Dena Kulani Hausa Novel Part 1
Dena Kulani Hausa Novel Part 1
*GWANDOU* ..1
_©2022._
*DENA KULANI* .
_Page._ 1
_BISMILLAHIR RAHMANIR RAHEEM_ .
“`DEDICATED TO MOMMAH..“`
••••••••••••••
*IBRAHIM ALI WAKKO PALACE* …
Matashiyar budurwa ce zaune a É—aya daga cikin manya royal chairs É—in da ke zube acikin haÉ—aÉ—É—en parlourn, kishingiÉ—e take a É—aya side É—in kujerar da take zaune, hannun ta É—auke da wani book da alama shi take dubawa.
Zirrrr-zirrrr! Kukan da wayarta keyi shine ya mayar da ita daga duniyar littafin da tafaɗa, hannu ta miƙa ta ɗauki wayar haɗi da ɗaurawa a kunnen ta.
“Na’am Khadijah, lafiya Æ™alau nake kamar ke, bansan me ta cikin wayar ta gaya mata ba naga ta zare idanuwa haÉ—i da xabura tare da faÉ—ar yaushe?
O.ok-ok bari nayi sauri Nima aduba min tawah”.
Saurin ajiye wayar tayi agefen kujera saura ƙiris ta faɗi,batama lura ba saboda tsananin saurin da take zabgawa.
“Ummah-ummah! Wa’ec tafito wallahi Ummah exam ta fito”, take ta faÉ—a ba Æ™aƙƙautawa.
Ganin wanda yake zaune a gefen Ummah da gani suna tattauna wata magana mai muhimmanci ne, yasa ta fara tattnatsuwar ta.
Kallo na nakai gun wadda take kira da Ummah nayi,Masha Allah wata matashiyar matace Zaune a saman sallaya yayinda wani matashin saurayi yake zaune a gefen ta kallo É—aya zaka yi musu ka gane cewa dukan su jinin Fulani na yawo a jikinsu.
“Lafiya oum-salmah kike min wannan kira kamar zaki Æ™ara Arar baki,meya faru” Ummah ta Æ™arasa faÉ—a tana mai zuba mata idanuwa.
Ganin yanda tayi tsuru-tsuru da idanuwa ne yasa Ummah girgiza kai haÉ—i da kallon saurayin dake zaune a gefen ta wanda shima ya zubawa Oum-salmah idanuwa yana mata kallon mamaki janye idanuwan ta tayi daga kansa tare da faÉ—ar Abdul…na’am Ummah…kaje ta baka cards É—inta na wa’ec aduba mata, dan nasan idan nace sai gobe yarinyar nan bazata samu baccin kirki ba.
Littafan Hausa Guda 1000 Download
Ok Tauyayi, ke.. je…..maganarsa ce ta maÆ™ale ganin yanda tayi wata sufa kamar fatalwa, kasa rufe baki yayi saboda ganin ikon Allah, murmushi Ummah tayi tare da faÉ—ar “Allah ya shirya ki Salmah”da Ameen yaah Abdul ya amsa dan tana buÆ™atar addu’ar.
Shigowar tane yasa Ummah Æ™ara Binta da kallo haÉ—i da haÉ—ar”kifayi a hankali,duk kinbi kin susuta kanki… Uhm!!”Tauyayi”
Ummah Salmah ta ƙarashe faɗa idanuwanta na cikowa da hawaye.
MiÆ™awa Yaah Abdul slip É—in tayi haÉ—i da faÉ—ar”Please yaah Abdul dan Allah kayi sauri…É—agowa yayi tare da hararar gefen ta haÉ—i da faÉ—ar matsamun aka kada kifaÉ—a akaina, dan nalura kinyi loosing control É—inki, saura balance.
Tura baki tayi tare da komawa gefen Ummah ta zauna,…zaro wayarshi yayi daga cikin aljihu, ganin ya fara duba slip É—in tata hakan ya tabbatar mata da cewa acikin wayarshi zai duba mata,nan take kuwa jikinta ya Æ™ara tsuma,Rufe idanuwan ta tayi tare da cusa fuskarta a tsakanin cinyoyin ta, addu’a kuwa babu kalar wadda bata jawowah amma kowacce daga tafara daga tsaka sai kuma tafara ta kasa Æ™arasawa…wannan shi ake kira da Anxiety.
