Bawa na Hausa Novel Oum Hairan
Tag: BAWA NA!
OUM HAIRAN
PAGE 1-2
Zamani ke tafiyar da yanayi, yanayi kuma ke shuɗawa da Lokaci, Masarautar Yamlash babbar masarauta ce me ƙarfin faɗa aji da ƙarfin mulki gami da jin izzar sarauta, wanda a wannan ƙarni babu wata masarauta da take taka rawarta yanda takeso kamar wannan masarauta.
Al’ummar dake rayuwa a birnin Yamlash sun kasance ma’abota bautar rana ne ita suka É—auka abar dogaronsu sun bada gaskiya da ita sannan sun yarda komai baya faruwa Saida lamuncewar Rana.
Farfajiyar gidan sarautar cike yake maƙil da mutane barori bayi da kuyangi gabaɗayansu sun tattare a guri guda, kowannensu ka gani fuskarsa cike take da fargaba zullumi da tsoron da yake bayyana asalin halin da suke ciki.
Daidai wannan lokacin ne aka buga tambarin daya kaɗa zuciyar kowanne mahaluki dake wanzuwa a wannan farfajiya, cikin amon murya me amsa kuwwa zagin fada ya fara gabatar da shelarsa da take ƙara shigar da kowa hankalinsa faɗi yake.
“Yekuwa jama’ar masarautar Yamlash maza da mata manya da yara tsoho da tsohuwa bawa da baiwa! kuyi sani Gimbiya Samha tana gab da fitowa, tabada sanarwar bata buÆ™atar kowa cikin wannan fada ya kasance cikin yanayin dariya tanason taga fuskar kowa a murtuke kamar an aiko da sakon mutuwar ubanninku saÉ“awa wannan doka daidai yake da siyawa kanka wulaÆ™ancin da bazakaso ko a labari kaji anyiwa wani irinsa ba, in kunne yaji ita gangar jiki zata zauna lafiya…..”
Sosai mutane suka ƙara shiga hankalinsu don sun riga sun sani saɓawa wannan umarni daidai yake da taro guguwar ajalinka, tsayin lokaci me tsaho bayin suka ɗauka shanye a rana sai zufa sukeyi kowanne da irin nasa cin maganin abin sai wanda yagani.
Can saitin busar sarewa ya fara tashi da amo me daÉ—in sauraro daidai lokacin ne kuma wasu yammata kyawawa guda arba’in suka fito a jere tsakiyarsu kuma wata kyakkyawar halitta siririyar budurwa ce wacce kyawunta ya zarce tsayawa fasaltawa saidai gani da ido, sanye take da wani bakin yadin siliki É—inkin doguwar riga da taci ado da duwatsu masu babbar daraja, rigar tana sharar Æ™asa waÉ—annan kuyangi arba’in na hagu da dama suna naÉ—ewa tare da karkaÉ—ewa.
Cilla ƙafarta takeyi saman shimfiɗar dardumar da akayi wa inda zata taka wata ƙara na tashi ta haɗuwar sarƙoƙin adon dake ɗaure a sangalalin ƙafarta, saman kanta anyi mata rumfa da wani yadi me kauri da ƙyalƙyali da haka suka rinƙa takawa har suka iso tsakiyar gidan sarautar inda bayin nan ke tsaye ƙiƙam a rana, daidai kuma lokacin ne wani bawa ya kutso cikin taron ya nemi guri ya tsaya shima amma saɓanin sauran bayin shi fuskarsa a naɗe take da wani farin ƙyalle.
Tsayawa tayi a inda aka tanada dominta ta fara bin bayin da kallo cikin Æ™asÆ™anci da wulaÆ™antarwa tana wani yatsina fuska, yanda take kallonsu kamar mai nazarin wani abu yabawa idanunta damar hango mata wannan bawan daya naÉ—e kansa da cikin tsananin mamaki da baÆ™in ciki ta zuba masa idanu ranta yana tambayarta “waye shi a cikin bayi?” Juyawa tayi ta nufi hanyar da zata kaita É“angarenta bayan wuccewarta kowa ya watse cike da mamakin ko meye ya dagula walwala Gimbiya daga fitowarta?
