Guntun Goro Hausa Novel

Guntun Goro Hausa Novel

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

GUNTUN GORO

 

 

 

_Zainab Habib(Mom Islam_

 

 

*✨TEAM GAWURTATTU BIYAR5✨*

 

 

 

Dama gareku masu son a tallata muku hajarku, cikin farashi mai sauƙi ku tuntuɓi wannan number 08141799224

 

_Bismillahir rahmanir rahim_

 

🆓🅿️1-2

 

_Gargaɗi!! Gargaɗi!! Gargaɗi!! ban amince a sauyamin littafi ,ko a ɗoraminshi a wata ƙafa ba tare da izinina ba! wannan littafin mallakar Zainab Habib ne, yin hakan zai iya sawa ince nabar mutum da Allah! ina roƙon Allah yasa kamar inda muka fara littafinnan lafiya Allah kasa mu kammalashi cikin ƙoshin lafiya amin_

 

Asabar shida ga watan bakwai ,shekara ta dubu biyu da ashirin da biyu, 11:1am

Zaune nake gaban Abbana hannuna bisa kumatuna, idona kuwa nakan ciwon ƙafarsa wacce munyi magani har mun gaji.

“Ilham” Abba ya kira sunana cikin sanyayayyar muryarsa wacce duk sanda naji ya kirani da ita jikina ke kyarma sbda nasan babu lafiya.

“Na’am” nace kaina a Æ™asa ina jiran inji abinda Abbana zai cemin “Ilham kinga wannan ciwon Æ™afar tawa daÉ—a ta’azzara yake, gashi duk wata dukiya da muka mallaka a halin yanzu mun tashi babu ko sisi, ciki harda gonakin mahaifiyarki duk kince in siyar na siyar Allah baisa an dace ba”, kallon Abbana nayi idanuna na zubar da Æ™wallah nace “Abba to yanzu ya zamuyi gashi Æ™afar daÉ—a rarikewa take?”

yamutsa fuska Abbana yayi lokacin da yake ɗago ƙafar alamun zafi takeyi masa,

“Da zaki amince Ilham da na nema miki aikatau a gidan Alhaji Abdullahi Zakin Naira “a gigice na É—ago kaina dana sunkuyar ina kallon Abba kafin nace” aikatau kuma Abba ?ko ka mance kai da kake cemin baka shiri da iyayen da suke tura Æ´a’Æ´ansu aiki amma kai da bakinka kake kiramin inje inyi aiki” na faÉ—a gabana na dukan uku-uku, tabbas inda abinda na tsana bai wuce ace gani a gaban wasu sai nayi musu wanke-wanke da shara sannan zasu bani abinda zanci ba,cikin mamaki da tsoro nace “,Abba mezan gani haka ?kuka kakeyi ?, cikin muryar kuka Abba yace “Ilham bawai ina nufin ki dauwama kina aikin bane, nidai burina a bada kuÉ—in aikin naki in sun yarda mu fara zuwa asibiti tunda ,har yanzu bamu taÉ“a tunanin zuwa ba ko za’a dace” yanayin da naga Abbana ya shiga ya jefani cikin wani hali, nace “Abba ka nemo wata shawarar amma wannan batayiba” na miÆ™e rai a É“ace, a dole ina ganin Abba yanason ya sa a wulaÆ™antani, yo inba wulaÆ™antawa ba, yace inje wani gida aikatau bacin nasan zubar da mutunci ne, duk da nasan bashi da cikakkiyar lafiya .

Kai tsaye ɗakina na nufa, na kwanta saman katifata wacce taji zanin gado milk color ,kasancewar a ƙasa take duk da hakan bai hana zanin gadon ɗame ƙatifarba .

Kaina na kifa a kan pilo tare da tuno maganar Abbana ta gurin aikatau “ya illahi” na ambata idona na zubar da hawaye ,daga nan bacci yayi awon gaba dani.

Ganin na shiga ɗaki baba ya ɗogara ƙafarsa cikin ƙarfin hali ya wuce ɗakinsa, zuciyarsa fal baƙincikin ƙin amincewata da buƙatarsa.

