Farin Cikin Rayuwa Complete Hausa Novel

Farin Cikin Rayuwa Complete Hausa Novel

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

Tag:  FARIN CIKIN RAYUWA

 

 

 

*STORY AND WRITTEN*

BY

 

*RAHEENAT M ABBAKAR*

_(Meeraheenat)_

 

 

_Da sunan Allah me rahama mai jin k’ai_

 

 

 

*Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah subhanahu wata’ala, tsira da aminci su k’ara tabbata ga annabinmu, farkon k’aga k’arshen aika wata annabi Muhammad s.a.w*

 

 

*Komai tsanani komai wuya Allah shine abin godiya, bazan tab’a gajiyawa ba gurin fad’in _Alhamdulillahi_ , domin Allah shine ya ara min rai da lafiya har na kawo wannan lokaci, ikonsa ne har yasa na d’aura hannayena da sunan fara rubuta wannan labari, na gode wa Allah na sake gode masa, ya Allah ina rok’onka dan isa da ikonka yanda na fara rubuta wannan litttafi lafiya kasa na kammalasa lafiya, Allah ka saka min hannu kar ka barni da iyawata, ya Allah ka kaifafa tunanina ka tsarkake min harshena, ka nufe ni da rubuta Alkhairi ka hane ni rubuta sharri, ya Allah kasa duk wanda zai karanta wannan labari ya amfana da ko da kalma d’aya ne, ya Allah karka nufe wani da karantawa lokacin ibadunka ameen*

 

 

 

*Tabbas na ga masoyan k’warai, sosai Allah ya nuna min masoyana wanda duk iya wuya muna tare, dama wai haka soyayya take ? Sai kaji ana fad’in ina sonki, ina yinki, kina bada kala, jinjina gareki, ashe wai duk rubutunki ake ma wannan ba ke ba, tabbas masoyi yana nufin wanda zai kasance tare da kai cikin ko wani irin yanayi, wanda zai iya amfani da dukiyarsa k’arfinsa a kanka ba tare da yaji ko d’ar a ransa ba, wanda zai saka farin ciki ko da shi baya ciki, wannan shine ake kira da masoyi, duk wanda ba zai iya cire wani abu daga aljihunsa ya siya wani abu da ka kasa dan ka k’aru dashi ba wannan be cancaci kiran sunansa masoyi ba, dama rubutun namu ake so bamu É—in ba, bana da ra’ayi na siyar da novels É—ina, to amma sai na ce bari na jarabawa masoyana, to adai yi walÆ™iya ta haske idanun kowa, duk ina godiya sosai ga wad’anda suka cire kud’insu su siya novel d’ina, Allah ya bar k’auna na gode na gode, a ci gaba da gashi masoya*

 

 

_Jinjina ta musamman tare da tukwicin ƙauna wanda shi ma yake na musamman ga masoyana na ƙwarai, wanda suka iya cire kuɗin aljihunsu suka sai littafaina, na gode na gode Allah yabar ƙauna, haƙiƙa na amince ku ɗin masoyan Raheenat ce na ƙwarai, kun nuna min ƙauna da soyayya, kunyi haƙuri dani tare da yi min uzururruka a dukkan nawa ta, na gode muku sannan ina yi muku fatan alkhairi a rayuwarku da zuriarku, wallahi har cikin zuciyata nake ƙaunarku kuma nake alfahari daku, ku ɗin kun zamto tamkar ƴan uwana na jini, one love guys

 

 

 

 

Sadaukarwaka ga familyna

 

_Wannan karan sadaukarwar taku ce ƴan uwana abin alfaharina, ko yaushe kuna maƙale a zuciyata kun zamo bugun numfashina, kune ni, ina sonku kuma ina alfahari da kadancewarku ƴan uwana kuma jinina, Allah ya ƙara ƙarfafa mana zumuncinmu ya ƙara haɗa kawunan mu ya kuma kau da shaiɗan a tsakanin mu ameen ya rabbi_

 

 

 

Page 1

 

 

 

 

Kano state 5:30pm

 

