Dr Khaleel Hausa Novel Complete

~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar
1…..
A hankali yake cin fruit Salad din dake gabansa kansa a sunkuye yana murmushin nan nasa mae kyau da ya kai ga har ana iya ganin dimples dinsa, ya girgixa kai snn ya dago yana kallon matashiyar matar dake xaune kan kujerar dake kallon nasa fuskarta a daure ta kafa masa ido tana kallo, murmushi ya kuma yi mai sauti xae yi magana ta rigasa a fusace tace “ohh ga mahaukaciya na magana ko Khaleel, ni ce ma na xama abun dariyarka knn” ya dan marairaice ya ajiye fork din hannunsa yace “ba hka bane Mum, kiyi hkuri,” ya dan shafa kansa da damuwa yace “kinsan komai fa lkci ne mum, kawae su Ummi da Abba sun kasa gane hkn ne, sun ki fahimtar abinda nake nufi am just bored of all dis….” shafa kansa ya kuma yi har lkcn fuskarsa na dauke da damuwa yana kallon Small mum din tasa, sallamar da aka yi yasa duk suka maida hankalinsu ga bakin kofa tare da amsa sallamar, mikewa mum tayi ganin baki tayi da fara’arta tana masu sannu da xuwa suka karaso cikin falon aka shiga gaggaisawa, Khaleel ya mike yana kallon Small mum din tasa yace “to mumy sae na kuma dawowa ko xuwa gobe” tace “a’a ka dae dawo xuwa anjima da daddare bamu gama magana ba” yyi murmushi yace “in’sha Allah mum” bowl din fruit Salad din da ya ci ya dauka xae kai kitchen tace “a’a ka bar shi kawae xa a kwashe” yace “No bari in kai mum” ya nufi kitchen da bowl din ya ajiya snn ya fito yyi ma bakin sallama ya fice daga falon yana kallon agogon hannunsa, gun motarsa ya nufa yana tafe yana satan kallon wata bishiya dake dauke da fararen kujerun roba da table a karkashinta ya ga ko wa inda ya gani daxu gurin suna nan ko sun bar wajen, suna xaune ko har lkcn su biyu kmr ynda ya samesu da ya shigo, sae dae wnn karan ba hira suke ba daya na danna wayarta daya kuma na waya ne, hada ido suka yi da warce ke danna waya don ita ma satan kallon nasa take, ya dauke kansa da sauri, ita ko kallon me wayar tayi tana ‘yar dariya tace “dubi gantalalle neman gaisuwata yake” da sauri tayi pretend tace “lahh Ya Khaleel yaushe ka xo” juyawa yyi yana kallonta duk da yasan taga shigowarsa daxu bbu yabo bbu fallasa yace “kin ban sako ne” ta dan yatsine fuska tace “No kawae nayi mamakin ganin ka a gidanmu ne yau, coz ba saba xuwa kayi ba, any way ina yini” ya watsa mata wani mugun kallo ya bude motarsa ya shige yyi horn mai gadi ya bude masa gate ya fice daga gidan, dariya ta saki tana kallon kawarta da ta kasa ci gaba da wayan da take ta rakasa da kallo har ta daina hango motarsa mai gadi ya rufe gate din, can ta maida kallonta ga kawarta dake ta faman dariya ta sauke ajiyar xuciya tace “gaskiya gayen nn ya hadu Meenah, ni dae hka kawae naji yana burgeni,” Meenah tayi ma kawarta ta wani irin kallo tace “shi Khaleel din ke burgeki? Tabdi da kinsan halinsa da baxa ki ce komai ba wllh! wnn mugun dan rainin hankalin, ae ni tun da na taso kallon arziki bae taba hada mu ba kin dae ga dan uwana ne, ki bari xan baki lbrin ko waye shi salma, kin taba ganin wani cousin dina ya shigo gidan nn ban gaishesa ba, kuma kin dae san ni da son xumunci Salma, tunda har ki ka ga Khaleel ya shigo gidanmu ban gaida sa ba na dauke kai kiyi shiru kawae” Salma tace “haba abun ya ban mmki wllh, to Allah shi kyauta, ni dae mu shiga ciki in yi ma Momy sallama in kama hanyar gida kafin Mama ta fara kirana” Meenah tace “haba tun da wuri hka, to ki bari bakinta su tafi mana, nasan ba dde wa xa su yi ba” Salma ta harare ta tace “lallai kam da yake ke a gidan ku kike ba shiyasa xaki ce in jira bakin da ban san ranan tafiyarsu ba su wuce” mikewa salma tayi ta nufi cikin gida, Meenah ta mike tana dariya ta bita suka shiga falon a tare. Barkan Ku da Sallah sisterz.
[10/14, 3:25 PM] ‪+234 806 484 7850‬: ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar 2…… Karfe tara da rabi na dare Khaleel ya gama parkin din motarsa a parkin space din dake cikin gidansu dake G.R.A kaduna, ya bude motar ya fito yana kallon motar dad dinsa ko ba a gaya masa ba yasan ya dawo, ya nufi balconyn da xae sada sa da kofar shiga babban falon gidan, can ciki yyi sallama ya shiga falon ya tarda kanwarsa Rukayya kwance tana kallo, ta mike xaune ganinsa tace “sannu da dawowa ya Khaleel” ba tare da ya kalleta ba yace “sannu” snn ya nufi stairs, dad dinsa suka kusan cin karo da ya ja baya da sauri tare da dan ritsinawa ya gaishesa, bbu yabo bbu fallasa mahaifin nasa ya amsa snn yace “ina nemanka a falona” dad dinsa na fadin hka ya juya ya koma xuwa falonsa, Khaleel ya share wata xufa dake keto masa a goshi ya shafa kansa snn ya shiga haurawa saman a sanyaye, dakin mum dinsa ya nufa tana xaune gefen gadonta tana waya, mai aiki na yayyanka mata fruits a faranti, ya nemi gefenta ya xauna har ta gama, tana kallonsa tace “sae ynxu son” ya dan marairaice mata yace “ummi don Allah ki raka ni gun abba wae yana kirana” tayi masa wani irin kallo tace “sae na raka ka? Ashe ko baxa ka je ba” ya ciro handkerchief ya share fuskarsa bae ce komai ba ya mike ya fita daga dakin ya nufi falon Abbansa, xaune ya tarda Abban nasa yana shan coffee, ya xauna kasan carpet din dake tsakiyar falon ba tare da ya kallesa ba yace “Abba gani”Abban nasa ya ajiya kofin hannunsa yace “ka gama play din hide nd seek din dani Khaleel” Khaleel ya dan yi murmushi ba tare da ya shirya ba yace “wllh ba hka bane Abba aiki ne yyi min yawa a clinic” ummi ce ta turo kofan falon ta shigo, Khaleel yaji ddin ganinta ta nemi gefen mai gidan nata ta xauna.
[10/14, 3:26 PM] ‪+234 806 484 7850‬: ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar 3….. A hankali Khaleel ya daga kai yana kallon Abbansa ganin shirun yyi yawa, kallonsa ya ga Abba na yi, hkn yasa ya dukar da kansa kuma, Abba ya girgixa kai ya sauke ajiyar xuciya yace “me kke nufi da mu Khaleel?” kasa cewa komai Khaleel yyi har lkcin kansa na kasa, Abba ya maida kallonsa ga TVn dake ta aiki a falon yace “shknn, dat clearly shows dat raina mu kawae kayi, don hka ni na yanke shawarar hada ka da either Meenah ko Maryam, ka je kayi shawara ka xabi daya cikinsu, nd bet me, dat wont take a lng tym, ka tashi ka bamu waje” kasa ko da kwakkwaran Motsi Khaleel yyi daga inda yake a durkushe, komae nasa ya tsaya cak, da kyar ya shiga share xufar dake keto masa a fuska ya daga kai yana kallon Mum dinsa da ko kadan bae ga alaman hkn ya dameta ba, sunayen wa inda Abba ya ambato masa suka shiga yawo a kansa, wae Meenah ko Maryam, ji yyi kmr ya saka ma iyayen nasa kuka, Muryar Abba ya ji a tsakiyar kansa yana cewa “nace ka tashi ka bamu waje” dago kansa yyi da sauri ya marairaice murya yana kallon iyayen nasa yace “don Allah don annabi kayi hkuri Abba wllh ni duk bana son su, na maka alkawarin nn da wata daya kacal xan gabato maku da matar da xan aura plss Abbana consider me, nasan na maku laifi” ya karashe mgnr kmr xae yi kuka, Abba na masa mugun kallo yace “ka raina ma kan ka hankali ba mu ba, common get out my frnd” juyawa yyi da sauri yana kallon Mum dinsa, idonsa ya kada yyi jajur cikin rawan murya ya fara mata mgna “ummi don Allah ki sa baki….” harara ta watsa masa tace “da knn ba ynxu ba” dafe kansa yyi xuciyarsa na tafarfasa, ae shi da ya aure wa in nan yaran da abba ya ambato masa gwara ya mutu ba aure, dat aside ma shi ko kadan bae son auren xumunci kallon arxiki baya hada sa da yaran yan uwan iyayensa gaba daya duk baya sake masu, goge Fuskarsa yyi da handkerchief a nutse yana kallon Abbansa ya fara magana “Abba i knw na maku laifi, plss ku yi hkuri ku yafe min, na kuma maku alkawarin nan da wata daya xan…..” tsawa Abba ya daka masa yace “Enough Malam, tashi ka ban waje” Khaleel bae kuma cewa komai ba ya mike da kyar ya juya ya fice daga falon. Karfe sha daya da rabi Ummi ta shigo dakin Khaleel, yana kwance ya kafa ma Ac ido da ganinsa kasan abun duniya ya ishesa, ummi ta karaso ta xauna gefensa tana kallonsa ya mike xaune yace “ummina kin ga abinda Abba ke shirin min ko” Ummi tace “to ae kai ka ja ma kan ka Khaleel, tun yaushe muke bin ka kana kakkaucewa ka maida mu yara” komawa yyi ya kwanta bae kuma cewa komai ba, sarai tasan halin dan nata da abun da ke iya faruwa kafin gobe in ya kwana cikin tashin hankalin nn da yake ciki, hkn yasa tace “ka kwantar da hankalinka son, na shawo mana kan Abba amma fa da kyar, ya kuma baka wata dayan da kace don hka kafin lkcn ka gabato matar, kar ka kuma ban kunya kasan ni bana son abinda xae taba min kai son” mikewa Khaleel yyi ya rungume ummin tasa cike da jin ddi ya shiga mata godiya, ta shafa kansa tana murmushi ta sa masa albarka snn ta mike yyi mata sae da safe ta fita xuwa dakinta. Kasa bacci Khaleel yyi daren ranan duk da hankalinsa ya kwanta, amma damuwarsa daya ta inda xae fara nemo matar da xae gabato ma parent dinsa ynxu, ta ina xae fara wnn jan aikin, tunanin hkn na mugun tada masa hankali.
[10/14, 3:26 PM] ‪+234 806 484 7850‬: ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar
4…..