Bani na tashi ba sai waje Æ™arfe biyu dai-dai ,ina mutsike idona na fito tsakar gida ina cewa “gaskiya nayi bacci mai nisa taÉ“É“ yaushe rabona dayin wannan barcin ?”,

Bayi nashiga na É—auki buta na kama ruwa kana na fito nayi alwalah, na nufi É—aki dan gabatar da sallah, ina idarwa na shafa adu’oi na ,na miÆ™e na ninke sallahya na cire hijab kana na fito tsakar gida tambayar Abba mai zamu dafa zuwa dare .

Da sallama na shiga É—akin nasa ,bayan ya amsa na tsuguna kafin nace “,Abba me za’a dafa É—azu da safe ma raguwar gari nasha da suga” rai a É“ace Abbana yake kallona ,wanda yasa na fara tsorata dan tunda mahaifiyata ta rasu lallashina yake, amma yau shine dayimin irin wannan kallon?, na tambayi kaina cikin tsoro.

“Tashi ki bani guri bana son Æ™ara jin maganarki” Abba ya faÉ—a yana nunani da hannunsa, Innalilahi wa inna ilaihirraji raji’un na ambata a fili kafin nace,”Abba ko nayi maka laifi ne?” abinda Abbana baya yimin naga ya kuma yimin wato harara, shidako mugun kallo baya min haka kuma ko me nakeso shi za’a dafa, kasancewar ana yawan kawo mana sadakar abinci .

Jiki a sanyaye na tashi nabar gurin idona tabb da ƙwallah, ina shiga ɗaki suka zubo,

Har aka kira sallahar la’asar Abba bai cemin komai ba, har akayi magrib ko kulani ma bayayi, balle yaji nayi masa magana.

Tunowa nayi, ashe akan ƙin amincewa da buƙatarsa da naƙi yine yasa shi yin fushi dani,

Kiran sallahar Azhar da akayi ne ya sani fitowa daga É—akina, saboda inason idan nayi alwalah nayi sallah inje gidansu Muhibba Æ™awata wace muka gama secondary tare, in aro nera É—ari, ina tsaye ina shirin shiga bayi naji Abbana na sauke numfarfashi kamar wanda yayi uban gudu, da sauri nayi É—akin cikin mamaki na gansa a zaune yana kuka ga Æ™afar na zubar ruwa, “mun shiga uku” na ambata sai kuma na fashe da matsanancin kuka, bansan lokacin da nace “Abba na amince ,na yarda zanyi aikatau domin samun lafiyar Æ™afarka”,

Albarka Abba ya dinga samin har cemin ga ɗari biyar in siyo taliya a dafa ko mai da yaji ne, tunda bama rabo da kayan abinci amma yau kam bamu da taliya ta ƙare.

Ganin fara’a a fuskar Abbana yasa nima naji farinciki sosai,

Na miƙe na haɗa wuta na ɗora sanwa, ruwan na tafasa na zuba taliyar, na tsiyayo manja na yanko albasa, bayan taliyar ta dahu na sauke na juye a kwando,na ɗora manja nasa albasa, ina gama haɗa komai na zubawa Abba nasa, nima na zuba nawa.

ÆŠakinsa naje munacin abincin muna hira har muka gama, Abba ya miÆ™e ya kuskure baki, dan gabatar da sallaha ni kuma na dawo É—akina nayi tawa sallahar, tare da kwararo adu’oi akan samun lafiyar Abbana.

Washe gari,bayan anyi sallah Abba yayi tasa a gida sbda Æ™afarsa, ina idarwa naje na gaishesa ya amsa cikin sakin fuska, na fito na haÉ—a wuta,wutar na kamawa na É—ora ruwan wanka haÉ—e da ruwan kunu, yanayin zafi na É—iba naje na sirka kana na nufi bayi kasancewar soso da sabulun yana can, cikin sauri nayi wanka na fito,lokacin ruwan yanata tafasa na dama kunun zuwa anjima nasa gasara na sanya suga,na É—auko kofin baba na sanya masa na shiga É—akinsa da sallama, amsawa Abba yayi fuska a sake ,na durÆ™usa nace “Abba ga kokon naka “Abba ya karÉ“a yana sanyamin Albarka na fice .