Yammaci ne me cike ni’ima sabida iskar da yake kaÉ—awa me daÉ—i, tuÆ™i takeyi cike da natsuwa yayin da karatun Alqur’ani ke tashi a cikin motar Æ™asa-Æ™asa, tuÆ™i takeyi idanunta na zube bisa kwalta, yayin da wacce ke zaune gefenta take waya cikin Æ™asa da sauti fuskarta na bayyana murmushi wanda zai yi maka nuni da tana jin daÉ—in wayar da takeyi É—in, duk da cewa idanunta da nutsuwarta na saman kwalta amma rabin hankalinta na kan wayar da *Zeey* É—in keyi wanda babu abinda wayar ke sakata sai jin takaici, a hankali ta kai hannu ta Æ™ara volume É—in Æ™ira’ar dake tashi a motar wanda dama Zeey É—in ce tayi Æ™asa dashi sabida wayar da takeyi, tana É—auke hannunta Zeey ta kai nata hannun ta Æ™ara yin Æ™asa dashi, da sauri ta É—aga fararen idanuwanta ta watsasu bisa fuskar Zeey É—in tana jifanta da wani kallo tare da sakin tsakin da yayi dai-dai da tsaida motartata da tayi.

 

Ita ma Zeey kallonta tayi tare da kallon inda ta tsaida motar sannan ta dawo da kallonta kanta tana me yin sallama da wanda suke wayar, saida ta É—aura wayar bisa cinyarta sannan ta buÉ—e baki tace “meye na tsaida mu bisa hanya kuma *Maryam* ? Sannan wai meye matsalarki da wayata ce.?”

 

Idanunta na kan Zeey tace cikin wata irin tattausar murya “na tsayar da motar ne dan ki fice min a moto matuÆ™ar zaki ci gaba da wayar, maganar matsalata da wayar ki kuma kin fi kowa saninta, kunnuwana sun gaji da sauraron yaudararrun kalaman ku daga ke har shi wanda kike ikirarin zaki aurar, haba! Duk babu komai a zuciyarku sai Æ™arya da yaudara! Kowa abinda ke zuciyarsa daban abinda bakinsa ke faÉ—a daban! To ni na gaji, in zakuna wayarku ki daina yi a gabana daga yau, in ba haka ba komai na iya faruwa, na tsani Æ™arya wallahi!.”

 

Karanta Littafin Yarima Ashman

Kallon Æ™aramin bakinta da take maganar Zeey keyi tunda ta fara har ta dasa aya, murmushi ta saki me sauti tace “Maryam wai me yasa ke abokiyar adawata ce ne ? Meye na Æ™arya da yaudara anan dan Allah.?”

 

Wani kallo ta jefi Zeey dashi tana sakin wata guntuwar tsaki tace “ai har kullum zan ci gaba da zama abokiyar adawarki matuÆ™ar baki sauka akan wannan banzan aÆ™idar naki ba, Æ™arya da yaudara kuma ai shine abinda ya cancanci kiran kalamanku dasu, domin yaudarar junanku kukeyi akan kuna son juna, kuce dai kuna son abubuwan juna, wallahi ko rantsuwa nayi ba zan yi kaffara ba bakya son Alhaji Ahmed, kuÉ—insa kike so kamar yanda shi ma surar jikinki da kyawunki shine abinda yake so kuma yake ruÉ—arsa, Zainab kullum dai ina faÉ—a miki kuÉ—i ba sune *farin cikin rayuwa* ba, ki tsaya kiyi tunani da kyau.”

 

 

Murmushi Zeey ta kuma saki tana gyara zamanta tace “Diyana tawa, kina bani mamaki wallahi, taya ma zaki ce kuÉ—i basu ne *farin cikin rayuwa* ba, kuÉ—i sune komai Hajiya, in kana da kuÉ—i za kayi komai haka ma zaki iya yin komai, duk wanda kika ji ya ce kuÉ—i ba suyi ba to be san daÉ—insu bane, in kana da kuÉ—i zaka taka wanda ka so kayi abinda ka ga dama babu me tanka ka, yes! KuÉ—in Alhaji Ahmed nake so domin ko yana dasu, na tabbata in na auresa zan huta in fantama yanda nake so, zan hau duk motar da naso na ga dama, sannan in zaga duk Æ™asar da na ke so, na saka suturar da na ke so, na taka wanda na ke so, nayi abinda na ke so, to ki faÉ—a min in ba kuÉ—i ba meye zasu yi min duk wannan.?”