Yes..yes..yes! Jin irin yanda yaah Abdul keyi shine ya mayarda ita a hayyacinta,saurin miÆ™ewa tayi kamar zata kife ta Æ™arasa gunshi…zubewa tayi dai-dai Æ™afafun sa tare da tambayar sa”menaci yaya,menaci? Nasamu?…kin samu sister,kinsamu gaba É—aya B, zaro idanu Ummah dake gefensu tayi tare da faÉ—ar B, fah kace Abdul …kuma gaba É—aya?
ÆŠagowa yayi daga inda yake zaune tare da nunawa Ummah fuskar wayar tasa, Masha Allah Ummah tafara faÉ—a haÉ—i da fara shafa kan Salmah da tayi relax a gefen ta.
Bari naje a fito mata da ita faÉ—ar Abdul yana mai miÆ™ewa tsaye dan barin É—akin murmushi É—auke saman fuskar shi,iyye Salmah yar jami’a yafaÉ—a yana mai barin É—akin.
ÆŠago kanta tayi tare da faÉ—ar Ummah Abba zaiyi farin ciki koh?…ehh mana kin taÉ“a ganin ubanda Æ´arshi zata samu alkhairi yaÆ™i farin ciki?,jinjina kai tayi tare da faÉ—ar nakusa zuwa higher school hmmm! Waya ganni…
………..
*AMBASSADOR ABDULLAHI SHAMS P.*
°°°°°°Ma’aikata ne zube acikin harabar gidan,yayin da kowa yake kan aikin sa duk da kasan cewar magrib ta gabato…wani kamtamemen gida ne wanda kallo É—aya zakayi masa kagane cewa lallai duniya ta zauna a hannun masu gidan kuma har ila wayau suna kan jin daÉ—in su.
…fihh..fihhh horn É—in da naji anyi shine ya mayar dani ga kallon hanyar katafaren get É—in gidan wanda kusan masu gadi har biyu ke fakon shi da kuma Æ™oÆ™arin buÉ—ashi idan har É“uÆ™atar hakan ta kama.
Wata dalleliyar farar mota ce Æ™irar “Toyota Camry 2020, ta Kunno Kai acikin filin harabar gidan yayin da wani zazzafan sauti ke tashi acikin ta.
Masha Allah wata matashiyar budurwa ce ta fito daga cikin motar wadda aƙalla shekarun ta bazasu gaza sha tara(19) ba aduniya, sanye take da riga da wando waɗanda suka kama jikin ta sai kuma after dress data ɗora saman tufafin wadda taji aiki da jajayen stones, zan iya cewa itace abunda ta taimaka wajen rufe ƴan madaidaitan mazaunan yarinyar.
ÆŠaya Æ™ofar motar naga anÆ™ara buÉ—ewa yayin da wata yarinya Æ™aramar wadda shekarun ta bazasu wuce 6-7 ba aduniya da fito daga É“angaren, latsar wayar dake hannun ta take yi hankali kwance ba tareda wani damuwa ba…El~herm kenan Æ™arama,É—iya ta Shida kuma last born, agidan ambassador Abdullahi shams.
Wani ma’aikaci ne yayi saurin Æ™arasowa gurin su,..cikin girmamawa yake gaida babbar wadda ake kira da Ameerah”Barka da dawowa ranki ya daÉ—e” É—ago idanuwa tayi tareda barin kallon wayar dake hannun ta, yawwa tafaÉ—a tana mai janye jikin ta daga gun motar da take jingine, keys É—in motar ta cilla mishi tana mai juyawa haÉ—i da faÉ—ar “Na Manzo, komai abishi bisa kan tsari, yanda aka saba ba abinda yake haÉ—e komai a ware yake ok.
An gama ranki yadaÉ—e yafaÉ—a yana mai saurin juyawa domin cika umarnin hajiyar sa.
