* da wannan mummunar kalma wlh sam batada wannan d’abiar halayenta Masu kyau ne *Aleeyah* tsabtatacciya ce meyasa kuka bari tafita daga gidannan natabbata be’asan ranta tabar gidannan ba”” rai a’bace yatashi yawuce izuwa d’akinsa,’..
Kan gado yafad’a sai juyi yake yarasa meke masa dad’i aduniya azuciyarsa yake magana “”haba ummana meyasa kuka Man haka meyasa kuka bari *Aleeyah* ta tafi, dan Allah *Aleeyah* kidawo gareni nafad’a maki amsar maganarki inasanki wlh inasanki da dikkanin zuciyata banta’ba san wats y’a Mace ba aduniya sai ke kada ki gujeni dan Allah kidawo ga reni idan kika barni bakima zuciya ta adalci ba, yanzu ne ta amince da k’udirinki sannan ta amince dake amatsayin masoyiyarta kada ki barni yak’arasa yana mai zubda kwallah””,.
Kimanin kwanansa shida da dawowa tini yakoma aiki saidai dik ya canza bayasan zama cikin mutane bayasan hayaniya da damuwa yafisan zama shikad’ai, abun yafara damun umma tin bata kulashi yanzu hartafara kulashi coz abun yafara damunta tanasan Aryan fiye da komai nata hakan yasa ko kad’an batasan damuwarsa,’…
Kwance yake a d’akinsa dawowarsa kenan daga gun aiki, wayarsa ce ahannunsa yana kallon hotunan su *Aleeyah* wad’anda yamasu ranar bikin kammala makarantarsu ita da jawahir da hanifa ne suna dariya pic d’in yayi kyau sosai akoda yaushe suke tayashi fira saikuma tinanin *Aleeyah*, jin sallamar da akayi ne yadawo dashi daga tinanin da yake,,,….
Ummace tak’araso tazauna akusa dashi sannan tace “”haba Aryan tin d’azu fa naji shigowarka amma kokazo kagaidani Kak’i nalura Aryan tin dawowarka daga u. s komai naka yacanza kadaina walwala kamar da haba yakamata kafa tina kai ba yaro bane “” hmm….!!! yanisa umma kinfi kowa sanin damuwata umma narasa waye daliline yasa kuka kori *Aleeyah* daga gidannan shin wane laifi tamaku shin baki tinanin wane hali take ciki haba umma kefa uwa ce shin zakiji dad’i idan akace y’arkice akayiwa haka yazakiji natabbata bazakiji,,,….
Shuru tai kawai batace dashi komai ba ta tashi tace kafito kaci abinci yana dining table ina a falo inajiranka tana fad’ar haka tafita, ksanciyarsa yai saida yayi yan mintina sannan yafito,,,……
******* *******
Yau takasan ce Saturday around 11:15pm su *Aleeyah* sukaci gayu sunyi matukar kyau cikin wani tsadadden sweezless pink colour yamatukar yimasu kyau dikda *Aleeyah* bawani make-up taiba amma hakan baihana kyanta bayyana ba, bayan Sun shirya ne suka fito gun mami sukaje suna rok’onta tabarsu suje kasuwa dakyar ta amince saidai tace batayarda suyi driving dakansu ba saidai Ahmad ko Anwar yakaisu, kasancewar sunasan suje yasa basuyi musu ba,’..
Atare suka fito suna jiran AAhmad yafito……………….
*℘ąɠɛ 80-85*
*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*
*A* tare suka fito suna jiran Ahmad saiga Anwar yafito cikin shiga Mai kyau shaddace gizna light blue da hula yamatuk’ar yin kyau sai zuba k’amshi yake,’…..
Sunyi matukar yin mamaki coz basu Ta’ba zaton Anwar zaiyarda yakaisu ba saidai kuma indai mami tai magana toh ba musu,,,…….
Tinda yak’araso ko kallonsu baiyiba yashiga mota yatada ganin haka yasa suma suka shiga yafigi motar sai Central market, cikin k’ank’anen lokaci suka isa atare suka shiga suna siyayya,’.
Suna cikin tafiya daidai gun Masu siyarda jakukuna cikin rashin sani jawahir ta bangaji wata yarinya har kayanda ke hannunta suka zube juyowarda zasuyi saisukayi kallon kallo, farida ce Class mate d’insu kawar hanifa, dariya sukayi sannan suka gaisa *Aleeyah* ta duka ta kwaso kayan ta mik’a mata jawahir tace “”wai kina had’uwa da k’awarki kuwa…? “”
“”murmushi tai tace eh ai garinmu d’aya da ita a unguwa d’aya ma muke “” Allah sarki wlh tin damuka k’are school rabonmu da ita bani phone Nmbr d’inta da naki “ok” nansukayi musayar Nmbr sannan suka rabu,,,…….
Sai kusan 2:30pm sannan suka kammala suka fito abakin gate suka tararda Anwar yanashan fira shi da abokanansa, dariya yamasu yace harkun fito ai nad’auka ko duka kasuwar zaku siye, dariya yabasu akakawo masu kujera suka zauna sannan suka gaisa da abokin Anwar,’..
Kallon *Aleeyah* yai tamik’a mata wata cover do’alamu dai tazobe ce yace kar’ba gwada muga ko zaimaki, bata masa musu ba takar’ba tasaka…. Woww zo kuga yanda yamata kamar danta aka k’eroshi, kallonta jawahir tai tana dariya tace “yamaki kyau kamar danki akayoshi ” murmushi tai sannan ta kalli Anwar tace yayana nagode sosai amma ina na tar’uwata…?,,,
Murmushi yamata sannan yamik’awa jawahir agogon hanu shima mai shegen kyau ne ga tsada nansuka masa godiya sannan yatashi suka wuce,,,…..
Da komawarsu gida suka kira hanifa tayi matuk’ar jin dad’i sabida itama nemansu take ruwa a jallo taji dad’in kasancewar *Aleeyah* agidansu jawahir da jawahir ta bata labarin yanda *Aleeyah* ta kasance asanda iyayenta suka gane ta musulunta harda kuka saida tai da irin wahalhalunda tasha, nan tafad’amasu tanan zuwa Abuja itama gidan baffan ta sunji dad’i sosai sunjima suna fira sannan sukayi sallama,’..
Ranar Saturday around 8:00am su jawahir dama kowa na gidan suka kama hanyar Abuja cikin dalla dallan motocinsu, abunda yawargaza tsarin da sukayi na su Anwar su fara tafiya daga bisani su Abba suzo shine kayanda Abba yatsaya jira ne suka iso da wuri hakan yasa yace kawai su shirya su wuce atare, sai kusan 5:30pm sannan suka iso Abuja,’….
Kwanan su biyu da dawowa suka saka ranarda zasuje gidan iyayen *Aleeysh* domin sasanta tsakaninsu ranar Saturday mai zuwa suka saka,,,…..
Kwance take itakad’ai jawahir ta fita saiga Anwar yashigo, da sauri ta tashi zaune tareda janyo blanket ta rufe jikinta saboda rigar bacci ce ajikinta iya cinya mai Hannun bes, dariya abun nata Yabashi zama yai akusa da ita yana kallon ta “”My pretty bacci kike “” cikin in in na tace aaa…… aa wanka zanyi “ok” to kiyi sauri kifito yunwa nakeji ki dafa Man indomie dasauri tace to coz dik a tsorace take yafahimci haka wani mayen kallo yabita dashi harsaida ta d’auke kanta daga kallonshi blanket d’inda ta rufa dashi komai bai rufe mata ba bress d’inta awaje coz rigar batada duhu sosai, ganin yanda ta takure jikinta yasa shi yamik’e zuwa fita saida yakai bakin k’ofa yace kiyi sauri kifito inajiranki “to” tace sannan yafita,,,….
Kimanin k’arfe 12:15am su *Aleeyah* na bacci kawai ta farka da k’arfi tareda buga wata irin k’ara a tsorace da sauri jawahir ta farka nan *Aleeyah* ta rungumega tana kuka jikinta sai rawa yake ganin haka yasa jawahir taje takirawo mami, cikin sauri mami tazo *Aleeyah* ta rungumeta tana kuka nan mami tadinga yimata karatun tareda addu’oi har tadaina karkarwar da takeyi ahankali har bacci ya d’auke ta nan mami tace”jawahir meke damunta ne….? Wlh mami ina bacci kawai naji k’arar ta hmm….!!! Shikenan Allah shikyauta ameeen jawahir tace,’..