Cire hijab É—in dana fito daga wanka nayi,na janyo ledar kayan kwalliyata, cikin Æ™warewa irin tawa a fannin ado da kwalliya na tsara kwalliya mai É—aukar hankali, bayan mayukan dana shafe jikina dasu masu Æ™amshi mai daÉ—i, miÆ™ewa nayi na buÉ—e akwatin kayana na ciro doguwar rigar milk color anyi mata flawoyi da pink É—in zane wanda yai matuÆ™ar fito da kyan rigar, bayan na feshe jikina da turare na kawo rigar nasa,nayi rolling É—in mayafin rigar a kaina tare da kallon kaina a mudubi” murmishi nayi kana nace Alhmdulilh, na É—auki glass É—ina no respect nasa, wanda ya rufe ilahirin fuskata, duk wanda ya ganni zai É—auka Æ´ar wata alhajin ce sbda irin shigar da nayi koni jin kaina nake a sama lol, farin takalmi da farin mayafi na É—auko kana da sarÆ™a da warwaro da É—ankunne duk na maÆ™alasu, tunowa nayi ban sanya agogon hannuna wanda nake gayu dashi sbda a zahiri baya aiki kawai dai ina sawa ne.

Kunsan in mutum yayi wanka,musamman ma yaci tsaleliyar kwalliya baya son ya dinga tafiya cikin rashin tsari, to nima a nawa É“angaren haka ne, tafiya nake kamar Æ´ar wani mai muÆ™ami, kofin danasha kunu na fito dashi, Allah yasa nayi wanke-wanke, ina daga bakin Æ™ofar É—akina ina kallon fuskata a mudubi na É—aga murya nace “Abba yanzu Æ™arfe nawa?”Abba ya kalli agogon wayarsa kana yace “Æ™arfe goma saura minti uku (9:57am) “To” nace, dan ba haka naso ba, naso ace Æ™arfe sha É—aya ne yanzu, na zauna har Æ™arfe goma sha É—aya (11:00) dai dai na fito haÉ—e da janyo Æ™ofar É—akina,naje É—akin Abba nace Abba zanje gidansu Muhibba “Abba yake kinsan dai banason ki fita ki kai yamma koh ?”Abba insha Allah ba jimawa zanyi ba”,

See also  Kawar 'Ya ta ce complete

Abba yace “a dawo lafiya” nafice.

Karin wasu littafai da zaku so

Powered by: www.mynovels.com.ng
Kai tsaye na fita,

Bakin titi na nufa ina jiran napep,

Wata dalleliyar mota fara sol mai masifar kyau ta biyo ta gabana,saura kaÉ—an ta bigeni “cike da masifa haÉ—i da huci na jin haushin abinda mai motar ya yimin, naja tsaki mtsw, sai kuma naga motar ta dawo da baya tayi parking a gabana, rage tsayin baÆ™in gilashin motarsa yayi, na kusa dashi yace “Æ´am mata dan Allah kiyi haÆ™uri” cikin yamutsa fuska na nuna wanda yake mazaunin driver da hannu kafin na fara zazzaga musu ruwan masifa ina cewa “banda tsabar wulaÆ™anci da rainin wayo shi drivern makaho ne ?”ko baya gani ne?, inda abinda yafi bani haushi bai wuce, Æ™in kulani da drivern yayi ba, sai wani shan Æ™amshi yake “Ibrahim sai da nace maka bazan dawo ba bana son raini amma kaga abinda ka janyo mana ko ?”wanda saurayin ya kira da Ibrahim yace “afuwan Mubin, kamar inda ake yabon ahalin gidanku gurin tarbiya da sanin mutuncin juna bai kamata ka sauya naka halin ba” Ibrahim ya Æ™arshe zancen yana dafa kafaÉ—ar Mubin.

Niko raina ya gama É“aci sosai gashi ban sami adai-daita sahu ba, gashi sun wani taremin gaba nikuma nakasa matsawa tsabar inajin ruwan masifa.

Ibrahim ya leÆ™o da kansa, cikin sanyaya murya yace “Æ´an mata kiyi haÆ™uri dan Allah”,

Shiko Mubin É—in tsaki yaja tare da cewa “aikin banza aikin wofi ni kaga ba tsayawa jiranka zanyi ba “jibeki mitsw”

Mubin yaja mota kamar wanda zai kuma bi ta gabana.

Iya jin haushi naji haushi ji nake kamar zanyi kuka tsabar baƙinciki, gashi inajin kamar inkoma gida.