. A hanxarce Khaleel ya gama shirinsa cikin bakar suit da wando da farar T-Shirt sae neck tie ash colour, dakin Umminsa ya nufa ya sameta xaune gaban madubi tana gyara gashinta, yace “ummina xan tafi” Ummi na kallonsa tace “baka yi breakfast ba” ya kalli agogon hannunsa yace “idan naje office xan yi ummi, sae na fara xuwa cikin gari an duba min motata” Ummi tace “ba john ya kai shekaranjiya an gyara ba” ya girgixa mata kai yace “a’a it’s still nt ok, xan je da kaina ynxu” Ummi tace “ikon Allah, to shi kadae ne motar ka Khaleel ka dauki wata mana in ya so ko anjima sae john ya maidata” yace “No xan tafi da ita ynxu Ummi na fi son in je da kai na” Ummi tace “to Allah ya tsare” ya nufi kofa xae fita yace “Ameen ummina sae na dawo” tace “to a dawo lfya” a stairs suka hadu da Rukayya tace “yaya baka yi breakfast ba” yace “eh sauri nake sae na je office” tace “to yaya ka ajiye ni ni ma sch xan tafi ynxu” yace “cikin gari na nufa ynxu” yana kai wa nn ya sauka ya nufi kofar fita daga falon, ta bi sa da kallo snn ta dan tabe baki ta nufi dakin ummi. Karfe takwas da kusan rabi Khaleel ya iso cikin gari, ya mika ma engineers din motarsa snn ya nemi kujerah ya xauna tare da fiddo wayarsa yana dannawa to while away time. Tafe take tana bincike jakar dake sakale a kafadarta alaman tana neman abu, cak ta tsaya ta wara ido hade da bude baki ta saki salati tana kallon cikin jakar, hkn ya ja hankalin Khaleel dake xaune har lkcn yana danna waya, juyawa tayi ta bi layin da ta fito daga da kallo, can ta dan tabe baki hade da tsaki ta xuge jakar ta kuma sakala sa a kafadarta da kyau snn ta ci gaba da tafiyarta da takunta mai jan hankali, sanye take da riga da skirt ta atamfa orange colour mae ratsin ash da brown, hijabin jikinta ma orange ne ya wuce gwiwa da kadan, hka ma takalmin kafarta orange ne, jakar hannunta kadae ne brown, da ganinta kasan makaranta xa ta, Khaleel ya bi ta da kallo har ta isa bakin titi snn yyi tsaki ya ci gaba da duba wayarsa, tsaye tayi bakin titin alamar tana jiran abun hawa, ba a Kuma dau lkci ba ta samu ta hau suka bar gurin, kmr ance Khaleel ya juya ya ga wasu fararen takardu a kasa dai dai inda ta tsaya, ya mike ya nufi gurin ya duka ya kwashe takardun har uku yana kallonsu, reciept ya gani da admission letter sae handout na physics, ya girgixa kai hade da tsaki da kmr xae wurgar da su sae kuma ya fasa ya linkesu ya koma ya xauna da xumar ya ba kanikawan idan sun ganta su bata, cikin minti sha biyar aka gama yi ma motarsa abinda ya kamata, ya basu kudi duk da basu bukaci hkn ba snn ya shige motarsa ya kama hanyar office cikin hanxari don ya makara. Tana xaune a class ta sa Chemistry text buk dinta a gaba kmr me karatu taji an rankwasheta, ta juya da sauri kuma a fusace don taga waye, ta wani hade rae tace “bana son irin wasan nn Aisha” Aisha ta xauna tace “Allah ya baki hkuri” sauran kawayen nata ma xaunawa suka yi suna kallonta, Ummi tace “wae me ya faru ne Ashnaah yau duk you re nt ur self” tayi masu wani irin kallo tace “dole ku ce am nt my self tunda ba reciept dinku bane ya fadi” Maryam tace “au wae shi yasa kika xama hka, ba mun ce maki xaki gani ba kila ma a gida kika xubar” tsaki Ashnaah tayi tace “eh naji xan gani a gida ku rabu dani” Bilkisu ta mike ta bar wajen Nafisa ta bi bayanta, Ashnaah ta bi su da harara, snn tace “bari in ta murna na xubar da reciept dina” tana kai wa nn ta mike ita ma ta fice daga class din, Ummi tace “da’alla mu rabu da ita mu muka xubar mata” mikewa su ma suka yi suka bar class din.
[10/14, 3:26 PM] ‪+234 806 484 7850‬: ~Dr Khaleel By Khaleesat Haiydar
5…..
Khaleel ne xaune office dinsa ya jinginar da kansa jikin kujera idonsa lumshe, maganganun umminsa ne ke masa yawo a ka, tunanin ta Inda xae fara neman mata kawae yake, ko kadan shi kam matan kaduna ba su masa ba, basa burgesa, bude office dinsa da aka yi ya sa ya gyara xamansa da sauri ya bude ido ya ga wani isasshen ne xae shigo masa office ba knocking, ta rufe kofar bayan ta shigo, ya wani hade rae yana kallonta, da ma yasan baxae wuce ita ba, bae jira jin me xata ce ba a nutse yace “get out” ta dan marairaice masa tace “ka ga fa files na kawo maka Sir” ya kuma hade rae yace “ki bar min office nace” ajiye files din hannunta tayi nn da nn idonta ya kada, ta juya xata fita, murya can kasa yace “Ameesha” ta juya tana kallonsa sae ga hawaye, ya mike tsaye ya karasa kusa da ita ya kamo hannunta, sae ta sakar masa kuka, dafa kafadarta yyi ya dago kanta yana goge mata hawayen idonta a hankali yace “am sorry” gyada masa kai tayi hawaye na ci gaba da xuba a fuskarta tace “Abbana yace in kawo maka files” tana fadin haka ta juya ta Fita daga office din tare da kullo masa kofarsa, komawa yyi ya xauna ya lumshe idonsa duk abun duniya sun ishesa. Bayan minti goma da fitan Ameesha aka kwankwasa masa kofa, ya tura file din gabansa bayan kmr minti daya yace “come in” wata nurse ta shigo rike da file a hannunta ta gaishesa cike da ladabi snn tace “Dr patient xaka duba, kuma Emergency ne, yace “don me xaki kawo min baki kai ma Dr Umar ba, ni din engine ne?” Tace “No sir suna Theatre ne, Oga ne yace in kawo maka” tsaki yyi ta ajiye masa file din ta Fita, ba a dau lkci ba nurse din ta dawo da patient din ya daga kai yana kallon yarinyar da baxa ta wuce sha takwas ba, bbu abinda take sae kuka tana rike da cikinta, ya dan yi tsaki Mara sauti ya jawo file dinta ya bude yana dubawa, nurse din ta juya ta Fita, yace “ke malama ba kuka xa ki min ba amsa min duk tambayoyina xa ki,” shiru tayi tana goge hawayen fuskarta tana kallonsa, jin ynda tayi shiru lkci daya yasa ya daga kai yana kallonta, ta sunkuyar da kanta da sauri, cire farin glass din idonsa yyi ya sake fuska ya dan sassauta murya yace “daurewa xa ki yi Zeenat and tel me wat ur prblm, look at me” ta daga idonta da ya rine don kuka tana kallonsa, ya sakar mata murmushi snn ya shiga yi mata tambayoyi tana basa amsa. Karfe hudu da rabi Ashnaah ta shigo gida ta jefar da Jakarta nan bakin kofa ba tare da ta kalli inna dake tuka tuwo tsakar gidan ba ta Shige falo, inna ta tabe baki tace “aniyar ki ta bi ki yarinya, kuma ba ni kika wurga ma jaka ba, Adamu kika jefa ma” Ashnaah ta fito tace “kin fara ko inna ni dae fa ki dinga kyaleni, kina ganin na batar da takardun makaranta na gaba daya duk ban gani ba” inna ta mike da sauri ta dafe kirjinta tace “takardun makarantar ki?” Ashnaah kmr xata yi kuka tace “eh mana” inna tace “barawo ne ya sace su ko ya aka yi?” Ashnaah tace “eh mana, kuma gashi ni ynxu bn san me xan ce a makaranta ba, ga kuma Abba ma ban san me xan ce masa ba” inna tace “to wa ke ta wani Abba can, ynxu kawae gobe in shirya in rakaki makarantar in yi ma masu makarantar bayani,” Ashnaah ta xaro ido ta kwashe da dariya tace “Allah ya tsareni, ance maki makarantar ta yara ce kuma snn ba a bari tsofaffi su shiga, ynxu dae abinda nake so dake kawae ke ce xaki ce ma Abba kina kwalema sae kika bude jakar makaranta ta kiga takardu sun yi yawa sae kika kwashe kika xubar kuma masu kwasan shara suka xo suka xubar kinga ae baxae iya cewa komae ba sae ya tafi makaranta yasa a min sabo,” inna tace “ae wnn abu me sauki ne Allah ya kawo sa” Ashnaah tayi murmushi tace “shi yasa nake son ki inna.”
[10/14, 3:26 PM] ‪+234 806 484 7850‬: ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar
6…..
Khaleel ya ajiye pen din hannunsa yana kallon mahaifin Zeenah dake xaune gabansa yace “ka kwantar da hankalin ka sir, in’sha Allah ur dota will b alryt but nt until yhu give her wat her heart desires” Alhajin yace “nt at all, ni ban tada hankali na ba ae, just dat aure ne dae sae na mata ko ta ki ko ta so, sae dae in mutuwa tayi” Khaleel yyi shiru yana kallonsa, can dae yace “duk da halin da take cikin ynxu Alhaji” Alhajin yace “kwarae kuwa” yana kai wa nn ya mike ya fice yana cewa “to in ta mutun ma uwarta dake xugata tayi asara ba ni ba” Murmushi Khaleel yyi ya daga kafada ya ci gaba da abinda yake. Karfe shidda saura na yamma Khaleel ya rufe office dinsa rike da suit dinsa ya nufi ward din da patient din tasa take, tana xaune tayi jigum, wata matashiyar mata na yanka mata fruit ya karaso cikin dakin yana kallonta yace ya jikin?” Kai kawae ta gyada masa, matar dake yanka mata fruits tace “sae dae fa kirjin nn tace bae daina ba, kan ma ynxu take ce min ya fara mata ciwo,” yace “ae dama ba lkci daya ciwon kirjin xae daina ba, anjima xa a shigo mata allura a kuma bata drugs, Allah ya sauwake” yana kai wa nn ya fice daga dakin, last floor ya haura ya nufi wani office, ya kwankwasa kofa aka masa ixinin shigo wa ya bude kofar ya shiga da sallamarsa, yana xaune kan daya daga lafiyayyun kujerun office dinsa rike da jarida a hannu, Ameesha kuma na xaune kan office chair dinsa tana danna laptop, Khaleel ya gaishesa cike da ladabi, ya amsa tare da cewa “yhu re off knn” Khaleel yace “eh dad amma kila in dawo can da daddare,” juyawa yyi yana kallon Ameesha yace “baki tafi gida ba dama” Ameesha ta rufe laptop din gabanta tace “dama kai nake jira Dr, drop me” Dakewa Khaleel yyi tare da kirkiro murmushi yace “ni cikin gari na nufa ynxu driver ya kai ki kawae” kmr xatayi kuka tace “plss mana” bata jira me xae ce ba ta mike da sauri ta dauki dan farin mayafinta tayi roll dinsa kan farin uniform din jikinta snn ta figi Jakarta ta dauki laptop dinta tace ‘bye dad sae ka dawo” Abban nata yace “yau dae ba aiki kika xo yi ba pretty,” juyawa Khaleel yyi ran sa a bace ya fice daga office din, yana gaba tana biye da shi a baya da sauri yake tafiyar tasa, hkn yasa ta kirasa kmr xata yi kuka, ya xabga mata wani mugun harara ya karasa parking space Inda motar sa yake, Sosae jikinta yyi sanyi ta shiga binsa a sanyaye, yana isa gun motar sa ya saka hannu xae Ciro makullin mota a aljihu yaji takardu, fito dasu yyi yana kallo da dan mamaki sae a snn ya tunasu receipt din daxu da ya tsinta, yyi tsaki ya cukuikuye su ya jefar, Ameesha da ke tsaye dan nesa da shi tace “kasan me ya Khaleel, na manta xan tafi gun frnd dita ka tafi kawae” tana kai wa nn ta juya da sauri ta nufi gate, ya bita da kallo snn ya kauda kansa ya bude motarsa xae shiga idonsa ya sauka kan takardun da ya jefar, karasawa yyi ya duka ya kwashi takardun kuma snn ya shiga motarsa ya tada ya fice daga asibitin bayan an bude masa gate, a hankali yake tukin har ya iso Ameesha dake tsaye bakin titi tana jiran abun hawa yyi parking ya xuge glass yace “shigo mu je” xata yi magana ya daura yatsunsa kan lips dinsa alamar kar tace komae, a hankali ta bude motar ta shiga ya ja motar suka bar wajen.
[10/14, 3:26 PM] ‪+234 806 484 7850‬: ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar
7…..