……da sallama É—auke a bakin ta tashiga babban parlour nasu,wanda a kallo É—aya zaka iya kwatanta shi da aljannar duniya…É—auke yake da kayan alatu na morewa rayuwar zamani, Masha Allah tsayawa bayanin É“ata lokaci ne, amma zaku iya kwatanta wa..iya tunanin ku..yaya gidan hamshaÆ™in É—an kasuwa wanda ya mallake kamfanoni daban-daban, wanda kuma yake da hannun jari da Æ™asashe da dama A faÉ—in duniya,shin ya muhallin shi da kuma iyalan shi zaku kasan ce?.
Wata ƙofar naga ta nufa inda Ni kuma na rufa mata baya domin ganin inda ta dosa.
Sallama ta Æ™arayi a karo na biyu tareda Æ™arasawa cikin madaidaicin parlourn wanda a yake É—auke da wasu Italian chairs set ukku…, Wai ku bakwa jine sai faman sallama nake yi kun wani shareni…to mu ina mukaji cewar Shemaah, Shema’u itace wadda Ameerah take bima a shekaru.
“toke Malama waya kasa dake ne balle ki É—auka..wama ya kawo ki gidan nan yanzu?…uhmm! so gida sai kace ba satin can kikazo ba, mtssww.
Mayarda kallon ta tayi gun babbar yayarsu Balkisu wadda itace É—iya ta biyu agurin Hajiya na’eemah da kuma Ambassador Abdullahi shams, Ah aunty bilki yaushe a gari,zuwa haka ba sanarwa?…to uwata yi haÆ™uri kinji..nayi kuskure ban nemi izinin kiba da yake igiyar auren nawa a hannun ki take ko?..kai aunty me yayi zafi haka, Allah ya huci zuciyar ki..ta Æ™arashe faÉ—a haÉ—i da zama a saman É—aya daga cikin kujerar parlourn.
*(ASALIN IBRAHIM ALI WAKKO* )
~~mahaifin Alhaji Ibrahim haifaffen jihar Borno ne wanda ya tashi yana rayuwa acikin mai duguri,tareda matarsa da kuma Æ´aÆ´ansa ukku mata biyu da kuma namiji É—aya, Hindatu, Ummu Salamah da kuma Ibrahim.
Alhaji Ibrahim sun tashi cikin gata da kuma jin daɗi,da yake mahaifinsa mutum ne shi mai neman na kanshi da kuma jajircewa wajen biyawa iyali buƙatun su gudun faɗawa halaka.
Duk da kasan cewar mahaifin Alhaji Ibrahim baiyi boko ba amma ya ginu da burin saka nashi iyali don kaucewa jahilci da kuma neman madafa dan ba’a san me gobe zata haifar ba.
Cikin ikon Allah kuma,sai ya sami iyali jajirtattatu masu buƙatar ilimi, acikin ƴaƴan nasa daya mallaka ba bora afagen ilimi,tun daga fannin arbiya har kan ilimin zamani (boko).
Hindatu itace babbar, sannan Ibrahim sai kuma Æ™aramarsu wato Salamah,sun tashi cikin soyayya da Æ™aunar juna..haka dai rayuwa taci gaba da tafiya yau daÉ—i gobe a kasin hakan, bayan jan wasu shekaru kuma, sai Allah ya É—auki rayuwar Alh Ali wakko bayan ya aurar da Æ´aÆ´ansa mata, a inda shi kuma Ibrahim yake a mataki na biyu a jami’a…mutuwarda ta taÉ“a iyalinsa da kuma maÆ™ota tareda Æ´an uwah na nesa dana kusa.
Kasancewar a lokacin boko kamar a kyauta ne, sannan ba kowa yake yin shiba saboda suna mishi wata mahanga ta daban yasa Alh Ibrahim yasamu damar cigaba da karatun sa tareda taimakon wasu wakilai na makarantar su ba komai kuma ya jawo hakan ba sai dan kasancewar sa ɗaliba mai ƙwazo.
Haka dai rayuwar taci gaba da tafiya yau daÉ—i gobe akasin hakan har zuwa lokacin da ya kammala karatun sa,a sannan ne kuma ya samu yarinyar da yake so har soyayyar takaisu da aure… To masu karatu karku shagala labarin mu yafara ne A gidan Alh Ibrahim Ali wakko, a inda yanzu yake tareda matar sa da kuma Æ´aÆ´an sa biyu da Allah ya mallaka masa, a yanzu haka yana aikin gwamnati (civil servant) a inda yake da babban muÆ™amin permanent secretery of finance…
**ASALIN*
( *AMBASSADOR ABDULLAHI SHAMS* .)