Kallon jikina nayi naga ai yama watsamin kwatami, na dafe kaina cikin zafin rai nace “anyi shege É—an kutumar uba Allah sai ya saka min, inhar kere na yawo zabo na yawo watarana zasu gamu, ina tsaka da tunani naji mai napep na cewa “hajiya tafiya ne?”

Idanuwana nayimin zafi nace eh zakaje É—orayi ?” mai napep yace “naira É—ari” batare da na taya ba nace tom muje ,

Muna tafiya ina tuno wulaÆ™ancin Mubin da bani haÆ™uri da abokinsa Ibrahim yayi, nuna masa Æ™ofar gidansu Muhibba, bayan yayi parking nace dan Allah yayi haÆ™uri in shiga in amso kuÉ—i “mai napep É—in yacemin babu komai”.

Cikin sauri na shiga, tare da yin sallama nayi sa’a Muhibba na zaune tana latse-latse a wayarta, gefe kuma mahaifiyarta ce take bawa Æ™aninta nono, ina Æ™aÆ™alo murmishi nace “Muhibba bani nera É—ari “mahaifiyarta na washe baki tace “ah Ilham kece a gidan ?”ta miÆ™omin É—ari biyu, na amsa na kaiwa mai napep ya bani chanji,

Dawowa nayi ina murmishi nace “Ummi ga chanjin “Ummi tace “kibarshi kawai Ilham muje ciki” Muhibba tana dariya ta fara tsokanata tana cewa “wannan wankan fa ?”nayi dariya kafin nace “,na zuwa gidanku ne” muka shiga É—akin Ummi dukkanmu,

Bayan mun gaisa da Ummi ta tambayeni ya jikin Abbana, nace mata yaji sauÆ™i, daga nan ta fice muka sha firarmu nida Muhibba “ya na ganki wani iri kamar kinyi ciwo gashi idonki kamar kinyi kuka ?”Muhibba ta tambayeni,

“mtsw Muhibba na haÉ—u da wani shege wanda kansa ke rawa walhi da tuni kunji labari yasha ban ban an kaÉ—eni “Muhibba ta dafe Æ™irji tana cewa” na shiga uku garin yaya “cikin Æ™osawa da bada labarin, sbda bana son in dinga tuno abinda yayimin yasani cewa “iskanci kawai “,

Bani nabar gidansu ba sai da muka yiwa Ummi gyaran ɗaki da wanke-wanke, muka sake gyara ɗakin Muhibban, kasancewar gidan babba ne, yasha siminti ɗakuna biyar ne a gidan, ɗay na Ummi ɗaya na Muhibba ɗaya kuma na baban Muhibba ɗaya na baƙi ɗayan kuma yana mazaunin kitchen ne.

Bayan mun sanya turaren wuta a gidan lokacin munyi sallahr Azhar muka shiga kitchen muka fere dankali na hausa muka soya, kasancewar sunada miya.

Idan naje gidansu Muhibba sai ka rantse gidanmu ne,

Ƙarfe 6:pm na É—auko mayafina ina cewa “Abbana yace kar in daÉ—e lallai yau zansha faÉ—a sosai” Muhibba tasa dariya tana cewa “Ilham akwai tsoro gaskiya, to gashi bakici abincin ba ai saiki tsaya dan bazaki tafi bakici ba” Ummi na jinmu tana dariya, har nayi hanyar waje Ummi ta Æ™walamin kira na amsa kana nazo, baÆ™ar leda naga ta miÆ™amin tace “aiko gashi na Æ™ulle miki a leda” murmishi nayi ina tattaba dankalin kana na rufe baki ina cewa “Ummi harda miya?,

Ummi tace” eh to ki gaida baban bak kice ina gaishe shi “,

Muka fito tare da Muhibba muna tafe muna hira, sannu a hankali muka iso bakin titi na tari napep zuwa anguwarmu Rijiyar lemo, Mukayi sallama da Muhibba.

Ina komawa gida na rangaÉ—a sallama, duk da nasan zansha faÉ—a,

Shiru naji babu alamun motsin Abba a gidan, cikin Æ™anÆ™anin lokaci na tsorata dan ko sallahar magrib ba’a kira ba ana harama, a iya sanina tunda Abba ya haÉ—u da ciwon Æ™afarnan ya dena yawan fita amma yau ina yaje ?, na tambayi kaina batare da tunanin ai babu wanda zai ani amsa ba.