Babu me ikon yin wannan tambayar saboda haka kowa ya kama aikin gabansa inda cikin bayin masu gajen hƙr da son sanin abinda bai shafesu ba suka fara tambayar junansu kamar yanda yake faruwa yanzu a Madafi inda na hango wasu mata guda biyu suna aikin gurza kwakwa.
ÆŠaya ce ta É—ago ta dubi Æ´ar uwarta tace “Salame yau gidannan fah babu alamun lafiya ran Gimbiya Samha ya jagula” riÆ™e haÉ“a Salame tayi tace “Yo ashe bani kaÉ—ai nayi wannan baÆ™in ganin ba ko meye yasata rashin walwala?” Goge hannu JaÉ“É“e tayi jikin zaninta tace “Yau har É“angaran sarauniya saidai ayi na dole wato hÆ™r
Saboda ran Æ´ar lele jinin gwal ya É“aci na kowa ma zai iya É“aci….” Shiru sukayi tare da É—ora hannunsu saman bakinsu jin motsi alamar akwai me shirin shigowa, wata kuyanga ce cikin kuyangin Gimbiya Samha ta shigo ta tsaya bakin Æ™ofa tace “Gimbiya na buÆ™atar tataccen ruwan kwakwa da markaÉ—aÉ—en dabino…..” Tun kafin rufe bakinta suka É—auki tambulan na gilashi suka tsiyayo cikin wani nau’in abin adana sanyi ta karÉ“a ta fice daga madafin ta nufi sashin Gimbiyar tana zuwa ta ishe ta ta miÆ™e sai zagaya É—akin nata takeyi tana dukan hannunta, daidai shigowar kuyangar ta juyo ta karÉ“i ruwan kwakwar ta kafa bakinta ta kwankwaÉ—a cikin bazata tayi jifa da cup É—in ta cizge hular kanta ta jefar dogon gashinta ya bazu a kafaÉ—arta zuwa gadon bayanta tace.
“Wayeshi Baiwa Sambur wayeshi da yake zuwarmin da siffar da bana ganewa kowa baya ganewa? Meye yasa Ni kaÉ—ai nake ganinsa cikin bayin gidannan…. Sambur a bincikomin wayeshi inason sanin wayeshi meye yasa yake zuwa da É“atacciyar siffa……..
[23/09, 8:31 pm] +234 904 674 2752: BAWA NA
OUM HAIRAN
F PAGE 3-4
Follow me
Karin wasu littafai da zaku so
-
Matar maza 3
-
Zuciya ta
-
Mahaukaci ko boyayyen masoyi
-
Wuka a makoshi
-
Aure da haihuwa
-
Husna Hausa Novel
-
Musayar Zuciya
-
Gangar Shedan
-
Angon mata biyu
-
A gidan mu take
-
Bafulatanar Rugga
-
Matar yaro
-
Mr Bello
-
Mijin Buzuwa
-
Gidan Uncle Complete
Powered by: www.mynovels.com.ng
Cikin ladabi Baiwa Sambur ta rusuna kamar me shirin aikata sujjada ga uwar gijiyar tata tace “angama ranki ya daÉ—e lallai za’a bincika don sanin meye yake tafe dashi” iska Samha ta furzar ta faÉ—a kan wani gadon hutawa me lulawa tana sauke numfashi idanunta ya kada yayi jawur alamun da gaske É“acin rai ya shigeta, tana nan zaune aka buÉ—e Æ™ofar aka shigo ta É—auki idanunta ta É—orasu ga Æ™ofar ba kowa bace illa mahaifiyarta sarauniya Nuwaira, bayi na take mata baya har zuwa iyakarsu sukaja suka tsaya tare da juya bayansu gasu Gimbiya Samha da mahaifiyarta.