Adaren dai d’akinsu mami ta kwana dasafe saida ta tabbatar da babu wata matsala sannan tawuce d’akin ta, around 8:15pm Abba yakira su nawahir falon sa *Aleeyah* na kusa da mami nan Abba yace “” *Aleeyah* menene kika gani jiya ya tsirata ki..? “” ahankali ta d’ago tace Abba yau kwana hudu kenan did na kwanta sai nayi Mafarkin wata mata wacca nata’ba gani a gidansu Aryan, itace ta kwaceni alokacin da Abdallah ke duka na itace nake mafarki wani lokacin tanaman dariya wani lokacin kuma tana kirana, to jiya bayan mun kwanta naganta cikin mafarki cikin wani mawuyacin hali tana ceman nazo nataimaketa, naje zan taimaketa saiga wani mummunar halitta yazo yad’auketa nikuma yajefa ni cikin wani k’aton rami,,,….
Abba yace shaid’an ne kezomaki wata k’il ma bakiyi addu’ah ba dazaki kwanta “”wlh Abba nayi “” shikenan ranar Saturday insha Allah zamuje gun iyayenki saboda haka kutayamh da addu’ah insha Allah mami tace *Aleeyah* dai batace komi ba har suka koma d’akinsu,,,…
******* ******
Zaune yake a office d’insa yasaka waya agabansa sai kallon pics d’insu *Aleeyah* yake sai yaji ana nocking…..yes!!! yace sannan mai nocking d’in yashigo,,,….
Ganin babban aminin sa daya jima baisanyashi a ido ba yasa yataci cikin farin ciki suka rungume juna “”My best friend welcome back cewar Anwar “” cikin murmushi Aryan yace thanks my friend have a site, nan suka zauna suka k’ara gaisawa Anwar yace naje gida shekaranjiya umma tace kafita ” Allah sarki yh su mami na” dik suna klw klw, fira sukai akan harakokinsu inda suka kwana dakuma inda zasu tashi Sun jima sosai suna tattaunawa daga bisani suka wuce gidansu Aryan,’…
**********
Around 10:15am su Abba suka shirya zuwa gidan iyayen *Aleeyah* cikin shiga Mai kyau wata dakakkiyar shadda ce suka saka Anwar da Ahmad riga da wando ne kawai Abba kuwa harda bsbbar riga, acikin sabuwar motar Abba suka shiga Ahmad ne ke driving,,,…..
Koda suka isa cikin unguwar kuwa basu wani wahala ba suka gane gidan, suna isa kuwa suka tararda gate man awaje ysna shara nan sukayi parking sannan suka pito, sallama suka masa sannan sukayi musabah nan suka tambayeshi nanne gidan pastor David yace Masu He..!!! Abba yace yataimaka suganshi, baimasu musu ba kuwa yace sujirashi nan yashiga domin yakira masu shi……………….
*℘ąɠɛ 85~90*
*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*
Baifi minti biyar ba dashiga yafito yacemasu su shiga,’……
Shine yashiga gaba sukuma suna binsa baya har suka isa cikin falon hotunan *Aleeyah* suka fara cin karo dasu wasu tana k’arama wasu kuma dagirmanta sai wani wanda yafi kowanne girma ita da iyayen ta anrubuta masa Happy Birthday Jenifa baby,nan suka tabbatar da nanne gidan, zaune yake shikadai nansuma suka zauna sannan suka gaisa,,,…..
Abba yace ina fatar bamuyi ‘batan Kai ba kaine mahaifin Jenifa jin an ambaci abar k’aunarsa yasashi yamik’e dasauri tareda cire glass d’inda ke idanunsa da mamaki yace “”of course nine kunganta…??”” murmushi Abba yai yace come down my Frnd zauna kaji abunda ke tafe damu zama yai jikinsa a sanyaye Abba yafara magana “”wannan d’ana ne Anwar shine yabige jenifa da mota a bakin titi shine sai tad’auketa yakaita asibi bayan tasamu sauk’i ne yatambayeta gidansu saitamana kwatance “”,…..
Kwallah sukaga yana fita daga idanunsa sannan yafara magana “dik abunda yafaru da jenifa laifina ne nine sila nabiye rud’in zuciya na azabtar da y’ata bayan kuma nayiwa ubangijj alkawarin zan kula da ita hartsawon lokacin da zan maidata hannun iyayenta kiyafeman jenifa don yanzu natabbata yesu nafushi dani miyafeman jenifa… Kuka yaci k’arfinsa yakasa cigaba,’….
Maganarsa tasaka su Anwar cikin rid’ani Abba yace pastor David what do you mean by har kumaida jenifa gun iyayenta kanaso kace mana kenan bakune iyayenta ba….??,,,…
Tsaye sukaga yamik’e yace kujirani ina zuwa 5mintes da fitarsa saigashi yadawo tare da matarsa suka zauna yace Masu this is my wife Grace itace ta reni jenifa kuma zan sanardaku gsky saboda yanzu jenifa takuce tinda ta musilinta kodon kutayani neman iyayenta domin nacika alk’awarin da nai a church,’…
Kimanin 18 years dasuka wuce wata ranar Sunday muna tafiya da dare ni da grace kan hanyar mu tadawo daga kebbi sai mukatsaya abakin hanyar wani k’auye domin grace tayi fitsari, bayan fitarta da 15minutes saitadawo a tsorace wai kukan jinjiri takeji koda naje kuwa saimukaga jinjiri acikin zane yanata tsala kuka nan nai addu’ah waiko aljanine sainaga bashida kama dasu nan nasaka hannu nad’auka muka koma cikin mota, k’auyen dake kusa mukaje aka nuna mana gidan Mai gari nan muka nunamasa abunda mukai tsintuwa Mai gari yasaka akayi shaila aka bincika dika k’auyuyyukan dake kewansu Amma ba’agane iyayenta ba, ganin irin jimawarda mukai bamusami haihuwa ba yasa grace sha’awar d’aukan babyn amatsayin babynmu banmata musu ba coz nasan tanaso nan nacewa Mai gari zamuje da ita har jibi musake dawowa baiyi mana musu ba kuwa nan muka wuce,’…
Bayan kwana uku muka koma nanma dai shuru ba’agane ba, ganin haka yasa kawai bayanke shawarar d’aukan babyn muraineta har izuwa lokacin da za’agane iyayenta nan nabawa Mai gari address d’ina da phone Nmbr ba sannan muka dawo Abuja,’…
Bayan mun dawo mukaje church akayi biki nasaka mata suna tareda d’aukan alk’awarin maidata hannun iyayenta idan muka ganesu, tin daga wannan likacin dik bayan 5months saimunje k’auyen amma shuru har muka maida 3yeras haryanzu dai shuru gashi yanzu kuma nasa’ba alk’awarin da nai,,,…….
Hmm!!! Suka Nisa Abba yace alhmdllh yanzu dai jenifa tana hannunmu kuma yanzu sunanta *Aleeyah* zamu kawo maku ita kuganta amma bazamu barta anan ba zataci gaba da zama awajenmu har izuwa likacin da za’agane iyayenta sannan yakamata muje k’auyen kasaka mana likacin da zamuje,’…….
Murmushi yai yace toh bakomai idan nashirya zansanar daku grace tace “please kukawoman Jenifa naganta nayi missin Nata sosai” murmushi Ahmad yai yace zankawomaki ita har nan karkidamu mommyn jenifa dariya tai tace “to bagode”,,,…
Nan suka tashi zasu wuce harsun fita Anwar yadawo yace abashi Takardun *Aleeyah* nakammala secondary school yanaso taci ggaba ne pastor David yaji dad’i sosai dahakan baiyi musu ba kuwa yabawa Anwar sannan yarakasu har bakin gate saida suka wuce sannan yakima ciki,,,….
Ba k’aramin jin dad’i ba Anwar yai dayaji cewar basu suka haufeta ba su Abba kuwa bak’aramin mamaki sukayi ba, basu wani jima ba suka isa gida kasancewar Ahmad nagudu sosai kuma dai banisa sosai, ‘..
Su *Aleeyah* suka fara cin karo dasu sundawo daga wajen hadda nan suka masu sannu da dawowa idon Anwar kyam akan *Aleeyah* tini Ahmad yahangosa aikwa nan yadinga tsula dariyarsa idan yatambayeshi saiyace ba komai, itama ta kula da kallonda yake mata hakan yasa tawuce abunta cikingida,’….