Ban kawo komai a raina ba sbda banji wani yanayin damuwa a jikina ba, dan haka na wuce É—akina na buÉ—e kana na ajiye dankalin cikin roba, fitowa nayi tsakar gida ina mai cire no respect É—in idona nahau tunani,

Kiran sallahar magriba da akayi ne ya sanyani miÆ™ewa naje na É—auro alwlah na dawo na shimfiÉ—a sallahya na kabbara sallah, ina idarwa na fito tsakar gida na É—auki kujera Æ´ar tsugunno na zauna tare da rafka tagumi, abinda ya fara yimin ciwo shine rashin waya da bani da ita, har akayi sallahar isha’i aka idar har Æ™arfe tara Abba shiru, babu shi babu alamunsa..!

*GAWURTATTU BIYAR,5🤚TAFIYAR TA MUSAMANCE*

 

1, *MU GANI A ƘASA..🔥*

_Ummu Affan_

 

2, *ABIN CIKIN ƘWAI..🥚*

_Ummu Maher_

 

3, *GUNTUN GORO..*💥

_Mom Islam_

 

4, *GISHIRIN ZAMAN DUNIYA*🌎

_Mrs Bukhari_

 

5_ *AUREN WATA TARA👩‍❤️‍👨*

_Miss Hajo_

 

 

Guda É—aya N300

Guda biyu N500

Guda uku N600

Guda huÉ—u N700

Guda biyar 1k

 

*ZAKU TURA KUÆŠINKU TA WANNAN HANYAR👇*

 

 

Fatima Rabiu Sunusi

0037219728

StanbicIBTC Bank.

 

 

Shaidar biya tanan 👇

0810 433 5144

 

 

Masu tura katin MTN👇

0814 179 9224

 

………..🥚👩‍❤️‍👨💥🌎….

 

*ƳAN NIGER GA HANYOYIN BIYAN KUÆŠINKU👇

 

Guda biyar 1000f

Guda huÉ—u 700f

Guda uku 600f

Guda biyu 500f

Guda É—aya 300f

Kai tsaye ku tura da katin Airtel ta wannan number👇Kina turawa zamu saki a grp

+227 84 50 64 76

 

 

*MUN GODE DA KASANCEWA DA GAWURTATTU TAKUN FARKO*

[01/09, 2:15 pm] +234 803 192 1625: *💥GUNTUN GORO..!💥*

 

 

_Zainab Habib(Mom Islam_

 

 

*✨TEAM GAWURTATTU BIYAR*

See also  Basma Hausa Novel

 

 

Dama gareku masu son a tallata musu hajarsu cikin sassauƙan farashi suyi magana ta wannan number 08141799224

 

 

Free page 3-4

Cikin tsananin damuwa na fice, kai tsaye shagon Dauda dake kallon Æ™ofar gidanmu na nufa, ina zuwa na samu da mutane na nemi kan dogon bencin dake ajiye a gefe na zauna tare da rafka uban tagumi, leÆ™owa Dauda yayi cikin zolaya yace “,Æ´ar Abba me kikeso nasan dai bakya wuce kayan kwalliya .kasancewar yana siyarda su cosmetics ne,

Niko nafara nisa a tunani sbda a halin yanzu Abbana kawai nake tunani, tunda naga dare yayi.

Ganin bance komai ba,

Cikin É—aga murya Dauda yace “Æ´ar Abba…

Da sauri na É—ago jajayen idanuwana na kallesa kana nace “na’am “,

“Akwai damuwa ne na ganki haka Æ´ar Abba..”

Nace “É—azu na fita nabar Abbana a gida, nadawo kuma na samu baya nan “,

Na ƙarashe magnar ina share hawayen dake sintiri a fuskata tashi ɗaya.

Gani nayi Dauda ya fito ya zauna can nesa dani sai naji yace “haba Æ´ar Abba ai da kin kirashi a waya da kinji inda yake “,

Nidai burina kawai inji abinda ya sami Abbana sbda kwata-kwata hankalina ba a kwance yake ba.