See also  Furara Danko Part 2 Hausa Novel Download

 

Numfashi Maryam ta sauke tana sakin murmushi da ya bayyanar da tsantsar kyawunta, cikin sanyin ta da zaÆ™in sautinta da Allah ya hore mata tace “kullum dai tunaninki kenan Zainab, eh kuÉ—i suna iya saka mutum yayi komai, kuma kuÉ—i in kana dasu za kayi komai, sannan duk abinda kika zana kuÉ—i za suyi miki su tabbas, to amma abinda nake so ki sani shine abubuwan da kika zana basu kaÉ—ai ne mutum ke da buÆ™atar su a rayuwa ba, kuma basu kaÉ—ai ne zasu baiwa mutum farin ciki da nutsuwar da yake so ba, har yanzu dai ni dai ina nan a kan bakana kuÉ—i basu ne *farin cikin rayuwa* ba, akwai farin cikin rayuwar da kuÉ—i ba zasu baki ba, sannan akwai farin cikin da kuÉ—i ba zasu iya siya miki ba, amma tunda kin gaza fahimtata muje a haka, kowa ya tsaya akan aÆ™idar da yake ganin shine masa dai-dai, da sannu rayuwa zata nuna mana wanda yafi gaskiya.”

 

 

Jingina bayanta Zeey tayi a jikin seat tana faÉ—in “dama haka kika faÉ—i tun É—azu da baki tsayar damu kin É“ata mana lokaci kan kwalta ba, ni dai yanzu mu Æ™arisa gida dan ina bukatar hutawa.”

 

Girgiza kai Maryam tayi tana tada motar tare da maida Æ™ira’arta ta bawa motar wuta suka nufi gida cikin zuciyarta tana addu’ar Allah ya ganar da Æ™awarta kuma aminiyarta abinda take son ta fahimta……

 

 

 

****

 

 

Kaduna state 2:40pm

 

 

Cikin yanayi na damuwa ta shigo tsakar gidan nasu da sallama a bakinta, mahaifiyarta da Æ™anninta da ke zaune suka amsa mata suna binta da kallo suma fuskokin ko wannensu kana kallo zaka san É—auke take da damuwan, balle yanda suka ga Hafsat ta shigo babu alamun nasara a abinda taje nema, zama tayi kusa da mahaifiyar tasu cike da gajiya da yunwa tace “sannu da gida Mama.”

 

Kallonta Maman tayi tana faÉ—in “yauwa Hafsat, ba dai nasara yau ma É—in ko.?”

 

 

Ƙwalla ne ya ciko idanun Hafsat, cikin rawar murya tace “Mama wallahi ko da na je Kawu ko kallon arziÆ™i beyi min ba, gaisuwata ma daÆ™yar ya amsa, ko da na faÉ—a masa buÆ™atar da ta kawoni wajensa sai cewa yayi shi kuÉ—insa bana banza bane balle ya rinÆ™a rabonsa ga mutanen gari, Mama wai mu Kawu ke kira da mutanen gari.”

Ta ƙarisa tana fashewa da kuka.

 

Ta maza Mama tayi ta maida nata hawayen tana faÉ—in “kiyi shiru Hafsah ki bar kuka, komai yayi tsanani yana tare da sauÆ™i, Allah ya san damu, na tabbata watarana komai zai zama labari zamuyi farin ciki da yardan Allah.”

 

 

Hannu ta saka tana share hawayen da suke ta gudu a saman kumatunta tace “Mama sai yaushe ne wannan *farin cikin rayuwar* da kike ta faÉ—a zai zo ? Mama tun tashina na ganmu cikin wannan yanayi har yau kuma be canza ba, tun Baba na raye muke fuskantar wannan rayuwar har ya bar duniya komai yana nan sai ma Æ™ara taÉ“arÉ“arewa da yakeyi, sai yaushe ne zamuyi farin ciki Mama ? Sai yaushe ne mu zamu ji daÉ—i ? Anya kuwa Mama zamu risÆ™i wannan *farin cikin rayuwar.*?”