Atare suka shigo nan aka baje acikin falo Abba bai ‘biye masu komai ba yanda sukayi da pastor David abun kuwa yamatuk’ar bawa su Mami mamaki saidai tai godiya ga Allah dayasa ba wad’annan Christan bane iyayen *Aleeyah* haka itama ta fad’a,,,……
******** ******
Aryan abun duniya ya dameshi duniyar gabad’aya jinta yake badad’i yarasa ina zaisaka kansa yaji dad’i son *Aleeyah* na neman yahaukatashi babu wani abu dazaiyi yaji dad’i inba tinaninta ba ko kallon hotunanta, abun yadami ummansa babu wani mataki dabata d’aukarmasa ba amma dik abanza akan wata banzar yarinya d’anta nanema yasusuce komai nasa yacanza walwalarsa dakomai nasa yacanza kullum idan tamasa magana zancensa d’aya ne tanemomasa *Aleeyah* itace kid’ai maganin damuwarsa,’….
Zaune yake a falo shikad’ai TV a kunne yana aiki amma sam hankalinsa bayagun TV umma ce tashigo ta zauna akusa dashi amma dik baisaniba saida ta dafashi tareda kiran sunansa ahankali yad’ago yadubeta yajuya fuska “”haba Aryan wannan wace irin rayuwa ce kabi katakura kanka akan wata kaduba yanda dik kabi karame haba Aryan dan Allah kacire wannan damuwar banaso, yakamata kadinga d’aukan maganata da muhimmanci amatsayi na namahaifiyarka,,,….
Hmm!!! Yanisa sannan yace umma ke mahaifiyata ce kuma natabbata dik uwa tanasan farincikin d’anta to meyasa ke bazakuso nawa farincikin ba *Aleeeyah* itace farinciki na kema kisota kicire karan tsanar da kuke mata kutayani addu’ah Allah yahad’ani da ita kuma yasa itace uwar y’ay’ana, wlh umma banta’ba San wata ba kamar *Aleeyah* inasanta fiye da tunanin mai tinani kema kiso ta dan Allah umma na,’….
Jan kalaman Aryan sunsanya jikinta yin sanyi cikin k’auna tashafa fuskarsa zan tayaka addu’ah insha Allah amma saika rage wannan damuwar murmushi yai yace maganin damuwana umma *Akeeyah* ce batasake ce masa komoi ba ta tashi tawuce d’akinta,,,……
************
Kimanin 3weeks dazuwansu Abba gidan pastor Anwar yafara kiciniyar nemawa su *Aleeyah* admission cikin Sa’a kuwa aka samu a F. U. B. K kebbi State bak’aramin jin dad’i *Aleeyah* tai ba nan akafara shirye shirye 2weeks dasamun admission suka wuce school cikin k’ank’anen lokaci suka fara karatu inda *Aleeyah* ke karanta low jawahir kuma medicine,,,…
Masha Allah ubangiji yabaku Sa’a ameeeen
Aranarda zasu wuce ne *Aleeyah* taje gidan pastor sunyi farinciki sosai sannan sunnemi yafiyarta nan tace bakomai Allah Ta yafemana aranar dai acan ta wuni ita da jawahir sai maraice Ahmad yaje tad’aukosu,’…
Kwana hudu da tafiyarsu school su Abba sukaje k’auyen marke Mai gari yasanrdasu shekara d’aya data wuce wasu sunzo neman y’arsu kuma yanda sukayi bayanin inda suka tsinceta itama matar haka tace anan ta ajiye y’arta rashin zuwansu pastor ne yasa ta tafi amma tabar Nmbr d’inta idan sunzo sai akirata, Anwar baitsaya ba kuwa yak’arbi Nmbr yakira sannan yabawa abba sukai magana nan tasanya lokacin da zasu had’u kasancewar basa k’asar, Abba basubar k’auyen ba saida yaciksa maigari da abun Arziki aikwa nan yaita godiya sannan suka dawo gida,,,…
Karatu suke ba kama hannun yaro coz university bad’ai take da secondary ba aikwa su *Aleeyah* har anfara rama kimanin 3month’s dazuwansu hanifa tazo Abuja aikwa basuji dad’i ba nansukai ta rigima harsauda driver yakaita kebbi gunsu ssunji dad’i Sosai dazuwanta…………….
*Slm gsky zan daina yin tyaiping saboda rashin comment’s bazan iya zama some hours ina tyaipung nagama nayi posting amma ace bazakuyi comment ba idan har book d’in ne baimaku ba sainadaina amma wlh idan be’a comment zan daina musamman ku members na BRR ALEEYAH & MUHIBBAH Sam banaganin comment naku sosai wanda ko kune yakamata kufi kowa ma so idan angyara nacigaba idankuma bahaka ba hmm….. Kunsan k’arshen*
*℘ąɠɛ 90~95*
*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*
Sunji dad’i sosai da zuwanta, saida tai kwana biyu sannan takoma abuja,,,….
Yauce ranar da suka saka zasu had’u da iyayen *Aleeyah* nagaskiya dan haka tin dawuri suka shirya tsab suka wuce k’auyen marke tare da pastor David da matarsa, saikusan 12:30pm sannan sukazo,’….
Bayan sun gaisa ne suka fara abunda yakawosu, pastor David yafara magana “”nudai nine Wanda yatsinci yarinyar nan yabasu dikkanin labarin komai”” kuka sukaga tafara Tana zubarda kwallah wlh y’atace nice na’ahiyeta anan kanbishiya adaren da nahaufeta sanadin wasu dalilai,,,……
Cikin mamaki Abba yace kekuwa wane daliline zaisa kiyarda y’arki dakika haifa dakanki dikda tsananin k’aunarda ke tsakanin uwa da y’arta shin bakiyi tinanin irin halinda zatashiga ba watak’il ma tamutu sabida yinwa ko k’ishi,,,…..
Ahankali ta d’ago sannan tafara magana “zulaihat Abba Adam nicikakkiyar y’ar kasuwa ce nayi karatu ne ak’asar waje wato Oxford acan nahad’u da masoyina Ibrahim Mubarak’u sosai da juna harmuka yanke agawarar yin aure saidai ina tsoro mahaufina yakasance Mai zafin zuci Mai rsattsauran ra’ayi mu Fulani ne hakan yasa mahaufinmu baya aurardamu saiga Fulani, gashi nikuma inasan Ibrahim sosai nankawai muka yanke shawarar yin aure aganinmu shikad’aine mafita agaremu, bayan munyi aure da kimanin wata uku basamu ciki nanfa hankalina yatashi koda nafad’awa Ibrahim cewa yai azubar da cikin, nantake nanunamasa kin amuncewa ta mudai nemi wata mafitar, alokacin da cikina yakai wata shida ne muka kammala karatu sainadawo gida, bansan ya’akayi ba iyayena sukasan halinda nake ciki ba aranar nafuskanci mummunan ‘bacin rai agun magaifina Wanda ‘bata gani ba aranar mahaifina yakoreni daga gidansa cikin fushi sakuma ‘bacin rai, nayi kuka nayi bak’in ciki tareda nadamar abunda na’aikata kud’inda nazo dasu na k’asar waje su naje na canja shine nazo wannan k’auyen nasiye gida maid’aki d’aya da toilet anan nacigaba da rainen cikina har haihuwa tazo man cukin dare nahaifi y’a rashin sanin yanda zanyi da ita dakuma tina bak’in cikinda nake ciki dakuma rud’ar shaid’an yasa nayanke shawarar yarda ta, kuka yaci k’arfinta tai shuru nawasu yan mintina sannan tacigaba,,,……
Bayan nakaita kan bishiya na’ajiye ne nawuce abuja nahau jirgi nawuce Oxford gidan Antyn na Sam banyarda nasanar da ita abunda yafaru ba nantake nakira Ibrahim nanemi saki saboda bazan iya cigaba da zama dashi ba coz dik ta silar aurensa ne nashiga wannan matsalar Dakyar yasake, bayan faruwar haka da shekara d’aya nacigaba da karatu har Allah yahad’ani da alhj mustapha mukai aure, ahalin yanzu y’ay’an mu hud’u dashi yamallakamin tarin dukiya wacca bake kasuwanci da ita kuma muna matuk’ar k’aunar junanmu, amma wlh tinda nasake haihuwa y’ata tadawoman arai Abun haryafara damuna harma yadami mujina hakan yasa nadawo wannan k’auyen domin nemanta cikin sa’a kuwa ma mai gari yafad’aman labarinku nayi farinciki sosai,,,…….
Hmm!!!… Abba yanisa tabbas wannan Abun akwai al’ajabi to ahalin yanzu dai y’arki dai bazaki ganta ba saboda tana makaranta tareda y’ata a kebbi State sabida haka kiyi hak’uri saiki bamu address d’inki idan sundawo sai akaikami ita daganan saikikaita gun mahaifinta,’…..