_to be continue_ …
🩸🩸🩸🩸🩸🩸
*©GWANDOU.*
[11/10, 8:36 pm] +234 814 290 4255: 🩸🩸🩸🩸🩸🩸
*@GWANDOU* ..
_©2022_ .
*DENA KULANI* .
_Page.2_
*ASALIN*
( *AMBASSADOR ABDULLAHI SHAMS* .)
…Mahaifin Ambassador Abdullahi haifaffen jihar Kano ne,a inda mahaifiyar sa take Æ´ar asalin Æ™asar Niger a garin agadaz,.. dangin ambassador Abdullahi masu arziÆ™i ne,yayin da wasu ma suka ce sungadi arziÆ™i tun daga kakannin ka kanni.
Ambassador Abdullahi shams ya gadi arziƙi ta uwa da uba dan kuwah ko dangin mahaifiyarsa ba baya ba wajen dukiya, suna cikin jerin masu arziƙi na farko a ƙasar niger.
A yanzu haka ambassador Abdullahi shams,babban ɗan kasuwa ne wanda sunan sa yazagaye kaff, ƙasashen duniya,yake kuma da hannayen jari a ƙasashe da dama.
Yanzu haka yana tareda mahaifiyarsa da iyalinsa a garin Abuja Nigeria,.. Æ´aÆ´ansa shidda (6)maza biyu mata huÉ—u,Balkisu Al-Æ™asim, Muhammad, Shema’u, Ameerah,sai kuma El-herm.
Matarsa Hajiya na’eemah bata ga maciji da talaka ko Æ™adan, wannan aÆ™idar Tata itace ta zauna ajinin Æ´aÆ´anta mata musamman balki da Shema’u dan ita ameerah hankalinta bai zaunu ba kuma yawancin zamanta a gurin kakarta take yinsa saboda basa wani shiri da mahaifiyarta…ba komai ya jawo hakan ba kuwa sai É—an banbancin halayyar da suke dashi a tsakaninsu.
*CI GABAN LABARI* …
…Matashin saurayi ne zaune akan dining, dogo ne fari tass, sanye yake da shadda kaftan ruwan zuma,wadda ta Æ™awatu da aikin brown É—in zare.
Abincinsa yakeci hankali kwance batare da wata damuwa ba yayin da yake aiki da wayar shi murmushi ne kwance akan kyakkyawar fuskarsa,hakan zai nuna maka cewa yana wani nishaÉ—in ne.
Jan É—aya daga cikin kujerin da akayi ne ya mayar dashi daga duniyar nishaÉ—in daya lula, murmushi ya saki yana mai ajiye wayar dake hannun shi,tareda faÉ—ar “good morning mommy,.. murmushi Hajiya na’eemah tayi tareda faÉ—ar “morning dear, numfashi taja sannan taci gaba da magana, meya hana Muhammad dawowah ne?hmm! Ko har yanzu yana fushi ne?.
Ajiye cokalin dake hannunsa Al-ƙasim yayi tareda juyowa ya ƙara fuskantar mahaifiyar tasa, No mommy ba wannan dalilin bane ya hana shi dawowah ba akwai ƴan ayukkan da yake so ya kammala ne, dan har mun shirya tafiyar tare kuma sai wani aikin ya taso masa shine kawai dalilin.
Numfashi ta sauke, haÉ—i da kallon É—an nata,tareda faÉ—ar”ka tabbatar Wannan ne..ehh! Mommy…ok shikenan dama na tambaya ne dan nasan halin murÉ—aÉ—É—en halin shine.
Fitowar ameerah ne yasa suka bita da kallo gaba É—ayansu,sanye take da kayan bacci hakan ne ya tabbatar musu da cewar lokacin ta tashi daga baccin, Good morning mommy, ta Æ™arasa faÉ—a haÉ—i da zama É—aya daga cikin kujerin dining É—in, “welcome back brother,ta faÉ—a tanamai fara serving na kanta… thanks sister, ya exams…kwanaki dady yake gayamun kin kusa kammala exams É—inki.