Karfe hudu saura na yamma Khaleel yyi parking motarsa dae dae gun da aka masa gyara jiya da safe, masu gyaran motar suka karaso ya fito suka gaisa suna tambayarsa ko gyaran ne bae yi ba still, Khaleel ya fito da takardun hannunsa xae yi magana knn ya hangota ta fito daga wani mota da yyi parkin gefen titi, tana gyara mayafin dake kafadarta rike da jakarta ta kulle kofar motan, kallonta kawae Khaleel yake ko kiftawa baya yi, wani hadadden guy ne ya fito daga bangaren maxaunin driver, ita ko tuni ta fara tafiya saman layin, sunanta ya shiga kira ta juya a dan fusace tace “don Allah kar ka jawo min attention nn ni dae, nace maka sae gobe” tana kae wa nn ta yi gaba, yyi murmushi yana shafa sajensa, Khaleel yyi tsaki ya juya yana kallon kanikawan dake jiran jin me ya kawo sa yace “xan dawo gobe ma dae” yana kai wa nn ya shige motarsa ya bar gun. Ashnaah ta gama fesa turarenta na biyar snn ta dauki mayafinta ta yafa ta juya tana kallon inna da ta saki baki tana kallonta tace “inna gidan kawata xan tafi ynxu, ko da Allah xae kawo Abba kar fa kice masa na dawo daga sch fa” inna tace “to da magariban nn xaki gidan kawa Takwara” Ashnaah ta hade rae tace “karfe biyar ne magariba inna, ni dae na tafi ba dde wa xan yi ba” tana kai wa nn ta fice, dae dae bakin kofa suka ci karo da Abbanta, gabanta yyi mugun faduwa yana kallonta yace “ina xa ki?” Ta fara Kame kame, ya daka mata tsawa ta juya ta koma ciki da sauri, Abba ya shigo falon yana mata mugun kallo yace “wa ke dawo dake gida kusan kullum a mota Fateemah?” Ta tsorata ssae cikin rawan murya tace “ni Abba?” Inna ta mike tsaye a fusace tace wani munafukin ya gaya maka hka, ohh jita jitan Mara su aikin yin yan unguwan nn xaka dauka ko, to ko ma wani magulmacin ya gaya maka ka koma kace masa baxae taba albarka ba a rayuwa indae har jikata xae kafa ma ido.” Abba ya kirgo dubu goma ya ajiye mata yace ” ni xuwa gobe xan tafi Abuja kila inyi wata daya ko ma fin hka” ya juya yana kallon Ashnaah yace “ki same ni gida anjima” yana kai wa nn yyi ma mahaifiyarsa sallama ya fice, Ashnaah ta fashe da kuka ta xube kasa, inna tace “meye abin kuka, ae bbu Inda xa ki,” Ashnaah ta mike tana ci gaba da rusa kuka ta shige daki. Washegari da sassafe Ashnaah ta gama shirin makaranta ta bar gida, sae da ta fara biyawa gidan Abbanta don amsa kiran sa, yana breakfast ta shigo gidan, hkn yasa ta nufi dakin momynta, ta sameta xaune ta gaisheta, bbu yabo bbu fallasa ta amsa, Khadija ce ta shigo dakin da shirin makaranta ta ce “lah Ashnaah yaushe kika xo?” Ashnaah tace ynxu, Khadija tace “Mami ni xan tafi” Ashnaah tace “jirani mu Fita tare” Abba na gama break fst Ashnaah ta tafi falo tare da Khadija, Abba na rufe jakar laptop dinsa da xae yi tafiya da, Khadija ya kalla yace je kira min Mamarku, ta juya ta koma sama suka sakko tare da ita, suka shigo falon suka xauna, tuni gaban Ashnaah ya fara bugawa don bata san me Abbanta xae gaya mata ba, dama kullum ita cikin laifi take gashi an samu Wanda ya kuma kawo masa gulmanta, ta juya ta
kalli ‘yar uwarta dake kallonta ta galla mata Harara ta dauke kanta.
[10/14, 3:26 PM] ‪+234 806 484 7850‬: ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar
8…..
Kujera ya ja kusa da gadon da take kai ya xauna yana kallonta, hawayen da ya ki tsaya mata kawae take share wa, yace “to ki bani dalilin da yasa baki son Wanda ake son hada ki da,” da kmr baxata ce masa komae ba sae kuma ta tsayar da kukan da take murya can kasa tace “sbda nasan ba sbda Allah yake so na ba,” Khaleel ya kau da kai yana murmushi yace “to sbda me yake son ki” kin cewa komae tayi sae wani sabon hawayen da ta shiga yi, yace “ki daina stressin kan ki da kuka” bata ce komae ba sae kokarin daina kukan da tayi, yana kallonta yace “yaushe ne bikin naku?” A raunane tace “saura sati uku” Khaleel yyi shiru yana kallonta snn yace “amma mijin naki ya xo duba ki kuwa?” Cikin kuka tace “ni ba mijina bne kuma ban gansa ba wae yana Egypt” Khaleel xae yi magana aka bude kofa Ameesha ta shigo rike da faranti silver Mae dauke da allurori da wasu magunguna, da fara’arta t karaso kusa da gadon tana cewa “ya jikin Zeenah?” Zeenah ta dan yi murmushi tace “da sauki” ko kadan Ameesha bata lura da cewa Khaleel bane xaune kusa da ita don yyi backin kofar ne, ya juya yana kallonta yace “Ashe baki tafi ba” da sauri Ameesha ta juya tana kallon Inda yake da mamaki, juyawa tayi tana kallon Zeenah, snn ta kuma kallonsa, kirkiran murmushi kawae tayi tace “uhm ban tafi ba,” tana kai wa nn ta ajiye farantin hannunta ta juya ta fice da sauri, Khaleel ya bi ta da kallo, snn ya ci gaba da yi ma Zeenah tambayoyin da yake mata, ba shi ya bar dakin ba sae kusan karfe shidda na yamma bayan ya kira wata nurse ta yi mata alluran da Ameesha ta shigo da ta bata magungunan ma. Khaleel na Fita haraban asibitin ya ga motar Ameesha, duk a tunaninsa wucewa tayi, yyi tsaki a xuciyarsa yace kin gamu da wahala yarinya ko kadan mata marasu class basa burgesa gashi har yau bae hadu da mace mai class irin Nasa ba, gun motarsa ya nufa ya bude ya shiga ya tada ya bar asibitin. Sae dae ya fara yin maghrib a hanya snn ya iso gida, bbu kowa falonsu sae TV dake aiki, ya na haurawa sama suka kusan cin karo da Meenah tayi baya da sauri ta bi gefensa xata wuce ya fixgota yace “me ya kawo ki gidan nn” duk da ta tsorata amma bata nuna masa ba ta dake tace “wnn kuma naga ae ba matsalarka bace ya Khaleel” matse ta yyi a bango tayi yar kara hkn yasa ya saketa da sauri ya buge mata baki snn ya shige dakinsa, tace “Allah ya Isar min, mugu kawae” tana kai wa nn ta sauka kasa da sauri. Khaleel na kwance dakin mum dinsa da daddare, tace dama ina son muyi wata magana Khaleel, Khaleel ya Mike xaune yace ” ina ji Ummi,” sae da ta gama abinda take snn ta juya tana kallonsa tace “kan Ameesha ce Khaleel, kai ma kan ka kasan irin son da take maka ba sae na gaya maka ba dae ko” nn da nn Khaleel ya hade rae yana kallonta yace “so na kuma Ummi,” ta hararesa snn ta ci gaba da maganarta,”daxu ta xo ta same ni tana kuka……” Mikewa Khaleel yyi ransa a bace yace “tace miki me Ummi, ni fa wllh bana sonta, bata kuma kai matsayin in so ta ba, me xanyi da macen da bata da aji” yana kai wa nn yace sae da safe Ummi, snn ya fice daga dakin. Yana komawa daki ya shiga Neman layinta ransa a bace amma duk bae samu ba, hkn ya kuma bata masa rae, kulle dakinsa yyi da makulli snn ya dauki makullin fridge dinsa ya bude ya Ciro wine ya xuba a cup ya shanye nn take,sae da yyi hkn kusan sauri uku snn ya fada kan gado yyi ruf da ciki ya lumshe ido, mikewa yyi bayan kmr minti biyar ganin bacci na son daukesa ya shiga bayi ya wanke bakin sa snn ya fito ya isa kusa da bedside lamp xae kashe ya ga takardun da ya ajiye tun shekaranjiya a gurin, dauka yyi yana kallonsu, lkci daya fuskar Ashnaah ta dawo masa, xaunawa yyi yana rewinding din abinda ya gani shekaranjiya, wallet dinsa ya dauka ya linkesu ya saka su ciki don kar ya manta gobe. Washegari karfe biyu da rabi ya bar office ya nufi cikin gari, ba gun masu gyaran mota ba yyi parkin dis tym around, gama parkin dinsa ke da wuya ya Hangota tana fitowa daga layin nasu da hijab dinta har kasa, fitowa yyi daga motar ya tsaya dai dai inda yasan xata bi har ta karaso snn yace “Hey minti biyu” juyawa tayi da dara daran idonta tana kallonsa, shi ko ya hade rae don tunda yake bae taba tsayar da mace ba, kai hasali ma bae taba fara yi ma macen da bae sani ba mgna, ta wani hade rae tana masa mugun kallo daga sama xuwa kasa tace “da wa kke”
[10/14, 3:26 PM] ‪+234 806 484 7850‬: ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar
9…..
Da mamaki Khaleel ke kallonta, ya karyar da kai yana mata wani irin kallo yana nuna ta yace “da wnn abun nake” wani matsiyacin kallo tayi masa ta ja tsaki tace “kan ka ake ji” xata canxa hanya ya kuma shan gabanta, a fusace tace “dalla Malam ka bani hanya in wuce ko kana hauka ne” ya wara ido yace “ni din ke hauka,” tsaki tayi ta juya a fusace xata koma Inda ta fito ya fixgota da karfi yace “ni kika ce ma mahaukaci?” Bae rufe baki ba ta sauke masa mari, ya sake ta a hankali yana kallonta da mugun mamaki, tuni kallo ya dawo Kansu, tana hararansa tace “kadan ka gani” juyawa tayi abunta da sauri ta bar gun ta koma gida. A fusace ta shigo gida ta cire hijab din jikinta ta jefar kan kujera, inna tace “me ya faru kuma” labarta ma inna abun da ya faru tayi inna tace “kin min dae dae da hudu kika yi masa Marin ma” a guje Khaleel ya shigo compound dinsu da motarsa ya bar sa nn tsakiyar gidan ya fito ya rufe motar ba tare da ya sa mata key ba ya shige gida, dakinsa ya nufa ya fada kan gado yyi rub da ciki ya rumtse ido xuciyarsa na ci gaba da tafarfasa, bayan minti goma da shigowarsa aka bude kofar dakin a hankali, ya bude idonsa da sauri ya juya don ganin wnda ya shigo masa, Ameesha ce ta shigo dakin da sallamarta ya Mike tsaye da sauri ya karasa Inda take ya fixgota a fusace yace “wae ke me ke kawo ki gidanmu” a dan tsorace tace “ni gun Ummi nake xuwa ya Khaleel,” Mari ya xabga mata yana huci yace “kike ce mata me?” Bae jira me xata ce masa ba ya tura ta da karfi, ya nufi bathroom, sae a snn ya ji sanyi a ransa, xuciyarsa ya daina masa xugin da yake masa da, shower ya sakar ma kansa a bathroom, bayan minti kusan ashirin ya fito yana goge gashin kansa da towel ya xauna kan gado fuskar nn tasa bbu annuri, ya bude fridge dinsa ya Ciro wine dinsa ya kulle kofar dakinsa snn ya kafa kwalban a baki, sae da ya kusan shanyewa snn ya ajiye kwalban ya dafe kansa, ya kai minti goma a hka snn ya juya ya fada kan gado sae bacci. Ba shi ya tashi ba sae kusan magrib, shima Ummi ce ke ta buga masa kofa tana kiran sunansa, ya mike xaune yana kallon agogo, tashi yyi ya dauke kwalban wine din da yasha ya mayar cikin fridge snn ya bude mata kofar. Karfe takwas da kusan rabi Khaleel ya sakko downstairs sanye da jallabiya milk colour yana rike da makullin motarsa ya karaso cikin falo yace ma Ummi dake binsa da kallo “xan je gidan su Ameesha Ummi sae na dawo” tayi masa Allah ya kiyaye snn ya Fita. Tuki yake amma bbu abinda ke masa yawo a kai sae abinda ya faru daxu, yyi murmushin mugunta yana shafa sajensa yace “Amazing” Mai gadi ya sa yyi masa sallama da Ameesha, duk da ya shiga compound din nasu, mai gadin ya dawo yace ya bada sakon, horn aka yi mai gadi ya bude da sauri sae ga Mahaifin Ameesha ya shigo, Khaleel bae ji ddin hkn ba, amma dae ya fito suka gaisa da Boss din nasa, Alhajin yace “ya baka shiga ba Khaleel sae kace wani bako” Khaleel yyi murmushi yace “ae tana fitowa Abba” komawa yyi cikin mota bayan wucewar aminin dad din nasa, amma wnn karan back seat ya shiga, a hankali take tafiyar har ta karaso gun motar snn ta tsaya, ya bude motar yana kallonta ta dauke kai, da gninta kasan ta ci kuka, wayarsa ya shiga ring ya duba ya ga Abbanta ke kiransa, ya daga, Abban nata yace”khaleel ka dan je clinic ka dauko mata magani don Allah wae cikinta ke ciwo.” Khaleel ya kuma kallonta snn yace “to Abba.” Ya kashe wayar.