Cike da murmushi Sarauniya ke takawa har zuwa mazaunin É—iyar tata ta zauna a gefen Gimbiya tare da É—ora hannunta a fuskarta tace “fuska me kyau da murmushin aminci ta dace yake Æ´ata tabbas labari ya isheni yau ma kamar wancan makon baki samu nishaÉ—in da kike buÆ™ata a fitowar makonki ba hassali ma zuciyarki jagula tayi shin ko zan iya sanin dalilin shigar Gimbiya damuwa a yau?”
MiÆ™ewa Gimbiya Samha tayi daga inda take kishingiÉ—e tace “Idan ya kasance mutum ne kamar Ni zanyi masa azaba me raÉ—aÉ—in da sai ta sanyashi nadamar wasa da hankalina da yayi, yake mahaifiyata idan kuma ya kasance jinnu ne to zansa a gina masa kurkuku a Æ™arÆ™ashin Æ™asa wadda zansa aljanu dubu arba’in su rinÆ™a yi masa azaba salo salo har zuwa lokacin da ajalinsa zai riskeshi, tabbas yayi wasa a inda ba’a wasa yake mahaifiyata. Waye shi? Meye taÆ™amarsa kuma meye yasa yake zuwa da fuskarsa a rufe wanne matsayi gareshi cikin bayin gidannan?”
Cikin rashin fahimta sarauniya Nuwaira take kallo da sauraron É—iyar tata har Saida taga taja numfashi sannan ta miÆ™e tace “waye ne kike magana akansa yake abar Æ™aunata meye haÉ—inki da bawa cikin bayin gidannan?” Iska Gimbiya ta furzar tace “Lallai ne nabada yau zuwa gobe a bincikomin wayeshi idan hakan ta gagara to raina zai É“aci zan kasance cikin Æ™unci dana kasance na rasa samun biyan buÆ™ata a karon farko a tarihin rayuwata….”
Da sauri sarauniya tace “Aa yake Æ´ata na rantse da hasken abar Bauta bazaki taÉ“a rasa abinda kikeso ba dole ne a binciko ko waye….” Tana faÉ—in haka ta juya ta fice daga sashin na É—iyarta ta nufi sashin bayin gidan tun kafin isarta sanarwa ta isa garesu su daidatu akan kafafunsu ga sarauniya nan da kanta, nandanan kowa ya fara neman nutsuwarsa yana sanyawa kansa kafin isowar sarauniya gurin ya nutsu yayi cif tana zuwa ta tsaya a gabansu tana Æ™are wa kowacce fuska kallo cikin nazari da son gano bawan da É—iyar tata takeson sani can ta É—ago cikin isa da izza tace “Inason ku fitomin da baÆ™on bawan da yazo taron tsaiwar fitowar Gimbiya wancan makon sana ya kuma zuwa wannan makon” nandanan suka fara rarraba idanu kowa yanason gane fuskar bako a cikinsu amma sun kasa ganowa can wani cikin tsofaffin bayin gidan yayi gyaran murya tare da takowa ya gurfana gaban Sarauniya Nuwaira yace “Rana ta baki nasara ya shugabata shiÉ—in ya kasance ba zaunannen bawa bane a cikin gidannan yana shigowa ta Æ™ofar kudancin masarauta sannan yana fita ta gabashinta na naÆ™alci hakanne tun shigowarsa ta farko lkcn ina saman tsauni me tsarki ina addu’a naga ketowarsa akan doki ya sauka ya saki dokinsa a saura ina tsaye ina kallonsa har ya iso wajen taron fitowar makon Gimbiya ya naÉ—e fuskarsa da farin alawayyo, ban gajiya ba har zuwa lokacin da naga ya sulale daga cikin taron ya nufi gabashin masarauta can naga dokinsa ya tafi da gudu gareshi ya haye samansa ya fice.