 

 

Share guntun hawayenta Mama tayi tana faÉ—in “Rashida kar kiyi saÉ“o mana, ai ba’a taÉ“a cire rai da rahamar Ubangiji, in Allah ya so za muyi farin ciki zamuyi ne, in kuma a haka ya rubuta mana rayuwar babu yanda zamuyi, yanzu ma Alhamdulillahi kawai zamu faÉ—a tunda ya barmu da lafiyarmu, kuma duk halin nan da kike kallonmu ciki akwai waÉ—anda suka fimu, to kinga ai dole mu gode Allah, kuyi haÆ™uri da dukkan wani hali da zamu tsinci kanmu a cikinsa, Allah yasan damu, kuma jarabawarsa ce, dan haka sai muyi addu’ar cinyewa.”

 

 

Ita da Æ™anninta uku da su ma ke share hawaye suka gyaÉ—a kansu cike da aminta da zancen mahaifiyar tasu, cikin sanyin murya Hafsat tace “to Mama yanzu me zamu ci.?”

 

Ajiyar zuciya Mama ta sauke me Æ™arfi tace “ki tashi ki tattara wancan kwalayen da Abdul ya roro ki kunna wuta ki É—aura ruwan É—umi ko shi mu samu mu Æ™urba, nasan Æ´an hanjinmu zasu warware mu samu sassaucin yunwar da muke ji, sai mu ga abinda Allah zai yi zuwa anjuma kuma.”

 

Jiki a sanyaye Rashida ta miÆ™e dan aiwatar da abinda mahaifiyarta tace……..

 

 

 

 

****

 

 

 

Zaria 11:30am

 

 

 

 

Wata matashiyar budurwa da bazata gaza shekara sha bakwai ba na hango ta fito daga wani shagon aski dake nan cikin Æ´ar Æ™aramar kasuwar maÉ—aci dake a cikin garin Zaria hannunta riÆ™e da roba irin wanda masu saida abinci ke amfani dashi, daga cikin shagon wani saurayi na faÉ—in “Rashida ki zubo min abincin nima ki kawo min.”

 

Waigowa tayi ta na faÉ—in “wallahi Dauda yau bana baka abinci ko cokali É—aya ne matuÆ™ar ba kuÉ—aÉ—ena ka bani ba.”

 

Cikin kwantar da sauti wanda ta kira da Dauda ya ce “haba Rashida kar muyi haka da ke, kema kinsan zan baki kuÉ—inki.”

 

TaÉ“e baki tayi tana faÉ—in “dama yau muka saba da sai kayi min wannan daÉ—in bakin.”

 

 

Cikin wata murya na mayaudarar samari yace “ki zubo min wallahi yau zan haÉ—a miki kuÉ—aÉ—enki Ummu har da Æ™ari matukar zakiyi min yanda aka saba.”

 

Fuska ta washe tana faÉ—in “da gaske ka keyi Dauda.?”

 

Yana kallon idanunta yace “kinsan dai ba zan miki Æ™arya ba ai, ke dai je ki zubo min abincin kawai sauran sai ya biyo baya.”

 

Murmushi takeyi tana me ci gaba da tafiya take faÉ—in “kadai san masu kauri zaka Æ™ara, dan bana baka kaya ka kwasa ni kuma ka barni da biya ba ga kuma ciwon jiki.”

 

Dauda yana wata Æ´ar iskar dariya ya É—an É—aga muryarsa yanda zata jisa yace “karki damu, yau aljihuna akwai nauyi.”

 

 

 

 

 

 

 

Muje zuwa

 

 

 

 

 

 

 

Kuna buƙatar na ci gaba ?

 

 

 

 

*To ga Raheenat ta dawo bayan dogon lokaci, ina fatan zamu É—aura daga inda muka tsaya koma fiye da haka ?Comments naku shine zai tabbatar min da hakan*

 

 

 

 

 

Meeraheenat ce

 

*FARIN CIKIN RAYUWA*

 

 

 

 

 

*TSORY AND WRITTEN*

BY

 

*RAHEENAT M ABBAKAR*

_(Meeraheenat)_

 

 

 

 

 

*SADAUKARWA GA FAMILYNA ABIN ALFAHARINA*

 

 

 

 

PAGE 2

 

 

 

 

Kano

 

 

 

 

Saukowa takeyi cike da nutsuwa daga upstairs cikin shigar riga da wandon Pakistan ruwan pink yayin da ta yi rolling da mayafinsa, jakarta saɓe a kafaɗarta, sosai kayan suka karɓi jikinta kasancewarta me hasken fata.