Murmushi tai tareda goge kwallarda suka zubo mata cikin farinciki tace “nagode maku Sosai Allah yasaka maku da mafificin Alkhairi kunkulaman da y’ata cikin aminci, bakomai Allah yamaidasu lafiya yabasu sa’ar karatu,,,…
Suka amsa da ameeeen……!!!
Sunjima ak’auyen daga bisani suka wuce tareda kar’ban address d’in junansu,’……
*After 5months*
Su *Aleeyah* ankammala exam ta first semester sundawo gida cikin d’okin ganin yan’uwansu,,,…..
3days da dawowarsu *Aleeyah* aka shirya Masu zuwa gun mahaifiyarta kasancewar itama tana k’asar…………..
*yawan comments yawan tyaiping inba comments ba posting ehi*
*℘ąɠɛ 95~100*
*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*
3day’s da dawowar su *Aleeyah* aka shirya Masu zuwa gun magaifiyarta kasancewar itama tana k’asar,,,………
Sunshirya tsab cikin shiga mai kyau ita da jawahir kaya iri d’aya suka saka wata had’ad’d’iyar atamfa ce super wax light blue mai ratsin fari had’i da takakmansu farare saikuma mayafi shima fari, dik da bawani make up sukai ba amma hakan bai hana kyansu bayyana ba, Anwar shima ya shirya tsab coz tinda yaji zancen tafiyar yafara shiri shifa acewarsa baifa yarda *Aleeyah* tafita ba sai tare dashi,’…
Atare suka fito sai zuba k’anshi suke kamar wad’anda akayi ‘barin tirare ajikinsu, sabuwar motar Anwar dalleliya aciki suka shiga batareda wani ‘bata lokaci ba suka iso unguwar, basu wani wahala ba suka gane gidan kasancewar gateman yasan da zuwansu yasa yasa baitsaya yimasu tambaye tambaye ba ya bud’e Masu gate suka shiga, a inda ake parking Anwar yaje yai sannan suka fito, atare suke tafiya hanyarda zata sada su da cikin gidan suka bi saikuwa gasu a wani falo,, wasu kyawawan yara suka fara cin karo dasu su hud’u ne Mace d’aya da maza uku wasa suke abunsu kasancewar yau weekend ne, sallama sukai sai yaran suka dubosu macen ce ta taso Tana dariya tace masu sannunku da zuwa kuzo ku zauna abun mamaki yabawa Anwar ganin k’aramar yarinya da wannan kyakkawar tarbiyya haka,,,….
Zama sukayi sai yarinyar tafita cikin yan mintuna saigata ta dawo tare da wata kyakkawar mata mai kama da larabawa, Anwar na d’aga idansa ya kalleta yakuma kalli *Aleeyah* aransa yace tabbas kece mahaifiyar pretty na coz sak kamarsu d’aya zama kace yaya da k’anwa ne bcoz batayi tsufan da za’ace ita ta haifi *Aleeyah* ba, k’arasowa tai tareda zama sannan tanasu sallama cikin sakin fuska jin sallamar da *Aleeyah* tai yasa ta d’ago da kanta kallon kallo sukayiwa juna *Aleeyah* tafara magana hjy dama kece mahaufiyata…??,
Hmm…!!! ta nisa kwarai kuwa *Aleeyah* saidai nima bansan ke y’ata bace sai yanzu, murmushi *Aleeyah* tai tareda zubda kwallah sannan tace wannan dalilinne yasa nake mafarkinki juyowa tai ta kalli jawahir y’ar’uwa ta wannan itace nake mafarki acikin bacci na haba Ummi na meyasa kika yadani shin bakyasonane bakyatsoron abunda zai sameni alokacin da kika yadani haba ummi kowacce uwa burinta ta haihu tareni d’anta tabashi kulawa tareda tsintsar soyayyar uwa amma kekuma naki burin sai yasha banban danasauran iyayen menamaki ne dan Allah kuka ta fashe dashi, itama kuka take nan ta taso tadawo kusa da *Aleeyah* takama hannayenta tahad’a da nata sannan tafara magana “”dan Allah y’ata ki yafeman ki gafarceni wlh inasanki fiye da komai nawa alokacinda na yada ke inaganin kamar hakan shine mafita agareni zuciyata ta rufe namanta da k’aunar uwa da d’a sai bayan na aikata nakoma dana sani dan Allah kiyafeman”” ahankali ta d’ago ta kalleta cikin murmushi tace shikenan Allah ya yafe mana baki d’ai suka amsa da ameeen….!!,
Juyawa tai da fuskarta tafara magana “”hak’ik’a hjy hafsa ta tafka babban kuskure Wanda zata jima bata yafewa kanta ba, *Aleeyah* hjy hafsa mahaifiyarsu Aryan k’anwar mahaifinki ce carnal Ibrahim uwarsu d’ai ubansu d’ai itakad’ai ce mace acikinsu, ahannun mahaifinki tai karatu bayan tagama secondary school aka had’a ta da mahaifinsu Aryan aka Masu aure kasancewar auren zumunta ne da mahaifinsa da Nata ubansu d’aya, wasu mutane suna biyewa san zuciyarsu su aikata abunda sukeso sai daga baya kuma sukoma dana sani”” kallonta *Aleeyah* tai sannan tace Momy kidaina tina man rayuwata ta baya ni yanzu rauwata mai dad’i dazan shiga nake tinani yanzu bazama y’a kamar kowa sa’banin da danake baiwa nazama mai y’anci mai uwaye biyu da yayye uku had’i da k’anenne na Masu Kama dani murmushi sukai su duka jawahir tace kinmanta uwaye uku kegareki mami abba Momy da daddy saikuma pastor David da Momy Grace dariya sukai su duka,’..
Aranar dai dole Anwar yabarsu suka wuni badan yaso ba ko kad’an bayasan Nisa da ita ko asibiti yaje time by time yakira yaji lafiyar ta hakan yasa take k’ara k’aunarshi da T’ang uwansa baki d’ai, sun jima sosai agidan harsun fara sabawa da k’annenta mahaifiyarta kuwa ji take kamar ta maidata ciki tasake haifota saboda k’auna haka shima mijinta Doctor mustapha ji yake kamar shine mahaifin *Aleeyah* musamman yanda yaga shak’uwa ta shiga tsakanin ta da k’annenta Maryam wacca suke kira da Ami kasancewar sunan mahaifiyar sa ne sai twin’s Amir da ammar saikuma k’araminsu Ansar kyawawa ne suma kamar *Akeeyah* kamanninsu d’aya, sai kusan 5:15pm sannan Anwar yazo d’aukansu kayan cosmetics mahaifiyarta tabasu had’i da turaruka Masu tsada sannan suka Masu rakiya har gun mota suka shiga suka wuce,,,
1 week dazuwansu gidan mahaifiyarta ta shirya takai *Aleeyah* gidan mahaifinta soja ne Wanda ake ji dashi ak’asar nan, gida ne alfarma Wanda ya k’ar’bi sunansa gida sojoji ke tsaron kofar gidan dan haka suka hanasu shiga saida aka kirashi aka sanardashi sannan yace abarsu su shigo sannan aka barsu suka shiga, ganin hjy zulaihat agidansa yamatuk’ar bashi Mamaki, bata wani ‘bata lokaci ba tafad’amasa komai sannan ta nuna masa *Aleeyah* tace ga y’arka nan, ba k’aramin farinciki yai ba harda kwallah saida ya zubar bcoz matansa biyu anma tinda ya auresu ko ‘bari ba wadda ta ta’bayi gashi da tarin dukiya amma bak’in cikinsa shine rashin d’a kwatsam yau saigaahi yaga jininsa kuma Abun farinciki shine dik Wanda yaga *Aleeyah* yasan jininasa ce suna matuk’ar kama dikda tafi kama da magaifiyarta amma hakan baisa tarasa kama dashi ba,’..
Kwanan su *Aleeyah* uku ita da jawahir basu so sukwana ba amma dole tasa suka kwana dakansa yakai *Aleeyah* gidan iyayensa tareda masu kyakkawan bayani yanda zasu gamsu batareda sun zargesa ba, ssumasun nuna farinciki su Sosai sunjima suna addu’ar Allah yanuna Masu jinin d’ansu Ibrahim saigashi kuwa ya k’ar’bamasu ananma saisa suka wuni aikuwa *Aleeyah* tasha gata taga tsintsar k’aunar mahaifi da y’an uwa wacca tarasa a baya harma takejin kamar karsu rabu, haka suma matan dadynta suna nuna mata so, dazasu wuce kuwa tarin arziki yahad’ata dashi da kud’i Masu yawa sannan yasaka sojoji shida suka rakasu har gida tareda alk’awarin zaizo domin ganin inda take sannan yamasu godiya da irin kulawa da k’auna da suka nunawa *Aleeyah*,,,…..