See also  Maimoon Hausa Novel Complete

~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar
10…..
Shiru Zeenat tayi tana kallon Khaleel a dan tsorace, yace “yes dats d only way out, in ba dae ki fito da wanda kike so ba sae in san ynda xanyi convincing din dad dinki ya fasa hada ki da wanda ba kya so din ba” A sanyaye tace “to doctor Momy na fa ni dae ina sonta ssae” yace “daga baya we let her knw everythin” Zeenat na share hawayenta tace “am greatful doctor” yace “Neva mind” snn ya fice daga ward din ta bisa da kallo, Allah kadae yasan abinda take kitsawa a xuciyarta, shigowar kannin mum dinta ne ya dawo da ita daga duniyar tunanin da ta tafi, ta sakar masu murmushi suka ce to ki tashi gimbiya an sallamemu, wanda ya shigo bayansu yasa ta hade rae, ya karaso kusa da ita da damuwa yace “sannu prettyna an sallame mu” harara ta galla masa ta mike da sauri ganin yana kkrin daga ta, ta figi hijab din ta tasa ta bi bayan wasu daga kannin mum dinta da suka fita da kayayyaki hannunsu, harabar hospital suka yi ido hudu da Khaleel dake xaune kan farar kujerar roba da wani frnd dinsa, Zeenat ta sunkuyar da kanta, Khaleel ya bi gayen da Zeenat tace shine wanda ake son hadata da kallo, yyi murmushi, yan uwanta suka yi masa sallama da godiya snn suka nufi parkin space inda motarsu yake, bin Zeenah yyi da kallo har ta isa gun mota, abokinsa na dariya yace “kai wnn kallo hka Khaleel, habit din nn naka dae baka bar shi totally ba knn” Khaleel yyi murmushi yana shafa sajensa yace “yarinyar tayi ne, ga ta doguwa ga shape ga diri, ga ga… Infact komai yaji” sae kuma ya tabe baki yana girgixa kai yace “amma sae dae baka ce” dariya abokinsa ya dinga yi yace “I knw yhu can Neva Change from hu I knw yhu Khaleel” Khaleel ya mike yana yar dariya yace “wllh Khaleel ya canxa” abokinsa ya rikosa yace “wait Khaleel wae ya maganar auren ka? Ka samu mata kuwa? Khaleel ya koma ya xauna yace ” ina fa, frnd na rasa ynda xanyi da parent dina” frnd din nasa yace “to ko baturiya kke son aura” Khaleel yace “ae baxa su bar ni ba, amma hkn bayi niyya da” abokin yace “to wae in tambayeka mana Ameesha fa, naga she is very beautiful, educated, in fact….” Katse sa Khaleel yyi a fusace yace to kai ka aureta mana, Allah ya tsareni auren macen da bata da class” Abokinsa yace amma ka mata shaidar karya, yarinya da ko kallon namiji bata yi amma don tana sonka sae kace bata da aji,” Khaleel ya mike yace “kaga ni na koma office” yana kai wa nn yyi gaba. Khaleel ne xaune ran Sunday da frnd dinsa a gidan wani abokinsu, ya Kai karshen lbrinsa yana murmushi ya dauki kwalban wine din gabansa yana sha, duk suka yi tsit suna kallonsa kowa da mamaki bayyane a fuskarsa, mikewa Najeeb yyi yana tabe baki yace “amma ka bada maxa Khaleel, na sha surprise dinka, duk wnn ajin naka da Kyan ka, da kudin ka da iliminka da wayewar ka mace ta mare ka ka kyaleta??? Yhu let her go scot free? Just like dat” murmushi kawae Khaleel yake, duk abokan nasa suka masa caa da surutu ko wannensu rae a bace” sae da ya bari suka yi shiru don Kansu snn yace “nima har kun bata min rae tunda kuka iya mance wanene Khaleel, an gaya maku Khaleel xata Mara ta tafi scot free” Abdul ya mike yace “nonsense, after she’ve disgraced yhu in public and yhu let her go, me kuma kke tunanin xaka mata da xa ka burge?” Dariya duk frnds dinsa suka dinga yi, ya daga kai yana kallonsu yace ae abinda xan mata sae ya sa ta
yi da ta sanin haifota da uwarta tayi duniya, ni ina da reason dina na kyaleta. Najeeb ya bushe da dariya yana nunasa yace “ya wuce kace xaka yi rapin dinta ko kuma ka sa a xuba mata acid, ko a nakasata, kai dae nasan baka kisa, dats d only thin yhu can do, nothing more then dat, kuma still baka burge mu ba, yarinya ta sa hannu ta sharara maka mari ka bar ta ta wuce baka babbala bnxa ba mu ga wanda ya tsaya mata, nayi mmkin canxawar ka lkci daya, ni kam bn ji ddin dawowarka Nigeria ba Khaleel, kawae an bata maka rayuwa ne, iyayenka basu maka adalci ba.” Dariya kawae Khaleel yake yana rike da kansa, ya mike yana kallonsu yace “da kun san abinda na tanadar ma yarinyar nn ko, da ta Baku tausayi” yana kai wa nn ya mike ya fice daga falon rike da makullin motarsa.