Cokalin dake hannunta ta ajiye tareda kallon mommy sannan ta mayar da kallon ta agurin shi, wai yaya Æ™asim kar-dai kacemun bakasan har exams ta fito ba, lallai kam, gashi har ameerah na batun wucewa Æ™asar Paris karatu,..cike da mamaki ya furta”Paris kuma mommy, duk makarantun da suke acikin Nigeria basuyi ba har sai ta sake zuwa Æ™asar waje karatu? Uhm!.
To meye aciki, naga dai kaima a waje kayi karatu kuma yanzu haka acan kake rayuwar ka, wani abun yasa meka ne?…naga dai acan tayi secondary school gashi kuma ta gama lafiya Æ™alau dan haka kar nakuma jin wannan maganar.
Nifa mommy a naija zanci gaba da karatu na, dan haka karma ki kawo min wani zance dan nagaji da rayuwar can… rayuwar doka anan kawai zan cigaba da karatu na, tomm.
FaÉ—ar ameerah tana mai cigaba dacin abincin ta hankali kwance ba tareda tasake cewa komai ba…bazakiyi anan ba nace, bazakiyi ba dole kije Æ™asashe masu cigaba kiyi karatu hankali kwance,kai kuma idan har bazaka goye bayan taje waje karatu ba na fitar dakai acikin maganarr…buga teburin da akayi shine ya dakatar da’ita daga Æ™arasa maganarta.
Dakata Malama,shin dakike wannan maganar karatunki ko nawah,haba dan Allah karfa kiso ki takurawa rayuwata yanzu fa nakai matakin da zan iya yanke wa kaina ehh! Ko a’ah! So be careful ok.
Juyawa tayi cikin fushi,cike da sassarfa take taka matakalan da zasu fitar da ita daga dining É—in kamar zata tashi sama.
Ruwan da Al-Æ™asim ya miÆ™a mata sune suka mayar da’ita daga nisan da tayi,ajiyar zuciya take ta saukewa ba Æ™aƙƙautawa.
Kinga illar fitar da’ita wajen ko?,..yanzu mommy ki duba fah kigani secondary kawai tayi a Æ™asar London amma ki dubi idanuwan ameerah yanda suka dawo tsakiyar kai, batajin maganar kowah..idan zaki yarda da magana ta mommy yanzu haka ameerah tanashan Æ™wayoy…whatttt!!..mekake shirin faÉ—a ne Æ™ashim..kafita daga hankalinka ne? Kodai kafara Æ™iyayyar Æ´an uwanka ne? Ƴar tawa?..calm down mommy..bafa nafaÉ—a danki tayarda hankalin ki bane, kawai dai abinda nake hasashe ne ok.
Kaci ƙaniyar ka dakai da hasashen, Ni banyi shashanci da kuruciya taba,dan haka bazan haifi ƴan iska ba..sorry mommy.
Kwafa tayi sannan taci gaba da faÉ—ar” Bama wannan ba..kunyi magana da hajjoo (balkisu)?..kallon ta yayi cikin yanayin dake nuna mamaki sannan yace” bayan gaisawa kuma akwai wani magana da zamu tattauna da’ita ne?…ok kenan bata gaya maka komai ba..ehh! Nikam ba abinda muka tattauna..but tunda gaki kuma ina ganin abu É—ayane kifaÉ—amun kawai ok.
“Bari nazo” faÉ—ar mommy tana mai mayarda hankalinta gun wayar ta.
“Hello,..hajjo kisameni a dining area yanzun nan kinji.
Ajiye wayar tayi tana mai Æ™ara fuskantar sa…Uhm! Ya ayyukan naku daddynku ya gaya mini cewa abubuwan sai gaba suke Masha Allah..
ehh! Alhmdllh gaskiya komai yana cigaba da tafiya da kyau, yanzu haka Ni ina Æ™oÆ™arin zuba hannun jari da wasu kamfanoni da suke a Æ™asar _england_ da kuma _Paris._ .”wow that’s my son” faÉ—ar mommy tana washe haÆ™ora.. lallai yarona ya zama babban mutum.. Muhammad fah..mug É—in da ke gefen shi ya jawo tare da É—aukar Æ™aramin cup É—in dake gabanshi, tsiyaya lemon dake ciki yayi sannan ya É—ago..no mommy kinsan fah my bro bayason ana fallasa mishi secret then,yafiso yafaÉ—a da kanshi,so kijira dawowan shi..zai gaya maki komai about him ok.