Kwanansu biyar da dawowa suka koma school……………..
“`Allah sarki rayuwa mai sauyi wata rana asha zuma wata rana kuma asha mad’i BAYAN WUYA SAI DA’DI Allah ya sada mu da dad’in gobe k’iyama ameeen “`
*℘ąɠɛ 100~105*
*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*
Kwanansu biyar da dawowa suka koma school,,,…..
Ahalin yanzu zuciyar *Akeeyah* cike take da farinciki ta ko’ina yanzu y’argata ce time by time dadynta yana zuwa kaimata ziyara haka ma momynta kuma dik wanda yaje da provition Mai tsoka yake zuwa, yanzu kam alhmdllh rayuwa natafiyar mata yanda takeso, yanzukam karatu suka saka agaba dan ganin sunfito da result Mai kyau,’….
“`AFTER 4 MONTHS“`
Su *Aleeyah* andawo gida hutun second semester yanzu kam hadda kawai Sukeyi agun Mami saikuma dan karatu kada amanta abunda aka iya,,,….
Zaune take ita kad’ai acikin lambu Tana shan iska karatu takeyi da’alamu, sallama taji daga gefenta “”amincin Allah ya tabbata agareki yake sarauniyar kyawawa “” d’agowa tai sannan tasakar masa wani k’ayataccen murmushi tace tare dakai yayana barka da Zuwa, zama yai yana fuskantarta cikin Fara’a dakuma sakin fuska karatu ake pretty “Eh” tace dashi dakyau,,,….
Shuru yad’an ratsa wajen nawasu mintina saikukan tsintsiye kakeji can dai yayi gyaran murya “pretty bani Aron hankalinki nan please” d’agowa tai tana kallonsa,, *Aleeyah* yau inaso nasanar dake ask’on da zuciyata tadad’e tana aikoni amma bakina yakasa furta maki *Aleeyah* ina sanki ina k’aunarki da dukkanin zuciyata Kai harma da gangar jikina, please pretty karkice bakyasona dan Allah, ‘….
Shuru tai batace dashi komai ba, *Aleeyah* yakira sunanta d’agowar da zatai kawai taganshi durk’ushe agabanta k’afarsa d’aya akasa d’aya kuma a durkushe, kallonta yake hannunsa rike da wata cover da’alamu dai ta zobe ce sannan yasake cemata “”pretty will you marry me”” zura masa ido tai cikin mamaki dakyar ta’iya cemasa “”yes I will”” yalwataccen murmushi yasakar mata sannan yajanyo hannunta yasaka mata zobe sannan itama tasaka masa, wani kallo yamata tareda kashe mata ido d’aya kunya taji takamata tai saurin rufe idonta da duka hannayenta biyu, ji yai tak’ara Shiga ransa kamar ya rungumeta saidai ba Hali,,,….
Soyayya shak’uwa had’e da k’aune ce kegudana tsakanin *Aleeyah* Anwar hartakai ga iyayensu suka sani, bak’aramin dad’i hakan yamasu ba nan take Anwar yabuk’aci amasu engagement, ganin suna k’aunar junansu yasa Abba baiwani damu ba yasanar da dadyn *Aleeyah* dama dik wani Wanda keda hak’k’in yasani, nan take Abba yasanya ranarda za’ayi engagement d’in ranar kuwa takasance ranar weekend ne saboda so yake kowa yahalarci engagement d’in,’…
Hmm…..zo kuga ikon Allah taron engagement kamar na d’aurin aure ko’ina sojoji ne sunzagaye gidan saboda tsaro,’..
A babban falon Abba aka gudanarda komai anci ansha daga bisani kowa ya watse, ranar kuwa Anwar kwana yai dafarinciki hakama *Aleeyah* dikda tanada kunya sosai amma hakan baihana murnarta bayyana ba jawahir da hanifa sai tsokanarta sukeyi kasancewar hanifa ma tazo tareda Abban ta, nan suka had’e sai farinciki suke,,,….
Angama hidimar biki kowa ya watse hanifa ma sunkoma su *Aleeyah* kuma hutunsu yak’are dan haka suma sunkoma school, rayuwa mai sauyi ahalin yanzu rayuwar *Aleeyah* cike take da farinciki babu abunda ke damunta karatu kawai suka saka a gaba, soyayya kuwa tsakanin ta Anwar sai dad’a bunk’asa takeyi suna matuk’ar k’aunar junansu itadai jawahir tazama y’ar kallo,,,…
“`AFTER 7 YEARS“`
Zaune take acikin katafaren gidanta Wanda mahaifinta yagina mata kuma yamallaka mata sanye take da wata tsadaddiyar rigar material red colour glass ne a idanunta tana danne dannen laptop, sallama akayi aka shigo cikin girmamawa da tsintsar ladabi yace “”hjy barka da hutawa ga wata mata nan tazo tace tanaso taganki”” d’agowa tai ta kallesa sannan tace Mlm Mani menafad’a maka banace dik Wanda yazo kucemasa banananba saboda kawai nahuta fa nazo nan haba dan Allah kubarni nahuta mana dame zanji tarin ayyukan dake gabana kokuma koke koken mutane,’..
“”Allah ya huci zuciyarki hjy wlh matarce bataji yau kwananta uku kenan tana zuwa nemanki yaudai tadamemu da magiya shine nace bara nazo nasanardake “”,..
Hmm….!!! Shikenan ganinan zuwa, saida takusa 30minutes sannan tafita tafiya take irinta hamshak’an mata masu ji da kyau kud’i dakuma gayu tamkar mai tausayin k’asa, tin da tafuto Masu aiki kegaidata har isa bakin gate dasauri gateman yabud’e mata k’ofa ta fita,’…
Dumm….!!! taji gabanta yafad’i aranta tace wazan gani haka…………
Hmm tabbas akwai cakwakwiya
*℘ąɠɛ 110~115*
*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*
*Aleeyah* da jawahir ne acikin lambu suna hutawa kasancewar yau weekend ne ba aiki, kwatsam saiga Anwar tareda Aryan kallon kallo sukai aka rasa mayiwa wani magana acikinsu, kawai sai Aryan yajuya zaiwuce Anwar yarik’o hannunsa batareda yace dashi komai ba yanemi ya janye hannun, Anwar yace d’anuwana kadaure katsaya dan Allah akwai maganarda nakeso muyi shiyasa nace MA muzo nan, badan yaso ba yatsaya batareda yajuyo ba,’….
Anwar yafara magana dafarko dai ina mai baku hak’uri dukanku musamman Kai ya nuna Aryan, nazauna nayi nazari tareda karatun tanutsu naga cewa tabbas idan har na aureki *Aleeyah* tabbas naci amana kuma idan narabaku to zan iya raba d’a da mahaifiyarsa, inaso kisani *Aleeyah* nadad’e dasanin kinasan Aryan sannan shima nasan yana matuk’ar k’aunarki, yau kimanin shekara takwas kenan Aryan yana dakon sonki ina riba agurina ace naraba soyayyarda aka ginata shekara da shekaru miye ribata aciki, ahankali yamatsa kusa da *Aleeyah* yakalleta sannan yace inarok’on alfarma agunki da darajar sonda kikeman ki tattarashi kik’ara akan wanda kikeyiwa d’anuwana sannan dan Allah dan Allah *Aleeyah* kiyafewa umma da Abdullah abunda suka maki,’…
Ahankali ta d’ago jajayen idanunta dasuka kad’a suka canja launi tace “”hak’ik’a samun y’anuwa kamarku awannan zamani abune mai wahala dakyar asami namijinda zai iya barwa wani matarda shima yakeso kuma harda alk’awarin aure atsakaninsu tabbas Anwar kacika jarumi kuma insha Allah zakaga haske arayuwarka kuma zakaga kyakkawan sakamako na ceton zuciyoyi biyu, tahakan zansamu damar sakamaka da abunda ka rok’eni, hmm….!!! tanisa shikenan Anwar nayafemasu Allah ya yafemana bakid’ai””,,,…..
Cikin murna suka kar’ba da ameeeen……!!!!