Sai na cika da al’ajabi gashi dai yazo da shigarmu ta bayi kuma ya fice da wata shigar daban to wannan tasa yauma na sake zuwa don ganin meye zai faru ilai kuwa ya kuma shigowa kamar yanda ya shigo wancan makon”
Shiru gurin yayi sarauniya Nuwaira ta tafi nazari can ta É—ago tace “Tsoho Hikam kaine kasan inda wannan bawa yabi lallai ne ina buÆ™atar Æ™asar gurin daya taka” tana faÉ—in haka ta juya ta nufi hanyar da zata sadata da sashin ta, hankalinta a tashe zuciyarta a jagule kuma cike da fargaba, lallai idan abinda take tunani ya kasance ba itaba hatta masarautar Yamlash tana cikin tsaka me wuya.
Wani É—aki ta shiga ta kulle kanta ta isa jikin wani madubin tsafi dake girke jikin bango ta dauki wata saÆ™alalliyar butar Æ™arfe ta watsa jikin madubin tana me karanta wasu surkulle take wata guguwa ta taso daga cikin wannan madubi tayi tsiri sama tayi hanÆ™am tana wani irin gunji can bayan shuÉ—ewar mintina guguwar ta fara yin Æ™asa hardai ta É“ace gurin ya bada wani siririn rami take wani maciji ya sulalo ta ciki ya fasa kai kawai saiya rikiÉ—a ya zama wani gabjejen aljani ya rusuna gaban Nuwaira cikin muryarsa mara daÉ—in ji yace “HaÆ™iÆ™a duk sanda kira ya riskeni daga wannan masarauta nasan akwai wani abu rikitacce kuma cukurkuÉ—aÉ—É—e da yake shirin faruwa yake wannan Gimbiya kuma sarauniya meye ya tunkaroki ko kuma kike tsoron tunkarowarsa da yasa kika buÆ™aci taimakona?”
Numfashi ta sauke tace “Yakai aljani Hijaz kayi sani Kafin mutuwar mijina sarki Nu’uman ya sanar dani akwai wani lokaci da zamu riska nida É—iyata Samha da zamu zama abokan gabar juna ta dalilin namiji ya sanar dani ba Æ™asÆ™antacce bane saidai zai bayyana da siffa mafi Æ™asÆ™anci ta bawa kuma zai É“ace cikin bayin wannan masarauta harsai yayi illa garemu sannan zai bayyana kansa, zuciyata tayi rauni hankalina ya tashi daga sanda naji Samha tana bincike akan bataccen bawan da yake bayyana mako biyu kenan duk ranar fitowar makonta”
Shiru ta gifta na lokaci me tsayi kafin aljani Hijaz ya É—ago idanunsa cike da Æ™walla yace “A lokacin ne ajalina zai riskeni bazan iya gujewa afkuwar hakan ba tabbas wannan lokaci ya Æ™arato yake wannan Gimbiya kuma sarauniya amma bazan iya baki tabbaci akan kasantuwar wannan bawa ya kusa bayyana ko shine ya bayyana ba domin komansa a lulluÉ“e yake babu abinda yake bayyana daga gareshi”
Dukan kanta tayi tace “Ina bazan taÉ“a amincewa wannan abu da kuke hasashe ya faru ba saidai ko meye zai faru ya faru ina amfanin tsaron dana sanyawa abar Æ™aunata kenan ina amfanin kangetan da nakeyi domin tsareta daga harin Æ´aÆ´an manyan sarakan duniya domin naci alwashin Gimbiya bazatayi aure ba bare tayi nesa dani bazatayi aure ba bare ta kwankwaÉ—i É—acin dana kwankwaÉ—a bazatayi aure ba bare darajarta ta fadi wani Æ™asÆ™antacce wulaÆ™antacce yake jin shi a samanta yake inko har ya zama dole to saidai ya amince itace a samansa dole kamar yanda na rayu da ubanta nice matsayin miji shine matsayin mata to shima wanda Æ™awarsa tasa ya nace sai Gimbiya to Saidai ya amince su rayu a haka in ko ba haka ba saidai ya haÆ™ura…….