Al-Æ™asim!..takira sunan shi tana mai kafeshi da idanuwa…”Yes mom”yafaÉ—a cike da sakalci,..gayamun me Muhammad yayi achieving banason shashanci..kodai har yanzu yana tareda damuwa ne.. Please Æ™asim karkamin Æ™arya.
“Hhhh” best mommy in the world..ok Æ™asim dariya ma nabaka..no sorry mommy..kawai dai inaso kigane cewa Muhammad fah yayi forget da komai ya kama aikin shi,..tunda kuka nuna bakwason yayi aikin lafiyar ya tattara ya watsar,..yanzu haka Muhammad Æ™asa biyu sukayi masa request na haÉ—a hannun jari dasu.. _Qatar_ da kuma _U.k_ sannan kuma ya kammala ginin babbar University da yake yi a Æ™asar nan kuma acikin garinnan na Abuja..wadda take Æ™unshe da fannoni da dama.. sannan yananan yana nema mata greatest teachers daga Æ™asashen waje har nan gida Nigeria..sannan makarantar tana É—auke da special and desirables men and female hostels..so calm down mommy your son’s wanna be famous of the world.
“Wow!AlÆ™asim ka faranta mun rai ba kaÉ—an ba,ina alfahari daku ta Æ™arashe faÉ—a tana mai murmushi irin na Æ™asaitattun matan nan,to maganar aure fa,Kanada wadda kake nema ne?
Gaban sane yayi wani dukan ukku-ukku,cike da gargada ya fara faÉ—ar,
“mom..mom..Ina..da but..Æ™arasowar Hajjo gurin ne ya katse mishi maganar da yake kanyi.
Barkan ku da hutawa hajjo ta faÉ—a tana mai Æ™oÆ™arin zama…tsayar da’ita mommy tayi ta hanyar cewa”no hajjo muje can cikin parlour dan maganar bata nan bace,kinsan Æ™annan naki sai nayi da gaske..naji yafara kawomin zancen yanada wata..muje naji Æ´ar waye acikin Æ™asar nan.
Dariya hajjo ta saka tana mai kallon Æ™asim da dayi wani kalar tausayi duk jikinsa yayi sanyi,gaba mommy tayi tana mai faÉ—ar “hajjo!..jawomin kan Æ™anin nan naki nayi dashi yanxun nan.
“Oya tashi muje mana”cewar hajjo tana mai Æ™oÆ™arin jan hannun shi,É—an É—agowa yayi tareda leÆ™awa ta bayanta ganin mommy tayi nisa ne yasa ya mayarda hankalin shi gurinta tareda faÉ—ar”Please sister ki taimakeni da wannan alfarmar,nasan mommy na É—aukar shawarar ki sosai idan kinka bata shawara zata É—auka kinji..wai menene kaketa wani magiya kaje kai tsaye ka gayan abinda kake so mana.
Wayarshi yayi saurin jawowa.. buÉ—e ta yayi tare da shiga cikin galleries É—insa,hoton wata yarinya ya shiga tareda mika mata wayar.
Wow! Wacece wannan, tanada kyau.. murmushi Æ™asim yayi tare da jinjina kai,”but who’s her father? FaÉ—ar hajjo tana mai tsura mishi ido.
ya mutse fuska yayi tare da kallon ta.. menene kuma na wani tambayar babanta.. tambaya nayi dan nasan Æ´ar gidan waye..”to sannu mommy.. ahh..sannu tunda haihuwa na kikayi da zaki wani tsureni da tambaya,barima kawai na gaya maki ita ba Æ´ar kowan kowa bace,..abinda nasani kawai su talakawa ne..babanta babban malami ne a garin su..daga Æ™arshe abunda zan gaya maki shine itace matar da zan auraah…
Idanuwa hajjo ta fitar waje haÉ—i da faÉ—ar”whatt”…..
🩸🩸🩸🩸🩸🩸
*@GWANDOU* 😍