 

Kai tsaye dining area ta nufa inda mahaifinta da mahaifiyarta da Æ™aninta suke zaune suna break, kujera ta ja ta zauna tana faÉ—in “barkanku da wannan lokaci Ummi and Abbu.”

See also  Diyana hausa novel complete

 

_(Kasancewar sun gaisa tun bayan sallar asuba, dan Æ™a’ida ne da zaran ta idar da sallah ta gama addu’ointa kafin ta koma bacci zata bi É—akunan iyayan nata ta gaidasu sannan ta koma ta kwanta)_

 

Fuskarsu cike da annuri suke kallonta, Abbun nata ne ya fara faÉ—in “barkanki dai my daughter, sannu da fitowa.”

 

Murmushi tayi wanda ya bayyanar da fararen haÆ™oranta tace “yauwa Abbu.”

 

Ummi ma tana murmushi tace “barka my love har kin shirya kenan.?”

 

Fuskarta be gushe da murmushin da ke samansa ba tace “eh Ummi, break kawai zanyi sai na wuce, kinsan na faÉ—a miki yau lecture namu na safe ne, 9:30 zamu shiga.”

 

Agogon dake É—aure a tsintsiyar hannunsa Abbu ya kalla yace “to sai ki hanzarta dan yanzu 8:45 ne.”

 

Tana janyo cup dan haÉ—a tea take faÉ—in “insha Allahu Abbu.”

 

Hafiz ne yace “good morning Aunty Maryam.”

 

Kallonsa tayi da murmushi saman fuskarta tace “morning how are you my lovely brother.”

 

Shi ma yana murmushi yace “im fine Auntyna.”

 

Tana juya tean da ta haÉ—a cikin cup take faÉ—in “masha Allah, haka na keso dama na ji.”

 

Kallonsu kawai iyayan nasu keyi suna murmushi, zuciyarsu cike da ƙaunar yaran nasu wanda su kaɗai Allah ya mallaka musu.

 

 

Tea kawai tasha ta miÆ™e tana goge bakinta da tissue tana faÉ—in “Ummi and Abbu ni na tafi sai na dawo.”

 

Ummi ta fara faÉ—in “to Allah ya kiyaye ya tsare ya bada sa’a daughter.”

 

“Ameen Ummina”

Ta faÉ—a tana saÉ“a jakarta, Abbu ma cewa yayi “ki kula sosai daughter Allah ya tsare ya dawo mana da ke lafiya.”

 

Cike da jin daÉ—i tace “ameen ya Allah Abbuna, na gode da addu’oin ku.”

 

 

Tana Æ™oÆ™arin barin dining É—in Zeey ta shigo falon bakinta da sallama, amsa mata sukayi Maryam na takowa zuwa falon take faÉ—in “sarkin Æ´an makara, ai da baki shigo ba sai-dai ki sameni a school dan yau ba zan tsaya shiga gidanku ba.”

 

 

Harararta Zeey tayi ba tare da ta bi takan maganarta ba ta nufi dining tana faÉ—in “ni dai bari na gaisa dasu Ummi.”

 

TaÉ“e baki Maryam tayi ta nufi Æ™ofar fita tana cewa “ki sameni a mota, in kuma wallahi ki kayi zamanki sai-dai ki tadda Æ™urar motar.”

 

 

Cikin sauri Zeey ta gaisa dasu Abbu itama sukayi mata addu’ar ta fito da sassarfarta dan tasan kaÉ—an daga aikin Maryam ce ta tafi ta barta.

 

 

Aiko tana fitowa ta iske har ta tada motar, buÉ—e wa tayi da sauri ta shiga tana faÉ—in “ke fa wani lokacin ba mutunci ne da ke ba.”

 

Tana bugawa me gadin nasu horn take faÉ—in “kamar yanda ki ke ba.”

 

Murmushi Zeey tayi tace “Merona kar dai har yanzu fushi kike dani.?”

 

 

Tana ficewa a gidan nasu tace “fushi da ke akan me Zainab.?”

 

 

Zainab na kallonta tace “akan maganar jiya mana.”

 

Murmushi tayi tace “akan me zanyi fushi da ke ni ko Zainab ? Ba fa a jiya nasan halinki ba, kuma ba a jiya muka fara irin hakan ba, ke aminiyata ce wacce muka tashi tare, nasan ki nasan halinki, saidai ma na bai wa wasu labari, ra’ayinmu ne kawai yasha bambam, ke inda kika fuskanta daban haka nima inda na fuskanta daban, to ba kowa sai ya riÆ™e ra’ayinsa ba.”