Ahankali yajuyo ya Kalli Aryan yace d’anuwana kamin afuwa rashin sanine yasaka harnayi burin auren abark’aunarka amma yanzukam najanye wlh nabarma *Aleeyah* har abada saboda kaikafi cancanta dakazamo mijinta, saboda tsananin farinciki Aryan ba baki kawai rungume Anwar yai hakama *Akeeyah* ta rungume jawahir tana zubda kwallan farinciki, Aryan yace “”hak’ik’a Anwar kai d’anuwa ne Wanda yakeda wahalar samun irinsa awannan zamani kamin abunda bansan dame zan saka maka ba, Anwar nagode sosai kaima Allah yamaka za’bi mafi alkhairi arayuwarka”” cikin dariya jawahir tace ameen yamayi yanzu haka Abban Abdullah suna yola adamawa wajen nemamasa auren hanifa kuma har anbada, cikin mamaki *Aleeyah* ta kalleta jawahir tai dariya tace kinyi mamaki koh su Abba harma da mami diksunsani kune kad’ai baku saniba, dariya *Aleeyah* tai harsaida fararen hak’oranta suka bayyana atare suka wuce zuwa cikin gida sai farinciki sukeyi da nishad’i,,,..
Yau saura kwana 2days afara hidimar biki tini mami tasaka akazo da shahararrun mata Masu gyaran amare guda biyu daga kebbi aikwa nansuka saka *Aleeyah* do jawahir agaba da gyara cikin k’ank’anen lokaci fatarsu ta Sauya ga laushi kamar fatar jinjirai ga sentsi sudakansu sunsan Sun sauya, dilka da kurkur halawa hayak’i turaren tsuguno sihirtattun mayuka na shafawa tareda had’in sabulun wanka, jik’ejik’e da shaye shaye dikbawanda ba’amasu har *Aleeyah* tafara gajiya dazaran tasan lokacin sha yayi saitagudu gidan Anty Mimi gidan momynta idan taje canma bata tsira ba dan itama tana bata nata had’ehad’en shiyasa bata zuwa can,’…
Yauma dai kamar kullum kwance suke a falon Abba saiga mami tazo da had’ad’d’iyar kazar hausa wacca akamasu nanfa *Aleeyah* tafara murzar ido zuwa kuka “”mami dan Allah kiyi hak’uri wlh nak’oshi “” ko kallonta mami batayiba ta mik’amata tace taci dole ba halin gardama tafara cusa ta ammafa hawaye sunyi banza kam zubowa suke kamar pampo jawahir sai kyalkyala dariya take saiga Anwar yashigo ganin prettyn shi nakuka yasashi saurin zowa “pretty meke faruwa ne waya ta’baki y’ar abbanta” shuru tai takasa cewa komai juyowarda zaiyi saiyaga mami tana hararansa ai ba shiri yajuya zuwa cikin gida jawahir kuwa kamar cikinta ya fashe dan dariya, ‘…
******* *******
Anfar gudanarda shagalin bikin Manya kuma y’ay’an Manya, y’ay’an Manya shahararrun Doctor’s Manya shahararrun y’an kasuwa kuma Manya sojojin da ake ji dasu afad’in Nigeria bikin da yazagaye dik kasar Nigeria Manyasauka Manyan bak’i sai Sauka sukeyi daga k’asashe daban daban, kyaututtuka kuwa saisamunsu sukeyi, Pastor David yabama *Aleeyah* kyautar dalleliyar mota sabuwa gal da k’arin kud’in saka mai sannan dik motocinta dayake mata kyauta ranar birthday dika yad’aukosu yakawo tayi masa godiya sosai hakama dadynta yaji dad’i shima,’….
Ankawo lefen *Aleeyah* wanda dika Anty Mimi ce tahad’oshi daga k’asar Dubai, lefene nagani na fad’a babuce kawai babu aciki komai yayi set d’in akwatayya biyar, su hanifa an iso jawahir da *Aleeyah* sai tsokanarta sukeyi matar yaya matar brother haka suke kiranta yanzu,,,…
Anfara gudanarda shagalin biki jiya akayi kamu yau akayi dinner gobe za’ayi k’ayatacciyar walima wacca mami tahad’a da marance bayan and’aura aure daganan kuma sai akai amare gidajensu,,,….
Around 1:30am *Aleeyah* nakwance akan gado tad’ora kanta akan cinyar hanifa dawowarsu kenan daga dinner sungaji sosai kawai saitaji wayarta tai k’ara tana dubawa taga my husband kamar kartad’aga kuma dai sai tad’aga, “”kizo d’akin Anwar kisameni ina jiranki”” baijira tai magana ba kawai yakashe wayar wani uban tsaki tadaka batareda tace komai ba, hanifa ta kalleta tace to uwar tsaki ke da waye kuma…?? Aryan ne wainazo yanzu jawahir tai dariya aa kice angon ne to aje ajikiran maigida ttafad’a cikin tsokana, duka takai mata ta kauce tana dariya, tsauka tai daga gadon tasaka hijab kasancewar rigan bacci ce ajikinta tasaka takalma sannan ta fita,’….
Salaams tai tareda bud’e k’ofar tashiga ahankali, kwance yake shikad’ai akan gado sannan yatashi cikin sakin fuska yace bismillah zo kizauna uwargida ran gida kuma sarautar mata, k’arasawa tai tazauna nesa dashi bcoz atsorace take karwani yashigi yaganta ya lura da hakan amma ko ajikinsa matsowa yai gab da ita ahankali ya rungumeta yana shak’ar kamshin sihirtattun tirarukan da momynta tahad’amasu cikin k’ank’anen lokaci Aryan yafara zaucewa tini yaciremata hijab aik’ara rikicewa yai lokacinda yafara ganin surarta wani mayen kallo yake mata ahankali yana lumshe idanunsa, tsoro yagama mamaye *Aleeyah* jin k’arar bud’ar k’ofa yadawo dashi duniyar da yaje dasauri ta tashi tasaka hijab zata wuce yarik’e hannunta, Anwar ne yashigo yanaganinta yai murmushi yace aa amarya kinsha k’amshi amarsu ta ango, wata iriyar kunya taji takamata dasauri ta fige hannunta ta gaida Anwar tawuce dasauri tana rufe fuskarta, dariya Anwar yadinga kyalkyalawa ya kalli Aryan cikin tsokana yace haba ango bazaka jira ashafa fatiha ba da’alamu dai wannan angon ba sassauci agunsa,murmushi yai yanashafa kansa Anwar yace bro dan Allah karka wahalarman da k’anwa, hararansa yai yace idan akayi naku karka Ta’ba hanifa harsai ta shekara d’aya kai uban masu tausayi Me Anwar zaiyi inba dariya nan yaita kyalkyalata saida Aryan yakoreshi yai d’akin mami,’…
Around 10:00am aka d’aura auren *Aleeyah* da Aryan, jawahir da Abdu – Hakim, Ahmad da khairat gagarumin d’aurin auren da yasamu halartar manya yayan Manya dakuma su kansu manyan farar fata dama bak’ar fatar daga k’asashe daban daban…………
*℘ąɠɛ 115~120*
*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*
Around 10:00am aka d’aura auren *Aleeyah* da Aryan,Jawahir da Abdul-hakim, Ahmad da khairat, gagarumin d’aurin auren da yasamu halartar yayan manya dama su kansu manyan farar fata da bak’ar fata daga k’asashe daban daban,,,…..
Taro ne akayi wanda yabawa kowa mamaki saidai agun Masu taron ba mamaki, manyan abokanan su Abba na gun aiki dakuma abokan business d’insu dik sunzo hakama nasu Aryan suma sunzo, a can nahango Anwar da Aryan tamkar tagwayen asali Kaya iri d’aya suka saka shadda fara babbar rigar ta sama taji aiki sosai sai takalma bak’ak’e da Hula bak’a Mai zanen fari ajikinta sunyi kyau matuk’a Aryan saifaman washe baki yake suna gaisa da mutane,’….
Bayan angama d’aura aure Abban Ahmad yashirya masu k’asaitacciyar walima yayinda shikuma Anwar ya shirya masu liyafa ta musamman awani katafaren hol, naira ce ake kashi tamkar ba’asan zafinta ba ko abincin wajen liyafar kazuba da kanka ne kuma saiwanda ranka yake so,’…
Agun amare kuwa mami tasaka anca’ba Masu ado dawani had’ad’d’en material pink colour sannan suka d’ora abaya bak’a akai sunyi matukar kyau ainun, nan mami tashirya masu k’ayatacciyar walima wacca tasamu halartar shahararrun mata Masu ji da sunnah, nasihohi akayi Masu ratsa zuciya akan zaman aure daga bisani kuma mami tarufe taro da addu’ah, 4:30pm aka wuce da jawahir zuwa kebbi kasancewar ita a can zasu fara zama kamin suwuce honeymoon, dakyar aka raba jawahir da *aleeyah* sai kuka sukeyi na rabuwa da juna bayan anwuce da ita mami tasaka driver da Anty Mimi sukai *Aleeyah* gidan y’anuwanta da iyayenta,,,….