See also  Yar Malam Taki Halin Malam Hausa Novel

~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar
11.. Shiru yyi yana kallon small mum dinsa da ta bude baki da mamaki tana kallon sa, can tace “lallai ma Khaleel, sae yau nasan baka da tunani kasan hukuncin abinda kke shirin yi kuwa” Khaleel yace “bbu wani hukunci mum, Kinsan abinda ke iya faruwa da yarinya nn idan ban yi hka ba” Tace “to ina ruwan ka, ka fi iyayenta sanin abinda su ke yi ne” Khaleel ya sassauta murya yace”don Allah mum ki fahimce ni, wllh in kin ga yarinya nn sae ta ba ki tausayi, mu hadu mu ceci rayuwarta plss” da kyar Khaleel ya shawo kan ta, can bayan dan shirun da tayi tace “to shkkn amma ni dae ba ruwana” yyi dariya yace “dama mana, ruwana kadae ne ki kwantar da hankalin ki mum,” tace “Atoh” sallama ya mata yace da yamma xae dawo snn ya bar gidan. Ashnaah na xaune a aji da frnds dinta bayan sun gama lecture tana basu lbrin abinda ya faru shekaranjiya tsakaninta da Khaleel, duk suka tsaya kallonta baki bude, Maryam tace “kika maresa Ashnaah?” Ashnaah tayi yar dariya tace “kuna mamaki ne, dan dae hannu baya magana ne da ya Baku lbri” duk suka kwashe da dariya amma bnda Nafeesa da tace “to ki dae bi a hnkli, don in kin mari wani kin xauna lfya to wani ba kyaleki xae yi ba,” Ummi tace “to wnn din ma ca yyi maku kyaleta yyi, ba dae ya ga layinsu ba kawae dae Allah ya tsare” Ashnaah tace “to uban me xae iya min? In Baku da abin fadi kuyi shiru pls kar Ku bata min rae, ya dde bae min abinda xae yi ba” Duk suka yi shiru Nafeesa ta mike tace “ki dae bi a hankali” tana kae wa nn ta fice, Ashnaah ta bi ta da masifa wae aniyarta ya bita, canxa hira kawayen nata suka yi, Maryam tace ” wae ina saurayin nn naki me kawo ki makaranta Ashnaah” Ashnaah tace “uhn ki bari kawae akwae abokan babana masu lecturing a nn duk abinda nayi ana kae masa info, hka ma layin grandmum dita, shine ranan Abba ya kirani wae daga ynxu ya sake gani na da saurayi ko ma wani iri ne shi to aura Min shi xae yi tunda ba karatu nake son yi ba, Abbana kuma baya magana biyu shiyasa na ji tsoro don ni ban shirya aure ba, ina abun aure a jikina ynxu ni kam, ynxu dae ko xa mu hadu da Uthman a eatry Muke haduwa don ko layin mu ya daina xuwa, shiyasa nayi ma gayen nn abinda nayi masa, amma da don haduwa ya hadu kuma courage dinsa ya burgeni ssae,” duk suka kwashe da dariya, Ashnaah tace “eh mana ni dae ina son in yi karatu ssae daga fara remedial kawae sae a aurar dani ko Jami’an ma ban Shiga ba,” karfe shidda Khaleel yyi horn gidan small mum dinsa mai gadi ya bude gate ya shiga yyi parkin snn ya juya yana kallon Zeenah da tayi jigum yace “mu shiga” ba musu ta bude mota ta fita shima ya fito ya kulle motar yace “to ae sae ki cire nikaf din” ba musu ta cire, da ganinta kasan a tsorace take, tana biye da shi a baya suka shiga gidan, bbu kowa falon sae Tv dake aiki, ya nuna mata kujera ta xauna snn ya haura sama, tare suka sauko da mum, ta karaso cikin falon tana amsa gaisuwar Zeenah, Meenah ce ta sakko Mum tace Ku tafi sama da ita Amina, Meenah tace “to mu tafi,” Zeenah ta mike suka nufi sama tare, har sun fara hawa stairs mum tace Amina ba ki ga Khaleel bne?” Meenah ta juyo tace “au Ashe shine, ina yini ya Khaleel?” Khaleel ya dake yace “qlau” snn suka wuce sama. Yau ma kmr jiya Khaleel ya iso anguwarsu Ashnaah yyi parking yana bin anguwar da kallo a xuciyarsa yana addu’ar Allaah yasa kar yyi wahalar bnxa kmr ta jiya.

~Dr Khaleel~ 12 By Khaleesat Haiydar
Khaleel yyi murmushi hangota da yyi tana Tahowa daga layin da ke ranan lahadi ne layin shiru bbu mutane, mayafi ne yafe jikinta yau, ya kafa mata ido har ta karaso titi ta tsaya daga gefen motarsa ta tsayar da abun hawa ta hau, tada motarsa yyi ya hau kan titin ya bi bayan napep din da ta hau. Bae wani sha wahalan bin napep din ba don bbu motoci ssae kan titin, Tafiyar minti kusan goma suka yi keken ya sha kwanan wani layi shima ya bi bayansa, dai dai gate din wani duplex mai napep din ya paka, Khaleel yyi parkin dan nesa da gidan, Ashnaah ta fito ta mika masa kudinsa ta shige gida abunta. Khaleel ya fito yana kallon mai gadin dake xaune bakin gate ya karasa ya gaishesa snn yace “wnn yarinyar da ta shiga nan ne gidansu” mai gadin yace “eh nan ne” Khaleel yace “ok, mai gidan na ciki ne?” Mai gadin yyi shiru snn yace “da matsala ne” Khaleel ya girgixa kansa yace “ko daya, kawae na xata sa ni a kwana tayi da tace nn ne gidansu, ynxu dae ka min sallama da mai gidan in yana ciki” Mai gadin ya mike ya shiga ciki, Khaleel ya xauna yana murmushi, ba a dau lkci ba mai gadin ya dawo ya masa iso har balcony ya nuna masa kujera ya xauna snn ya koma bakin aikinsa, bude kofar falon aka yi wani mutumi da baxae wuce shekaru hamsin ba ya fito yana kallon Khaleel ya basa hannu Khaleel ya ki amsa ya sunkuyar da kansa snn ya gaishesa da ladabi, Mahaifin Ashnaah ya xauna snn ya shiga tambayarsa daga ina, Khaleel yyi shiru yana kkrin tuna sunan da ya gani jikin receipt din Ashnaah snn da sauri ya maxa yace “dama tare da Fateemah muke shine tace in shigo in gaida ka,” shiru Abban Ashnaah yyi, sae kuma ya dan yi murmushi yace “to nagode” Khaleel yace “to ni xan koma Abba” Abba ya kuma masa godiya snn ya mike ya bar balconyn Abba ya wuce ciki. Dakin mum din Ashnaah ya nufa ran sa a bace, Ashnaah na kwance tana danna waya, mum dinta kuma na kallon wani program ita da Ashraf, ya tura kofan duk suka juya da sauri, Abba na nuna Ashnaah yace “lallai kin rika Fateema, har ni xa ki turo ma wani ya xo ya gaida ni ko, wato ni kika raina, to daga yau na yanke xuwan ki makaranta a gidan nn, in fact ko nn da gate bana son ki sake fita, wayar Hannun ki kuma Ki kai min shi Daki ynxun nn” yana kai wa nn ya fice daga Dakin, kuka Ashnaah ta fashe da tana kallon mum dinta dake kallonta da mmki, “Ashnaah wa kika tura ma Abbanki” cikin kuka ssae tace “wllh ban sani ba mum,” Mum dinta tace “to daga ina kike ynxu” tace “daga gidan inna wllh nake mum, ni ban turo kowa ba” ta karashe maganar tana kuka ssae, mikewa Mum tayi ta fice daga Dakin, sae kuka Ashnaah take, usman ta kira bugu biyu ya daga a fusace ta fara magana “kai ne ka xo gidanmu yau?” Ya dan yi shiru snn yace “ni kuma?, kin manta ina Abuja?” Kashe wayar tayi ta kuma saka kuka don cikin samarinta Usman kadae ne yasan gidansu, kashe wayar tayi gaba daya don ma kar ya kuma kiranta, mum ta dawo ranta a bace tace “ki bar dauko min mgna Ashnaah, mahaifin ki gani yake kmr ni ke xuga ki ni fa ba ruwana ynxu gashi ni ma kin ja min, in kuma auren kike so to ae shkkn.” Kuka kawae Ashnaah take duk jikinta yyi sanyi, to waye wnn yyi mata hka, gashi Abba ya dakatar da ita daga xuwa makaranta. Har Khaleel ya isa gida murmushin dake dauke a fuskarsa tun bayan fitansa gidansu Ashnaah Bae bace ba, falonsu ya shiga ya tarda Abbansa xaune a falo da wani abokinsa, ya karasa cikin falon ya gaishesu, Abokin Abban nasa yace “har yau dae ka ki aure ko Khaleel ga Ma’aruf ynxu ‘ya yansa har uku, Khaleel yyi murmushi yana shafa kansa yace ” ni ma na kusa Abba, in Allah ya yrda watan da xa mu shiga” Abbansa ya sace kallonsa , Khaleel yyi dariya yace “Allah kuwa Abba na samu mata ynxu” Abban nasa yace “to Allah yasa” mikewa yyi ya masu sallama xae haura sama announcement din da ya ji ana yi a Tv yasa ya juya da sauri yana kallon tvn, murmushi yyi ganin hoton Zeenah boldly kan screen din Tvn snn ya haura sama. Satin Ashnaah biyu a gida bata je makaranta ba duk ta fice hayyacinta ta xama abun tausayi ga shi Abba ya amshe mata waya, duk irin lallaba Abba da mum dinta ta dinga yi tana basa hkuri hkn vae sanya ya canxa hkuncin da ya yanke ma Ashnaah ba don Bae yrda bata san daga inda mutumin yake ba, wani amininsa mum ta kira tayi ma bayanin komai don har inna ma yaki saurarenta, ranan da safe aminin nasa ya xo, bayan sun gaisa aminin yasa a kira masa Ashnaah, ta shigo falon da hijab dinta har kasa ta durkusa ta gaida abokin Baban nata, shi dae Abbanta Bae ko kalleta ba, Alhaji Salisu yace “Ashnaah me yasa Baki jin maganan iyayen ki ne?” Kasa cewa komai tayi kanta a Kasa, fada ya shiga yi mata daga karshe yace bbu ruwanta da ko wani saurayi daga ynxu har sae ta gama karatu, tace “to Abba ngdd” Abbanta yace ” Allah yasa ya shiga kunnenta, so nawa Mike yin hkn da ita, Alhaju Salisu yace wnn kuma tsakanina da ita na Alhaji, tashi ji tafi gobe ki shirya ki tafi makaranta, Ashnaah taji ddi ssae, kuma tayi vow a xuciyarta daga ynxu bata sake kula saurayi, har usman ma ta bar kulasa don bbu abinda take so kmr karatu a rayuwarta. Karfe biyar na yamma Khaleel ya shigo falonsu Meenah, mai aiki kadae ce a falon tana shara, ya xauna bayan ya amsa gaisuwarta yace “masu gidan basa nn ne” tace “Anty Amina da bakuwa ce kadae a gidan, Momy ta fita, sama ya nufa ya bude kofar Dakin Meenah, Zeenah ce xaune gaban madubi tana comb din gashinta da ya kusa bayanta, ta juya da sauri sae kuma ta mike ganin Khaleel ne ta dauki hijab dinta ta rufe kanta tace “ina yini ya Khaleel” yyi murmushi ya amsa yana kallon ta, Meenah ce ta fito daga bayi tace “haba meye hka Ya Khaleel xaka shigo ma mutane Daki ba sallama in mutum bbu kaya jikinsa fa” Khaleel yyi shiru yana kallonta, hararansa tayi ta koma bayi da sauri ta sa key don tasan me xae biyo baya, yyi murmushi a xuciyarsa yace”Allah ya taimake ki yarinya” waya ya Ciro a aljihunsa ya mika ma Zeenah yace “gashi xa mu dinga magana, hope ba matsala dae” ta gyada masa kai ta karbi wayan snn yyi mata sallama ya wuce. Ashnaah ta karasa gun da motar usman yake da sauri a dan tsorace tace don Allah ka dinga rufa min asiri ya usman,ba na maka bayanin komae ba wae, ynxu idan wani ya ganmu ya je ya gaya ma Abbana fa” da dan damuwa usman yace “to ya kike son in yi Ashnaah yau fa sati uku Rabon da in ganki ga shi ke ba waya ba, to a ina xan ganki in ba nn ba” Ashnaah na kalle kalle kmr munafuka tace ka ga mu hadu a eatryn da ka taba kai ni ranan” yace to da yaushe?” Tace “karfe hudu xan bar makaranta sae mu hadu a can kawae, ki ban xo ba ka jirani” yace to ynxu me kike da baxa mu tafi ba, tace tutorial Muke, tana kai wa nn tayi gaba da sauri, shi ko yyi reverse ya bar wajen.