 

 

Murmushi Zeey tayi tace “kuma ra’ayina yafi na ki ba.”

 

 

Dariya Maryam tayi tace “ban yi miki musu ba, kamar yanda dai na faÉ—a miki ne jiya, kowa ya tsaya akan ra’ayinsa, rayuwa ce zata nuna mana wanda nasa yafi na wani, kuma waye yafi gaskiya.”

 

Cike da rashin damuwa Zeey tace “shikenan, Allah ya ara mana rayuwar, zaki gane nafi ki gaskiya kam.”

 

Murmushi kawai Maryam ta yi tana me ci gaba da tuÆ™inta har suka iso cikin school É—in nasu…

 

 

*****

 

 

 

A jere suka fito suna hira abinsu, fuskokinsu kaɗai zaka kalla ka tabbatar basa da damuwar komai, fitowarsu kenan daga lecture nasu na ƙarshe, dan haka kai tsaye suka nufi gurin motarsu.

 

 

Tun daga nesa suka hangosa tsaye jikin motarsa hannunsa riÆ™e da makulli yana jujjuyashi, Zeey ce ta kalli Maryam fuskarta É—auke da murmushi tace “Maryam ga fa mutuninki nan.”

 

Harararta Maryam tayi tare da jan tsaki tana me kau da kanta daga kallon inda yake, Æ´ar siririyar dariya Zeey ta saki tana faÉ—in “wai me yasa kika tsani wannan bawan Allah ne haka Maryam.?”

 

Ba tare da ta kalleta ba tace “tsanarsa ? Ni na haliccesa da zan tsanesa ? Ni ban tsanesa ba, kawai dai bana ra’ayinsa ne, beyi min ba, wannan kawai shine.”

Ta gama faÉ—in hakan dai-dai sun iso inda yake, ba tare da ta nuna tasan da tsayuwarsa ba ta nufi inda motarta ke fake ta fara Æ™oÆ™arin buÉ—ewa, cikin sauri yace “Maryam tun É—azu ke fa nake tsayuwar jira, amma ya zaki zo ki wuce kamar baki ganni ba.?”

 

Wani irin juyowa tayi irin da gasken nan bata gansa ba sai lokacin da yayi magana tace “lah Sadam dama kai ne tsaye ? Ai ban lura kai ne ba shi yasa.”

 

Kallonta yakeyi yana mamakin yanda ta nuna bata lura dashi ba alhali yasan tun kafin ta Æ™araso ta gansa, sai kawai shima ya waske ya nuna mata hakan ne ya saki murmushi yace “ni ne Hafsat, tun É—azu na ke jiran fitowarki ai.”

 

Ita ma murmushin ta sakar masa tana faÉ—in “Allah sarki, kuÉ—i zaka bani ne halan.?”

Tayi maganar cikin sigar zolaya.

 

 

Dariya ya saki dan yasan shashantar dashi take son yi yace “in su ki ke so ai sai na baki duk da nasan kinfi Æ™arfin su.”

 

Murmushi tayi tace “wa ya faÉ—a maka ana fin Æ™arfin kuÉ—i, duk kuÉ—in ka kana son Æ™ari, baka ga É—angode har yau nema yake yi ba.?”

 

 

Fuskarsa É—auke da murmushi yace “hakane kuma, amma ni abinda zan baki yafi kuÉ—i muhimmanci.”

 

ÆŠan yatsina fuskarta tayi tace “am Sadam kaga daga lecture muka fito nayi matukar gajiya da yawa ina buÆ™atar hutu, ka bari zamuyi waya kawai.”

 

Yasan neman zille masa takeyi, amma jin tace zasu yi waya yasa ya saki murmushi yace “okay shikenan, ya kamata dama kije ki huta sai na kira É—in.”

 

Hannu ta É—aga masa kawai alamar bye ta muÉ—e motar ta shige, Zeey ta Æ™ariso itama ta shiga sannan tayi ma motar key suka fice daga makarantar, yana kallon motar tasu har ta fice sannan ya sauke numfashi ya shiga nasa motar shima yabar makarantar…

 

 

****

 

 

Suna tafe Zeey ta kalleta tace “Maryam me yasa ba zaki baiwa Sadam dama ba, ni sam banga aibun guy É—in ba, yana da kuÉ—i yana da kyau to me ya rage kuma.?”