Gidan kakanninta suka fara sannan suka wuce gidan dadynta nasihohi yamata masu ratsa zuciyar maisauraro akan zaman aure dagabisani yarakosu har gun mota tana jikinshi sai shar’ban kuka take nan yabud’e marfin mota tashiga yajanyo hannunta yasakamata tiraren [ ALMISKI ] sannan yaduk’o daidai kunnenta yace mata ‘yata gashinan kiyi amfani dashi idan kinje gidan mijinki, ahankali ta d’ago da jajayen idanunta takalleshi nan tarungumeshi tana kuka ahankali ya janyeta bcoz bazai iya jure kukanta ba zata iyasakashi shima yayi, nan ya rufe marfin driver yatada suka wuce, daganan kuma suka wuce gidan momynta itanadai hud’ubar tamata irin tamu ta iyaye mata sannan tabata had’ad’d’un tiraruka da humra mai k’amshin gaske daga bisani suka wuce gida,’….
Around 9:15pm mami tace Anty Mimi tasakewa *Aleeyah* shiri aikwa nan ta sake ca’ba mata wani sabon adon cikin wata had’ad’d’iyar super exclusive light blue mai ratsin fari da mayafi shima fari da takalamanta platshue nan ta fesheta da sihirtattun tiraruka Masu shegen k’amshi mai d’aukar hankalin Wanda yajisa,bayan tagama shiryata suka wuce falon Abba nan abba da Mami suka sakata a gaba da hud’uba akan rayuwarda zata shiga wato rayuwar aure sund’auki lokaci suna mata nasiha daga bisani aka fito da ita zuwa gidanta,’….
Abba yahana kowa zuwa kai amarya daga shi sai mami sai amarya mami tai tai yabari koda hanifa ce taje kodon siyan baki irin wanda ‘yammata keyi amma yahana yace ga motoci nan ga drivers gobe dik maisan zuwa akaishi amma dai yanzukam yahana dole badan tasoba takyale, wata dalleyir motarsa suka shiga aciki cikin k’ank’anen lokaci suka iso,,,…
“`k’alubale gaareku iyaye maza sunnah ce ta manzon tsira uba yaraka ‘yarsa da kansa zuwa gidanta na aure, manzo Allah [ S.A.W] yakasance idan ya aurarda ‘ya’yansa yakan rakasu da kanshi zuwa gidan aurensu tareda nasihohi Masu ratsa zuciya sannan yakan d’auki lokaci mai tsayi yana masu addu’ah ta neman zaman lfiya da mazajensu, Allah yabamu ikon koyi da da bin sunnar annabinmu ameeen“`
Kasancewar gateman yasan da zuwansu yasa yai saurin bud’emasu suka shiga yai parking sannan suka fito mami na rik’e da *Aleeyah* wacca fuskarta ke lullu’be da mayafi, ciki suka wuce suna isa falo Abba yatsaya mami tawuce da ita k’urya, abakin gado ta zaunarda ita tad’an k’ara mata jankunne sannan tafito, suna fitowa mami ta kira Anwar tace dan Allah suyi sauri suzo anbar *Aleeyah* ita kad’ai,’…
Fitarsu da 30minute’s su Anwar suka iso cikin motar Aryan nansuka fito suka gaisa da baba Mai gadi sannan suka wuce cikin gida suna raha da barkwanci irin na abokanan ango, su uku ne Aryan da Faruk abokinsa sai Anwar suna isa falo Aryan yace “”to alhmdllh malamai konace gwauraye saidasafe koh yafad’a yana murmushi “” hararansa Anwar yai yace what do you mean ai kayi kad’an fa wato tinda munrakoka shine zaka kiremu koh, Faruk yace barshi kawai tinbaiko Fara cin amarci ba zaifara korarmu, dariya Aryan ya kyalkyake da ita sannan yace kwadaije kuji da gwauranci kunga ni zanshige Madam najirana yafad’a yana dariya, Anwar ma dariya yai yamik’a masa ledarda suka shigo da ita yace ango saidasafe asha amarci lafiya faruk yace adaiyi ahankali kar akarye mana gado gobe muzo jinya sukai dariya sannan suka wuce yarufe k’ofar yawuce ciki,,,….
Dashigarsa d’akin daddad’an k’amshi yafara tarban hancinsa harsaida ya lumshe idanunsa, zaune take fuskarta rufe da mayafi wani k’ayataccen murmushin farin ciki yayi sannan yak’arasa inda take ya zauna ya ajiye ledarda yashigo da ita sannan ya Kalle ta sallama yafara mata sannan yafara magana “”Alhmdllh dikkanun yabo da godiya su k’ara tabbata ga mahaliccin sammai da k’assai wanda ya nuna mana wannan rana ta farinciki agaremu babu abunda zamu cemasa saigodiya agareshi, *Aleeyah* yau Allah yacika man burina yanuna man mafarkina a fili yau kinzama matata mallakina inarokon Allah dayatayani rikon amanarki kema kuma ina fatar zaki Man biyayyar aure Allah yabamu hak’urin zama da juna ameen “” jin tayi shuru batace komai ba yasan kunya ce ahankali yaduk’o daidai kunnenta yace amaryata to bud’e fuskar mana ko saina biya ne, maganarsa dariya ta bata harsaida tad’an murmusa amma bata bud’e fuskarba ganin haka yasa ya’be dakansa “Masha Allah yafad’a tsarki ya tabbata ga mahaliccin wannan kyakkawar surar ” murmushi tai batareda tace komai ba, ahankali yakai hannunsa ya rik’o nata yana kallon lallenta nan yakai bakinshi ya sumbaci lallen sannan ya tashi ya cire babbar rigarsa da hula yace muje mud’auro alwala ko nanma dai batace dashi komai ba baijirataba yawuce yayo yafito bayan yafito sannan tashiga itama tai ta fito, sallah sukai raka’a biyu sannan suka sallame nan yadinga kwararo masu addu’oi ganin tagaji hartafara gyangyad’i yasa yatsaya hakanan suka shafa nan yad’ora hannunsa a goshinta yamata addu’ah sannan yajanyo ledarda yashigo da ita gasasshiyar kaza ce da freshmilk nan yabud’e yace *Aleeyah* taci tace tak’oshi bazata ci ba yai yai taci tak’ici “”itafa adole hanifa tace mata idan taci kazarnan to tabbas saiya kwana da ita shine fa tace bazata ci ba hmm Lol “” kyaleta yai yaci abarsa saida ya k’oshi sannan yakai sauran kitchen yadawo,’…
Wardrobe d’inta ya bud’e yaciro mata wata arniyar night gown yasha kunu yamik’a mata “”tashi kiyi wanka kisaka mukwanta”” gabanta ya fad’i damm amma ta dake ta kar’ba tawuce toilet, tana shiga shima yafita izuwa nasa d’akin,’…
Wanka tai tafito ta shafa mai tai tsaye tana kallon rigarda yabata yace tasaka ita da babu dika d’ai nandai tasaka underwear d’inta tai tsaye tarasa yanda zatayi tak’ara d’aga rigar Tana k’are mata kallo jinshigowarsa yasa tai saurin juyowa tareda ‘boye rigar abayanta, tsaye yai yana kallonta aranshi yace wannan yarinyar kinma rainani wallahi nanyak’araso fuskarsa babu alamun wasa yasha kunu sosai ganin haka yafirgitata tai saurin ja da baya hannunsa yakai yacire tawel d’inda ke ajikinta da sauri ta yarda rigar ak’asa ta rufe fuskarta, tsaye yai yakasa koda motsawa idanunsa ko kiftawa basayi wani mayen kallo yakewa kyakkawar surarta tidin bobss d’inta yafi k’arfin bz d’inta hakan yasa bata rufesu ba gabad’aya rabi naciki rabi kuma a waje,,,….