~Dr Khaleel~ 13 By Khaleesat Haiydar
Karfe hudu saura Ashnaah ta bar sch bayan tayi la’asar a mosque, a dai daita sahu ta d auka ta nufi Eatryn da tace Usman ya jirata, bata yi mmkin ganinsa xaune yana jiranta ba, ta ja kujera ta xauna kujeran dake kallon nasa, shi kam sae bin ta da kallo yake, ta dan yi tagumi tana kallon sa, ya sauke ajiyar xuciya yace “me xa a kawo maki,” ta girgixa kai tace “aa ni a koshe nake kuma ban ma dde da shan soft drink ba a makaranta” Bae ce komae ba sae kallonta da yake, hkn yasa tace “ya usman ba laifina bne wllh, Abba baya son ganina da kowa ne, aurar da ni yace xae yi idan ya kuma gani na da saurayi,” Usman yace “to muyi aurenmu mana Ashnaah, wllh ina sonki tsakanina da Allah, xan bari ki ci gaba da karatun ki har kice kin gaji Ashnaah, yhu won’t regret marryin me” Ashnaah tayi masa wani mugun kallo tace “ta baxan yi ba din, yar yarinya da ni xaka wani dinga kira min aure? Am just 17 fa ko ka manta ne xaka dinga ce min aure” kmr xata yi kuka ta karashe maganar. Usman yyi shiru yana kallonta, juyawa tayi da xummar kallon agogon dake manne da bango taga karfe nawa suka yi ido hudu da Abbanta dake xaune da wasu mutane sun kai biyar da gani abu suke tattaunawa, Alhaji Salisu ta gani a gefenta shima yana kallonta, mikewa tayi da sauri kuma a rude ta bar eatry din, usman ya bi ta da kallon mamaki don shi Bae san Abbanta ba, ya mike ya bita da sauri, ko da ya fita har ta hau Napep. A rude Ashnaah ta isa gida ta dinga rusa ma mum dinta kuka, mum dinta duk ta rude tana tambayarta me ya faru hka ma Ashraf, da kyar ta shiga gaya masu abinda ya faru, mum dinta ta mata wani mugun kallo ta fice ta bar mata dakin kawae. Gidan inna ta nufa tana kuka, inna duk ta rude tana tambayar me ya faru, cikin kuka ta yi mata bayani ita ma, inna tace “shine xaki daga hankalin ki uwa kin kashe dan mutum, kai ni fa Adamu ya fara kai ni iyaka, to ya xo nn ya same ki in ya isa in ga, hka kawae duk ya bi ya takura ki don shine ya haife ki” Khaleel ya tsura ma lafiyayyun xannuwan dake kwance cikin akwatin dake gabansa ido snn ya ciro wani blue mai kyau da wani colour daban ya ajiye ma mum dinsa yace “ga wnn ummi” Ummi tace “aa ka bar mata kayanta kawae,” yace “ae ni na baki mum” ya cire wasu uku ya dauki daya yace “ke ma mum ga naki” small mum dinsa tace “aa da ka barsu kawae Khaleel” ajiye mata yyi kusa da ita ya rufe akwatin, Ummi tace “su kuma biyun hannunka fa” yace “Ameesha xan ba daya, dayan kuma ina da warce xan ba,” mum ce ta komar da lafiyayyun akwatunan har shidda inda suke, shi kuma ya fice daga Dakin, mum tayi dariya tace “kai! Allah yyi, sae dae kuma an ki kawo mana ita mu gani.” Washegari lahadi Ashnaah na kwance Dakin grand mum dinta duk ta rasa me ke mata ddi ga shi Abba Bae xo ba har lkcn bare ta ji hukuncin da xae yanke mata , to ko wani hukuncin xae yanke mata wnn karan kuma, wasu hawaye suka shiga gangarowa daga idonta, duk Usman ne ya ja mata komai. Karfe uku na yammacin ranan Abban Ashnaah na xaune falo yana duba jaridar da Bae duba ba da safe mai gadi ya danna kararrawar falon Ashfat ta bude yace da ita ana sallama da Alhaji, ta nufi falo ta ba Abbanta sakon snn ta wuce sama abunta. Mikewa Abba yyi Da yake daga anguwa yake har lkcin manyan kaya ne jikinsa ya fita xuwa gun bakin nasa, mamakin ganin bakin yyi su uku kuma duk Bae san su ba, yyi masu sannu da xuwa snn ya shigar da su har xuwa falonsa aka kuma gaggaisawa, da kansa ya kwaso masu ruwa da lemo a fridge suka masa godiya snn ya koma ya xauna.

~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar
14….
Shiru Abba yyi da mugun mamaki yana kallonsu jin me ke tafe da su, can ganin kar ya maida kansa karamin mutum a gabansu yyi saurin cewa “Eh hka muka yi da ita, amma bn yi tunanin yau xata sa ya turo Ku ba, bari in kira yan uwana ayi komae gaban su kun ga ba dadi inyi komae gaban kai na” suka ce “gskya ne wnn, ba matsala xa mu jira su in Allah ya yrda” Abba ya Mike yana jin jina abinda Ashnaah tayi a ransa, lallai Ashnaah ta fi karfinsa ta nuna masa iyakarsa, wato kan yace mata komae kan inda ya ganta jiya da saurayi bari ta sa a kawo masa gaisuwa, sama ya nufa xuciyarsa na tafarfasa ya shiga dakinsa ya dauki waya ya shiga kiran wasu daga yan uwansa da abokinsa Alhaji Salisu, ba a dau lkci ba duk suka iso gidan, duk suka yi mamakin abinda suka ga Abban Ashnaah na shirin yi kuma ba tare da saninsu ba don Ashnaah yarinya ce karama amma bbu wanda yyi query dinsa ganin bakin, aka yi duk abinda ya kamata bakin suka bada dubu hamsin kudin gaisuwa, suka kuma kirgo dubu Dari suka bada kudin sadaki, suka kuma bada kudin da xa’a siya wasu abubuwan da ya kamata da basu kawo ba, mai gadi aka sa ya shisshigo da akwatunan da suka kawo na gaisuwa, nan take Abban Ashnaah yasa aka sa ranan daurin aure, wata daya kacal, nan da sati biyu kuma xa’a kawo lefe, kallonsa kawae yan uwansa ke yi da mamaki, sae kusan la’asar bakin suka bar gidan bayan sun rakasu har bakin mota ana ta godiya, ita dae Momy tana ta mamakin meeting din da ake yi a fali ba tare da ya sanar da ita xae yi baki ba, ko falo ba su shiga ba daga rakiyan da suka yi Alhaji Salisu yace “ynxu Adamu duk maganar da na maka jiya Ashe baka dauka ba, abinda kayi a tunanin ka ya dace knn, did yhu think dis is d ryt decision” Abban Ashnaah yyi murmushin takaici ya ma rasa me xae ce ma abokin nasa, nan yan uwansa suka hau sa da fada wae ya nuna masu ba su suka Haifa masa Fateemah ba kuma da sun san kiran da ya musu knn da bbu me xuwa tunda lkcn da yace a kawo gaisuwar Bae nemi shawararsu ba, Abba yace “mu shiga ciki in maku bayanin komai, ko kadan banda laifi a nn, hasalima mutanan nn rana tsaka kawae na gansu” nan Abban Ashnaah yyi masu bayanin abinda ya faru tun daga ran da ya hana Ashnaah kula samari har ixuwa yau a cewarsa da ta nuna masa iyakarsa tasa aka kawo gaisuwa ba tare da ya sani ba, duk kowa yyi shiru da mamaki yana kallonsa, Alhaji Salisu yace “anya Ashnaah xata iya hka Adamu, gani nake fa kmr set up ne wnn ni dae, ynxu dae tana ina?” Abba yace “set up fa kace, to ni tun jiya da na dawo gidan nn ban ganta ba tana gidan inna, ae bbu abinda xae sa ni janye ra’ayina na aurar da yarinyar nn nan da wata daya, ba dae aure take so ba, xan aurar da ita” su kam yan uwan Abba Kasa cewa komae suka yi don abun ya daure masu kai. Abba na raka yan uwansa ya dauki wayarsa ya kira Momy tana dagawa yace ta sakko yana jiranta a Kasa, ba a dau lkci ba ta sakko ta shigo falon, ta dinga bin akwatuna da kudin da ta gani da kallon mamaki tace “wnn kuma fa Alhaji” da kyar ta iya masa tambayar don tuni jikinta yyi sanyi, bbu yabo bbu fallasa yace “Ah! yar ki ta turo a kawo min gaisuwa da kudin sadakinta” Momy tace “ya ta kuma?” A tsorace tayi masa tambayar, yyi bnxa da ita ya haura sama abunsa, kuka Momy ta saka tana tunanin anya Ashnaah ce xata yi hka kuwa?. Khaleel ya fada kan gado ya fashe da wata dariya yana shafa kansa snn ya mike xaune da sauri yace “yes! It all worked well at last”. Da kyar Ashnaah ta bude kofar falonsu tana lekan falon, har lkcin jikinta Bae daina rawan da yake ba tun lkcn da kiran Abba ya shigo wayar inna wae yana kiranta hankalinta ya Kasa kwanciya, ta juya tana kallon inna da ke bayanta, inna tace ” mu je mana kin tsaya kmr warce ta ga mugun abu, mu je in ji kiran da yake maki” Ashnaah ta shiga falon inna na biye da ita a baya.