See also  Matan Aure Masu Zina

 

ÆŠan kallonta Maryam tayi kana ta É—auke kanta sannan tace “yana da kuÉ—i yana da kyau, sai aka ce miki sune abin so ga namiji kaÉ—ai.?”

 

 

Zeey na kallonta tace “sosai ma kuwa, yana da masu gidan rana wanda zaka fantama yanda kake so, sannan yana da kyau wanda babu raini duk inda ka shiga dashi, a nawa ganin babu sauran wani abu, to me zaki nema kuma.?”

 

Maryam tace “hali na Æ™warai da addini da sanin kima da darajar É—an adam.”

 

TaÉ“e baki Zeey tayi tace “to gani nayi dai Sadam baya da wani mummunan hali, to wai ko yana dashi halin nasa zaki ci.?”

 

Juyowa Maryam tayi ta na mata wani irin kallo sannan ya maida hankalinta ga tuÆ™i tana faÉ—in “Zainab bansan ranar da zaki canza ba, wannan halin na ki shine hanya ta farko da zai saka ki cikin matsala a rayuwarki, halin mutum abin dubawa ne sosai in aka ce za kuyi zama ne dashi irin ta aure, domin shi aure zama ne da kake saka ran zaka yi sa har abada da mutum, to in aka ce baya da halayyar Æ™warai taya zaka ji daÉ—in wannan zaman dashi ? Bama wannan ba Zainab, Sadam ban san sa da wani halayya me muni ba, kawai ni dai beyi min bane bana ra’ayinsa, bazan ce bana sonsa ba sabida ban isa Æ™in halittar Ubangijina ba, amma ban taÉ“a jin son aurensa ba, ban taÉ“a masa kallo na mijin da zan zauna dashi ba, kuÉ—i kyau ba shine abin da na keso ga mijin da zan aura ba, hasali ma ni bana son mijin da yafi ye kyau da kuÉ—i, domin kyau da kika gansa hatsari ne babba, Zainab a tsarina na fi son na auri miji me rufin asiri, kuÉ—i basu taÉ“a É—aÉ—ani da Æ™asa ba, na tashi cikin gidan kuÉ—i, amma sam basu taÉ“a birgeni ba, ni har yau ban yanda cewa kuÉ—i sune *farin cikin rayuwa* ba, babu komai a cikin kuÉ—i sai wahala da Æ™alubale, duk na mijin da yake da kuÉ—i sosai da wahala ki ga yana da lokacin matarsa yanda ya kamata, ni ko macece me son ko yaushe in ganni tare da mijina cikin kulawarsa, Zainab ina so ki fahimta ba komai kuÉ—i sukeyi ba, sannan halayyar mutum da addininsa abin dubawa ne in aka ce za kayi rayuwa ne dashi na har abada, ni bana ra’ayin auren me kuÉ—i, ina son namijin da zai riÆ™eni da amana ne wanda zai bani dukkan kulawarsa me addini da sanin darajar É—an adam, wanda zai san darajata, ko baya da kuÉ—i zan zauna dashi har Æ™arshen rayuwana ba tare da Æ™orafi ba.”

 

 

Shiru Zainab tayi tana nazarin maganganun Maryam kafin daga bisani ta saki wani dogon numfashi tace “amma Maryam ni a nawa ganin kinyi ma kuÉ—i mugun fahimta ne kawai, sam yanda kike tunani ba haka suke ba, ni a nawa in ka auri me kuÉ—i ai ka gama hayewa, baka da wani matsala fa, amma rayuwar talauci babu komai cikinsa sai wahala da Æ™unci, sannan a ganina halayyar mutum ba cinsa za kayi ba, eh yana da kyau ace mutum yana da halayya na Æ™warai, to amma kuma in yana da kuÉ—i ai zasu É“oye aibunsa koda yana dashi, har yanzu ni dai ban yarda da rayuwar talauci ba, kuÉ—i kawai, ko duba ki kayi da iyayen mu kaÉ—ai zai saka ki Æ™ara son rayuwar daula, kuma kina maganar masu kuÉ—i basu fiye kula da iyalansu ba, to meye amfanin zaman mijin a gida ? Ya fita kawai ya nemo, yanzu iyayenmu wani damuwa kika gansu a ciki dan Allah.?”