Ai saboda shauk’i baisan lokacin da yarungumeta ba yamanneta da k’irjinshi, jin tidin bobss d’inta a jikinshi yak’ara rikitashi da rud’ashi kawai yad’auketa cakk……………
Sai gidana 😃😉🙈 Malam Aryan ka manta da night gown fa ko anbarwa MA čheřii ta maiunguwa ne 🤣😍
*℘ąɠɛ 120~125*
*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*
Ai saboda shauk’i baisan lokacin da yarungumeta ba Ya manneta da k’irjinshi, jin tidin bobss d’inta ajikinshi yak’ara rikitashi da rud’ashi kawai yad’auketa cakk sai kan gado,’…
Ahankali yafara shafarta hannunsa yakasa tsayuwa waje d’aya sai shafarta yake, tsoro da fargaba ne suka mamaye zuciyar *Aleeyah* dakuma rashin sanin abunda zai faru, hannunsa taji kan bobss d’inta yana matsasu tareda bz d’inta atsorace ta yunk’ura zata mik’e saitaji takasa hmm inafa zaki iya malama *Aleeyah* k’arfi ba d’ai ba, matsarsu yake sonranshi Yayinda takejin zafi sosai dak’arfi tace “”ya Aryan miye haka dan Allah ka kyaleni mana nifa ba ‘yar iska bace wallah wannan ai iskanci ne “” dikda yanayin da yake ciki amma saida yad’an murmusa dariya maganarta tabashi yace dakyar ya d’ago daidai kunnenta yace “”yace nima *Aleeyah* ba d’an iska bane lalura ce”” ba ruwana nidai ka Kyal….. bata k’arasa ba yahad’e bakinsu gu d’aya nankajita shuu, harshensa yadinga sawa yana tsotsar yawunta nan yahad’e harshensa da nata yana tsotsa yayinda hannunsa ke murzar bobss d’inta, ahankali yakai hannayensa yacire bz d’inta tareda pant d’inta nanyasauko da bakinsa gun cibiyarta yara kissing Nata kissing d’inta yake ta ko’ina yayinda hannunsa kuma yake kan bobss d’inta yana murzarsu San ransa, ahankali yafara tsktsarsu tamkar wanda yasamu sweet, uhm su *Aleeyah* ba baki saima gantsaro masa bobss d’in take da’alamu dai sak’onnin Aryan na isarmata shikwa dama abunda yakeso kenan, bobss d’inta sunfi komai birgeshi bcoz shi yafisan Mace mai bobss sosai saigashi kuma yasamu hhhh Lol,,,…
Tsotsar bobss d’inta yake tamkar mai tsotsar lollipop tini *Aleeyah* tariga da tabada gari danhaka bori kawai yacigaba da hawa, dakyar Aryan yai addu’ar saduwa da iyali nan yafara kiciniyar shigarta amma ina ba hanya wurin a rufe yake gamm, kok’ari yake yagadai yashigeta amma ina, nanfa *Aleeyah* tafara kuka bcoz zafi takeji sosai kok’arin shigarta yake itakuma kuka take masa na zafi dakyar yasamu hanya ammafa *Aleeyah* tasha wuya kwallah harda majina da wuya tai wuya nantafa kiran sunayen ubangiji
Tabd *Aleeyah* lallai kinsha wuya 🤣🙈
Kyla take tana kiran sunansa “”Aryan dan Allah kayi hakuri wlh mutuwa zanyi zan mutu nagaji bazan iyaba dan Allah ka kyaleni “” hmm ina ko jinta bayayi balle ya saurareta yayi nisa yafad’a tsundum acikin babban birnin masoya acikin makeken tafkin kogin k’auna da zazzak’ar madara had’e da zumar *Aleeyah*, danhaka bayajin kira haka taita magiya hartagaji tai shuru kwallah kawai kefita a idanunta shikwa yana kan aikinsa, dakyar yasamu yai releasing sannan yasauka akanta yana kallon fuskarta wacca tai Face face da hawaye idanunta na rufe, wani k’ayataccen murmushi yai na farinciki nan yatashi a zaune yana kallon kyakkawar surarta tindaga k’asa haryazo kan bobss d’inta wata sabuwar sha’awar tsotsarsu yaji bcoz bobss d’inta irin wad’anda be’agajiya da tsotsarsu ne kan jajir yake na shanun kuma fari tass abunka da farin mutum kuma bafulatani, 😍 kawai yadawo kanta, ahanka taji hannunta kansu,,,…
Oh my God 😨second round nawawoo *Aleeyah* you name is sorry woo 😍
Ahankali yad’ora bakinshi a kan yafara tsotsa gaya wani masifar zafi takejin suna mata amma bahalin tahanasa ahaka har yasake biyan buk’atarsa sannan yakyaleta, blanket yajawo yalullu’besu sai sanya mata albarka yake har bacci yad’aukesu,’..
5:15am yafarka ahankali ya janye jikinsa daga nata yawuce toilet yai wanka tareda d’auro alwala sannan yafito, jallabiyya yasaka bak’a nanyafara sallahr nafila yana mik’a godiyarsa ga ubangiji tareda addu’ar samun ‘ya’ya nagari bayan ya gama baitashi ba harsaida yai sallar asuba sannan yatashi, nan yagyara mata kwanciyarta kitchen yawuce yahad’a Masu breakfast a dining sannan yadawo d’akin, tafarka idanunta a bud’e amma takasa tashi yana shigowa tai saurin rufe idanunta batasan yaganta ba dariya yai yawuce toilet yahad’a mata ruwan dumi masu zafi sannan yasaka dettol aciki tareda wasu magunguna sannan yafito,,,…
Kan gadon yahau yaduk’o daidai kunnenta yace “”good morning my Queen hope kintashi lafiya”” k’ara rufe idanunta tai tak’i yin magana murmushi yai nan ya yaye blanket d’inda ke rufe da jikinta sannan ya sauko yad’auketa sai toilet, cikin ruwan yasakata ai saboda masifar azabar zafinda taji mara misaltuwa dak’arfi tabuga k’ara tarirrik’eshi jikinta sai rawa yake tana kuka zafi zafi zafitakeji tausayinta ya kama Aryan haka ya dake yazaunarda ita cikinsu bcoz hakan shikad’aine mafita, ahankali tafara jindad’in ruwan ta zauna dakyau fuskarta a rufe nan ya zage dantse yawanke mata jikinta tass harda gun wato inda yai operation d’in nanma saida yasaka ruwan d’umi yawankeshi tass, kunya tagama mamaye *Aleeyah* takasa bud’e idanunta haryanzu tini yaganota shikwa baidamu ba nanfa yai tsaye yace saitayi wankan tsarki agabanshi dole ba yanda ta’iya tai shi acewarshi wai koda akawai inda take da kure saiya gyaramata hmm Lol,’…
Bayan tagama yad’aura mata towel ya d’auko abarsa suka fito, dakansa yashiryata ita kuwa sai nok’e fuska takeyi haryanzu tak’i barin su had’a ido dashi, bayan ya shiryata tsabb sannan tai sallah amma a zaune bcoz bazata tsayuwa ba azaune tai hartak’arasa sannan yarik’ata sukawuce dining, nanma dai dakansa yabata abincin batawani ci dayawa ba saboda batajin dad’i ganin haka yasa yamaidata d’aki,,,…
suna Shiga ta kwanta karkarwar sanyi tafara nantake zazza’bi mai k’arfi ya rufeta aikwa ba shiri Aryan yakira Anwar shima bai’bata lokaci ba yazo, injection yamata sannan yabata magani aikwa nan Anwar yadinga kyalkyaka masa dariya yana tsokanarsa saida ya koresa,,,…
12:00pm Anwar ya kawo hanifa da Anty Mimi koda sukazo alhmdllh tasamu sauk’i harma ta tashi saidai haryanzu tafiyarta idan ka kula da kyau ba daidai takeyiba hhhh taji maza aidole ta sauya
Hanan yasa take d’an Hard’e k’afafunta kar Anty Mimi tagane hmm batasan tini tagano ba Lol, sund’an jima daga bisani sukabawa maigida gidansa yacigaba da jinya,’…
Kwanansu uku sukaje bankwana zasu wuce honeymoon, saida sukaje ko’ina sannan suka dawo gidansu Aryan, Ummu sai kunyar had’a ido take da *Aleeyah* ganin haka yasa *Aleeyah* tasaki jiki tana shiga cikin Jilin umma hartasaki jiki da ita tamkar wani Abu baita’ba faruwa ba atsakaninsu Abdallah ma yarok’eta gafara tace ai tini ta Manta da komai yanzukam acigaba da zumunci kawai, anan ta wuni sai dare sannan yazo yad’auketa suka wuce,,,…
suna isa gida kowa yawuce d’akinsa bcoz tin a first night d’insu yakyaleta ganin irin wahalarda tasha gaya shikuma tin da ya d’and’ani zumarta bazai iya jure kasancewa da ita batareda ya kusancetaba shiyasa kawai yake kwana a d’akinsa hartak’ara warwarewa,,,….
9:30am Anwar dasu Abba suka raka Aryan da *Aleeyah* air port……………