See also  A Jininsa Yake Hausa Novel Complete

~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar
15…..
Khaleel ne xaune office dinsa aka kwankwasa masa kofa ya bada ixini aka shigo wato nurse ta shigo ta gaishesa snn tace “Dr ne yace in kira ka can sama” Khaleel ya gyada mata kai ta juya ta fita snn ya mike ya fita daga office din ya nufi office din dad din Ameesha, yana tsaye Khaleel ya samesa a office din, Khaleel ya xauna snn ya gaishesa, ya juya yana kallon Khaleel snn ya ja kujera ya xauna ya fara magana a nutse “Khaleel don’t tel me that duk son da Ameesha ke maka ynxu baka sani ba,” Khaleel yyi shiru yana kallonsa, ya suke ajiyar xuciya snn ya ci gaba kmr hka “wacce yarinya kke shirin aure ynxu?” Khaleel ya kauda kansa yace “budurwa ta ce mun dde tare” Abban Ameesha ya dan yi shiru snn yace “shknn tashi ka tafi” mikewa Khaleel yyi ya fice daga office din nn da nn ransa ya bace ae ko me xae faru bbu abinda xae sa shi auren Ameesha. Ashnaah na kwance dakinta da daddare bayan inna ta koma gidan ta duk abun duniya ya isheta tun safe bbu wanda ya sake mata a gidan gashi har inna ta tafi Abba ya ki fadin kiran me yake mata, Ashfa ce ta shigo Dakin ta ce mata Abba na kiranta, Ashnaah ta mike da kyar gabanta na faduwa ta sauka kasa xuwa gun abban, Momy ma na xaune falon ta dan rabe jikin kujera tace “ga ni Abba” wasu kudade ta ga ya jefa mata yace “ga kudin gaisuwan da sadakin da kika sa aka kawo ma ni, amma ki sani ko kwandala ta baxae yi ciwon kai ba wnn auren naki, kuma kar ki taba nuna Kinsan ni ki je can ki nemi wani uban, xan maki alfarma daya in daura maki aure amma bayan nn ko hanyar gida na kar ki nuna kin sani, snn bbu me min biki a gidana a je can gidan mijin naki ayi” Tunda ya fara magana Ashnaah ke kallonsa kmr wata wawiya, ko kadan bata fahimce me yake cewa ba, anya ma da ita yake kuwa, juyawa tayi ta ga bbu kowa bayanta ta kuma kallonsa da sauri tace “Abba ban gane ba,” tsawa Abba ya daka mata yace “get out dama bana bukatar ganewarki” mikewa tayi da sauri tana kallon Momynta taga kuka take, sae ita ma ta fashe da kukan tace “don Allah ban gane ba Abba” mikewa da Abbanta yyi yasa ta bar wajen da sauri ta haura sama tana kuka. Ba karamin tashin hankali Ashnaah ta shiga ba bayan Ashfa ta mata bayanin abinda ya faru, ta mike da gudu ta nufi dakin momynta ta dinga rusa mata kuka wae ita wllh bata turo kowa ba bata san ko waye bane Sharri yake mata, Momy taki ko da kallon inda take, hkn yasa ta fice daga dakin ta koma dakinta ta dauki hijab dinta ta sauka kasa da sauri xata gidan inna amma mai gadi yace abbanta yace kar ya bari ta fita, Ashnaah ta rasa me ke mata ddi a duniya sae rusa kuka take ta daura hannu a ka, to waye wnn ke Neman ruin din mata rayuwarta, a ina ta san shi, tasan usman baxae mata hka ba, Allah ma yasa shi ne abun xae fi xuwa mata da sauki, da kyar ta koma balcony ta xube kasa nan tana ci gaba da Kukanta, tana nan har kusan rana mai gadi ya shigo balcony rike da envelop a hannunsa xae danna bell ta mike da sauri ta fixge a hannunsa snn ta shiga duba menene a ciki, IV ta gani gabanta yyi mugun faduwa ta bude da sauri, kan sunanta idonta ya fara sauka snn Khaleel Muh’d, mutuwar tsaye tayi a gurin xuciyarta na ci gaba da nanata sunan Khaleel, tayi wurgi da envelop din hannunta ta fasa wani ihu tayi cikin gida da gudu ta shige dakin mum dinta tana kuka tana cewa “wllh Momy ban sansa ba, ban taba jin sunansa ba, kin ga wae Khaleel, ni tunda aka haifeni ma ban taba jin sunan ba, don Allah Ku ceci rayuwata kar Ku hada ni da shi momy kila ma kudi yake so yyi da ni wllh” kallonta kawae Momy ta tsaya yi ita ma jikinta yyi sanyi, to waye wnn ya xo Neman auren ‘yar ta, tasan ko da wasa ynxu baxata tunkari mai gidan ta da wnn mgnan ba.

~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar
16…..
Ummi tayi shiru tana kallon Khaleel snn tace “to don me baxa su yi taron biki ba Khaleel” Khaleel ya daga kafada yace “basa taron biki wae su,” Mikewa yyi yace bari in je inyi wanka ummi, Ummi tace “to ynxu har biki ya karato baxa ka kawo min yarinyar ba inga” Ya koma ya xauna yace “kar ki damu ummina har sae kin gaji da ganinta, bana son tana fita ne ynxu, kwana nawa ne ya rage ki kwantar da hankalin ki” Tace “to Allah sa ayi a sa’a yasa tsohuwar gida ce” ficewa Khaleel yyi Bae ce komai ba. Ana ta shirye shirye gidansu Ashnaah don yau kwana biyar ya rage a daura mata aure, mamaki kawae take wae ita xa ayi ma aure, wae yaushe tayi birthday dinta na shekara sha bakwae ne ma dae, ko wata biyu ba ayi ba, shine wae xa a mata aure da wanda ma bata taba jin sunansa ba a cewarta, tunanin hkn nasa ta kukan takaici, Abba kam ca yyi bashi da ko sisin yi mata kayan daki Bae yi wnn budget din ba na wnn watan, takaici yyi ma Momy yawa ta rasa ynda xata yi, har da xata hadasa da mahaifiyarsa sae gashi amininsa da yayansa sun mata iya ynda xa su iya, da ka ga inna kasan tana cikin farin ciki, ita dae ayi a daura aure a fitar da jikarta waje, ko kadan bata ko maganan mijin da aka ba jikar ta ta. Ranar Juma’ah bayan an sauko daga masallaci aka daura auren Khaleel da Ashnaah, daurin auren da ya samu hallatar jama’a da dama, Khaleel ya nufi motarsa yana murmushin da shi kadae yasan dalilinsa bayan ya gama gaisawa da mutane da dama dake masa Allah sanya alkhairi da fatan xaman lfya da amaryarsa, frnds dinsa suka bi sa suna kiransa da ango cikin xolaya, ya hade rae yace “irin wnn wasan ne kuma ban so, Ku bari ran da na xama angon kwa kirani da hkn” ba su bar tsokanansa ba har suka bar wajen da motarsu, Najeeb yace “bari mu je mu dauko amaryarmu tunda ba biki.” Ashnaah ta mike tsaye da kyar ta dauki lafiyayyan lace din da kanwar mum dinta ta fito mata da ta sa, kkrin mayar da hawayen idonta take, taki barin Antyn ta dake ta lallashinta tun jiya ta gani don ta mata alkawarin daina koke koken da take, bbu abinda ta sa a cikinta ranan sae dan tean da aka tilastata ta sha, ba a wani yi mata make up ba ranan gaba daya, kawayenta na makaranta duk suka ji tausayinta, kowannensu na tunanin in shi ne aka ma hka ya xae yi. Karfe shidda saura Ashnaah ta sauka kasa da mayafi lullube fuskarta xuwa falon Abbanta kmr ynda aka umarceta, kallo daya ya mata ya dauke kansa, ta karaso a sanyaye ta durkusa gabansa ta shiga xubda a hawaye cikin rawan murya tace “don Allah don annabi Abba kayi hkuri ka yafe min,” kasa ci gaba tayi ta shiga rusa masa kuka ta kife kanta kan kujerar da yake xaune, ya cire glass din idonsa yace “tashi ki je Allah yyi maki albarka ya Baku xaman lafiya ke da mijin ki” Kasa dago kanta tayi hawaye na ci gaba da xuba idonta a raunane tace “to Abba karatuna fa” da kmr baxae ce komae ba sae kuma yace “da kina son karatun kika xabi aure” ta dago kanta da sauri cikin kuka tace “wllh Abba sharri aka min ni bance kowa ya turo ba, ka yrda da ni” Abba na kallonta yace “sharri aka maki?” Ta gyada masa kai tace “eh Abba ni ban turo maka kowa ba wllh”

 