 

 

Dariya Maryam ta saki tana faÉ—in “lallai Zainab na yarda kinyi nisa saidai Allah ya ceto ki, sannan dan Allah in zaki iya kije ki samu iyayenmu mata ki tambayesu suna jin daÉ—in zaman auren da sukeyi yanda suke so ko kuwa ? Amsar da suka baki zaki iya Æ™ara saka sa cikin maganganuna ki auna su, wataÆ™ila zaki gane gaskiyar abinda na ke faÉ—a miki, sannan wani abu guda É—aya, su iyayanmu maza suna iya Æ™oÆ™arin su gurin kula da matansu bakin gwargwado, kuma duk da haka ina tabbatar miki basa baiwa iyayenmu irin kulawar da suke buÆ™ata saidai suna kwatantawa, amma ki sani ba kowanne me kuÉ—i ne ke da irin halinsu ba, samun irin sun yana wahala ki fahimta.”

 

 

TaÉ“e baki Zeey tayi tace “ni dai ban ga wani rashin jin daÉ—i ba a cikin rayuwar iyayanmu, ke ne dai har yau kika kasa fahimta, basan me yasa kike adawa da duk wani abu da zan faÉ—a ba, kina bani mamakin yanda kike nuna kuÉ—i basa da wani mahimmanci a rayuwar É—an adam kamar ba a cikinsu kika ta so ba, ke kullum zancen ki kenan kuÉ—i basu ne *farin cikin rayuwa* ba, to sai ki faÉ—a min abinda ya fisu saka farin ciki a rayuwa, na ga ke ma yanzu sabida su ne kike farin cikin da kike ciki, baki nema komai kin rasa ba, bakya da wani damuwa, dan haka ni banga aibun su ba, kuma ba zan taÉ“a yarda na auri mijin da baya da masu gidan rana ba.”

 

 

Murmushi Maryam kawai tayi tare da faÉ—in “Allah ya taimaka Zainab, dan Allah da ga yau to karki Æ™ara kawo min wannan zancen, kowa ya bar ra’ayinsa cikin zuciyarsa, kowa yayi abinda yake ganin masa shine daidai faÆ™at.”

 

Wayarta Zainab ta hau dannawa tana faÉ—in “hakan ma yafi.”

 

Daga haka babu wanda ya sake magana a cikinsu……

 

 

 

******

 

 

 

 

Zaria

 

 

 

Sai da ta leÆ™o da kanta ta tabbatar babu kowa a wajen sannan ta fito daga É—an Æ™aramin É—akin kwanan samarin dake Æ™ofar gida tana Æ™ara gyara gyalenta take faÉ—i ma wanda ke ciki “ni na wuce sai kuma gobe.”

 

Yana daga kwance yace “shikenan sai mun Æ™ara jonewa goben, amma da so samu ne mu sake haÉ—ewa da yamma ki Æ™ara lasa min wannan zumar taki da kullum zaÆ™i take Æ™arawa.”

 

Harara ta sakar masa tace “ka dai sani bana fitowa da yamma, goben ma ba lallai na baka ka lasa ba, dan akwai masu buÆ™atar hakan wanda suka fika sakin hannu.”

 

Dariya yayi yace “Rashida ke dai sam bakya da godiyar Allah wallahi, yanzu fa dukkan kuÉ—in da ke jikina na zube miki amma kina faÉ—a min magana.”

 

TaÉ“e baki tayi tace “ni ka ga tafiyata kafin wani ya zo giftawa ya ganni, sai mun sake haÉ—ewa.”

 

Ko amsarsa ba ta jira ba ta sa kanta ta bar gurin, kai tsaye gurin saida abincinta ta nufa ta tattara kula da robobinta da É—aura wa almajiri suka nufi gida dama ta saida abincin tun É—azu ta tsaya amsar kuÉ—aÉ—enta ne gurin samarinta, dama sai ta gama shaida abinci zata bisu É—aya bayan É—aya tana amsar kuÉ—inta bayan sun gama jagwalgwalata sai a bata kuÉ—inta tare da Æ™ari……

 

 

 

Muje zuwa

 

 

 

 

 

Meeraheenat ce

Leave a Comment

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Scroll to Top