[10/10, 6:36 AM] ‪+234 701 117 6189‬: ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar
17…..
Abba ya tsura mata ido snn yace “to wa ya turo sa” Ashnaah ta shiga share hawayen fuskarta tana girgixa masa kai tace “wllh Abba ban san wanda ya turo sa ba, ni ban san shi ba, ban san daga ina yake ba,” tsawa Abba ya daka mata a fusace yace “ni kike ce ma baki san sa ba” Ashnaah ta fashe da wani sabon kukan tace “Allah Abba ban san shi ba sharri yake min, Abba ya kuma daka mata tsawan yace ” tashi ki ban waje” kin tashi tayi ta ci gaba da rusa masa kuka tana cewa ya yrda da ita, mikewa Abba yyi a fusace hkn yasa ta tashi da sauri ta bar wajen ta nufi sama, kasa komawa ya xauna yyi ya shiga kai koma a falon yana naxarin abinda Ashnaah ke cewa ynxu, wayarsa ya dauka ya kira mum dinta yace ta same shi falonsa, ba a dau lkci ba ta sakko kasa, ya nemi kujera ya xauna yana kallonta yace “A ina Ashnaah suka hadu da wnn yaro da ke shirin aurenta?” Momy tace “sae yau kasan da wnn tambayar?’ Tun da baka yi ta ba sae da aka daura aure, to ko kadan Ashnaah bata san daga inda mutumin yake ba, to da yake na ga Neman Kai kke da ‘yar taka shi yasa ban katse maku hanxarin Ku na aurar da ita ba,” Abba ya Mike tsaye ransa a bace yace “kar Ku raina min hankali, ni xa Ku maida yaro ko karamin mutum, Ku hada baki ke da yar ki Ku xo nn Ku caxa min kai, to bari kiji ko da ma da gsken ne bata san mutumin nn ba wllh wllh bbu abinda xae hanata xaman aure da shi, in an kai ta gidan nasa ma ya yanka ta karewar komae knn, yarinyar da bata dauki maganar uban da ya haifeta a bakin komae ba meye amfaninta, ba abun kunya bane ba ma ace kmr ni ana ganin ‘ya ta gidan cin abinci da holewa da saurayi, da na hanata wnn sae ta koma wancan sbda ta raina ni ke kuma kina kare ta, to ki koma Ki gaya mata plan din naku Bae yi aiki ba,” ya ja tsaki ya ce “mutanan bnxa kawae” dakinsa ya nufa ransa a bace, kan ya shiga ya juya yana kallon Momy da hawaye ya gama wanke mata fuska yace “kar kuma yar nn ta kuskura ta kwana gidana yau, maxa ana magariba a tafi da ita dakin mijinta” yana kai wa nn ya shige dakinsa. Momy ta nufi sama jikinta a sanyaye tana ci gaba da hawayen da take. Dai dai lkcn wa enda suka je yi ma Ashnaah Jere suka dawo kowa na yaba gidan da xa a kaita, kanwar momy ta ja ta xuwa daki tace “haba yaya kukan meye wnn baxa ki daina ba tun daxu, wllh Ki kwantar da hankalin ki, ni na tabbatar maki wnn mutumin ba don ya cutar da ita yyi hka ba, kawae tsabar sonta ne, sae kin ga gidan wllh, Ashnaah ta samu gidan Hutu ni na tabbatar maki yaya,” Momy tace “to da kike wnn maganan kin san aikin da mutumin yake ne” Anty farida tace “wllh likita ne, kuma ma babban likita snn mahaifinsa ma babban dan kasuwa ne, sae ma kinga ynda yan uwansa suka tarbe mu daxu wllh don duk suna gidan, ki kwantar da hankalin ki kawae yaya, ba mutanan bnxa bne” Momy ta share fuskarta tace “to Allah yasa, shi kuma Adam Allah ya shiryesa ya dawo da shi hanya”. Karfe bakwae da kusan rabi aka tafi da Ashnaah gidan mijinta da bata sani, bbu abinda take masu sae aikin kuka a motar, ita takaicin ta bbu wanda ke son yrda da ita idan tace bata san mijin ba, tafiyar kusan minti talatin suka yi kafin suka iso gidan mai gadi ya bude masu gate driven ya ja motar ya shiga ciki ya samu gu yyi parkin, ana bude ma Ashnaah kofa ta fito ta cire mayafin kanta da sauri tana kare ma kantamemen gidan kallo tana huci ae kam mai gidan nn ya aurar ma kansa fitina da tashin hnkli, aka ce ta fito da kafarta na dama bata ko sauraresu ba ta fito da ta hagu abunta kuma da gangan, suka kama yi mata masifa wae bata jin mgna, bata ko kallesu ba ta shiga bin kanwar mum dinta suna biye da su a baya har suka iso babban falon gidan, bbu abinda bbu cikin falon ba jin ddin rayuwa, Antynta ta juya da sauri ganin yan uwan khaleel a falon tace ” ke baki da kunya ko Ashnaah, baxa ki rufe fuskar ba, ” Ashnaah ta wara idonta da mamaki tace “ji Anty fa, akwae me bina bashi a nan ne ya fadi in ji da har xan rufe masa fuska” ganin ynda antynta ke kallonta jikinta yyi sanyi don ba Karamin nasiha aka mata ba kan su bar gida daxu yasa Ashnaah ta daura mayafin hannunta a kanta fuskarta a daure ta rike kugu tana kare ma mutanan dake xaune falon kallo.

~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar
18…..
Mum din Meenah ce ta taso tana kallon Ashnaah duk da jikinta yyi sanyi tace “sannun Ku da xuwa amarya” Ashnaah ta dan yi tsaki ta saki mayafin kanta ta rufe fuskarta da shi, mum din Meenah ta kama hannunta suka nufi sama su anty na biye da su a baya su ma a sanyaye, duk nasihan da aka taru ana ma Ashnaah a Daki kawae shiga kunnenta na Dama yake yana fita ta hagu, duk ta kagu su rabu da ita sae wani kallon banxa take ma Zeenah da Meenah dake dakin su ma suna kallonta, Anty da sauren yan uwan mum duk jikinsu yyi sanyi ssae, ynda kasan ba amarya suka kawo gidan ba ta wani sauke mayafin kanta xuwa kafada tana bin kowa dake dakin da kallo, Meenah da taji kmr ta sake dariyan dake cin ta ta mike kawae ta fice daga dakin Zeenah ta bi bayanta, sae da suka sakko kasa snn Zeenah tace “wnn ita ce amaryar ya Khaleel din wae Meenah” Meenah ta fashe da dariya har da kyakyatawa tace “to gashi kin gane ma idon ki kuwa, dai dai shi ya dauko ma kansa,” Zeenah ta kasa cewa komae tana mamakin duk ajin Khaleel ya rasa warce xae auro sae yarinya karama kuma fitsararriya, Meenah tace “ni dae tace xata kawo min iskanci naka da mata duka xan yi wllh, wnn ta wuce kanwata ta uku ma”. Sae kusan karfe tara duk aka watse aka bar Ashnaah daga ita sae halinta a gidan, nn fa hankalin ta ya tashi ssae ta soma rera kukan da bata yi ba tunda aka kawota gidan, kasa xaune tayi ta mike tsaye ta shiga xarya a dakin tana rusa kuka tana tunanin to yau wani irin mutumi xa su kwana gida daya da, wa ya sani ma ko dan yankan Kai ne, kila yau ma shine rananta na karshe a duniya, tunanin hkn yasa jikinta ya soma rawa ta fara tunanin to ko dae ta gudu ne kawae, tana cikin yanke decision din taji an bude gate din gidan, xuciyarta ya kusa shige wa cikinta son tsoro, wani sabon kukan ta saki ta durkushe wajen ta daura hannunta a ka tana kiran momynta, can kuma ta mike da sauri jikinta na rawa ta nufi window ta ga irinsa kan ya shigo gidan, har ya gama parkin motarsa a parkin space ya nufo kofar shiga gidan, bata ganin komae sae tall figure dinsa don bbu haske tsakar gidan sae daga can bakin gate, wani sabon kukan ta rushe da ta koma gefen gadonta da sauri ta xauna jikinta na rawa. Takun sa da taji a stairs yasa ta gane har ya shigo gidan ta mike a hnkli ta nufi gun inda ta ga switch din wutan dakin cikin sanda ta kashe wutan dakin snn ta koma da sauri ta xauna xuciyarta na bugawa tayi saurin share hawayen fuskarta da Mayafin jikinta, suma ne kawae bata yi ba da taji ya bude kofa Ashe wani kofa daban ya bude, ta sauke ajiyar xuciya, ta xamo kasan tiles a hnkli ta xauna don ji tayi xaman gadon ma ya gagareta, yau tata ta sameta, ko minti biyar bata yi da sauka kasan tiles din ba baccin tsoro ya sace ta nn xaune, a firgice ta farka jin an bude kofar dakin da take, ta ga mutum tsaye bakin kofa kuma har lkcn wutan Dakin a kashe yake, a hnkli ta mike ta koma kan gadon ta xauna xuciyarta na wani mugun bugu da Bae taba yi ba, shi ko har lkcn yana tsaye bakin kofar, sae a snn tayi da ta sanin kashe wutan dakin ko ba komae ae da ta ga fuskarsa ynxu, shknn har ya kashe ta baxata ga fuskarsa ba knn, ji tayi kmr ta sake fitsari ganin da tayi ya rufe kofar dakin, to ko dae ta fara rokonsa ne kawae ya ceci rayuwarta, ko kuma ta saki ihu kawae, duk da ba wuta dakin amma ana iya ganin inda take, karasowa taga yana yi xuwa gun da take, ta mike da sauri ta isa jikin bango jikinta na bari, nan da nan dubara ya xo mata cikin rawan murya tace “wllh xan caka maka abinda ke hannuna in ka karaso inda nake,” tsayawa ta ga yyi cak nn inda yake, ganin hkan yasa ta samu kwarin gwiwa ta ci gaba muryarta a dake tace “in kuma karya ne ka karaso ka ga” komawa taga yyi ya nufi gun switch din dakin nn da nn hankalinta ya tashi ta sake kuka ba tare da ta sani ba ta bi bayansa da sauri muryarta na rawa tace “wllh kar ka kunna min wuta, kana kunna wa xaka sha mamaki,” da sauri ya isa gun switch din ganin tana bayansa, kan ya Kai hannunsa ta wani fixgosa da karfi ya fado kanta duk suka fada kasan dakin, ba ita ba shi kansa sae da ya tsorata, ya tura ta daga jikinsa ta kuma rikosa da sauri cikin kuka tace “wllh na ce kar ka kunna min wuta xan baka mamaki,” kkrin mikewa tsaye ta fara yi ya fixgota ya kai ta kasa, snn shi ya mike ya nufi gun switch din ya kunna da sauri, xae juya suka kuma cin karo don Magyar har ta taso, ta cukumosa ta rufe fuskarta a kirjinsa tana rusa kuka tana cewa “wllh ka mai da ni gidanmu” ita ko kadan bata ma son ganin fuskarsa, duk da irin kamshin da yake ya dan kwantar mata da hankali, tura ta yyi da karfi ya jinginata da bango ynda xata gansa da kyau, amma kememe taki bude idonta.

Leave a Comment

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Scroll to Top