Dauda yace “ai wani Alhji ne yake taimakawa marasa lafiya shine Abban naki suka tafi shida Malam Ahmad, sbda akwai babban asibiti a cikin gidan bayan haka ma ina tunanin yabawa Abbanki gida a cikin gidan nasa, kinsan gidan kamar gari guda yake “,

Tunda Dauda ya fara magana nake jin zuciyata na zafi, duk da nasan taimakawa Abbana za’ayi to ni me yake nufi dani ?,in zauna a gidan ni É—aya ko kuma kawai ya daina sona ne, bayan kafin in tafi sai da nace masa na amince zanje aikatau É—in.

Maganar Dauda ce ta dawo dani daga tunanin dana fara tafiya, na miÆ™e jiki a sanyaye nace “to na gode barin koma gida “,

Tsabar baƙinciki ne ya hanani kiran Abba a waya, na koma gida naci kuka na godewa Allah, haka na kwanta banci komai ba,

Kiran sallahar asbha tare da ruwan da naji anfarayi ne ya tasheni, sbda tashi É—aya gari yaÉ—au sanyi, abin rufa na É—auka tare da fitila naje nayi alwalah na dawo na kabbara sallah, ina idarwa nayi adu’oi na ninke sallahyar tare da komawa na kwanta dan ji nake kamar bani da lafiya.

Bani na tashi ba sai da gari yayi haske sosai na miƙe ina salati, na ɗauko dankali na da na kasaci tsabar bakinciki, ba tare da na yi masa komai ba, na juye a kwano nasa miyar Allah ya taimaka batayi tsami ba na faraci.

Ina gamawa na É—auraye kwanukan naje na hura wutar ruwan wanka, wutar na kamawa na É—ora ruwa, cikin ikon Allah yayi zafi na juye naje nayi wanka, ina fitowa na wuce É—aki da gudu sbda sanyi da akeyi.

Duk da bacin ran da nake ciki bai hanani yin kwalliya ba, duk da yau ba wata kwalliya nayi ba, bayan mai dana shafa sai powder da tozali dana sanya a idona, na nufi gurin kayana na ciro doguwar rigar ta atamfa mai ratsin blue da fari tana ɗauke da manyan flowers, anbi kowanne gurin ado da stone fari mai ƙyalli, kasancewata mai jiki amma ba can ba, da tsayi dai-dai misali yasa rigar tayimin ɗass dama ɗinkin agwada ne.

Bayan na gama shirina na nemi guri na zauna na fara tuno maganar Dauda mai shago, dayace min wai Abbana yana gidan wani Alhji kuma zai taimaka masa,

“Shin Abban yasan Alhajin ne? ko kuma ciwon Æ™afar ne ya ishesa “,ni kaÉ—ai naketa sumbatu na haÉ—e da fashewa da matsanancin kuka.

Sallamar malam ahmad ne ya sanyani miƙewa ina share hawayen fuskata da hannu badan zanyi tunanin hodar dana shafa ta goge ba sbda ina cikin damuwa.

“Wa’alaikumussalam”

Na amsa masa fuska a tamke, a iya tunani ne shine yayiwa Abbana hanya, tunda gashi shi ya dawo amma Abbana yana can.

Har cikin gidan ya shigo ya tsaya a bakin Æ™ofa yana mai kallona haÉ—i da cewa “,Ilham Abbanki ne ya aikoni, yace wai ki shirya za’azo É—aukarki da misalin Æ™arfe É—aya na rana “,

Kallonsa kawai nake sbda, tsanarsa da nakeji yasa magana ma na kasa yi masa tunda haka ya zaɓarwa Abbana duk da nasan Abban ba yaro bane.

Cikin takaici na buÉ—i baki kamar mai koyon magana nace “to”

Na koma É—aki, shima ya fita.

Ina nan zaune a ɗaki in saƙa in warware har lokaci ya tafi,

“Nakasa gane inda Abba ya dosa, yana nufin zamubar gidannan kenan mu koma gidan wani?, wannan ai Æ™asÆ™anci ne “,

Na faÉ—a ina mai jin ciwon tafiyar da Abbana yayi.

Kiran sallahar Æ™arfe É—aya danaji anyi ne yasa gabana tsananta faÉ—uwa na miÆ™e ina ambaton sunan Allah, gashi kaf garinnan babu danginmu sai Æ´an uwa da abokan arziÆ™i, “to gurin wa zani ?wazai taimaka min ?” da wannan tunanin naje na É—auro alwalah na dawo na kabbara sallah, ina idarwa na dinga kwararo adu’a akan idan tafiyar nan tawa ba alkairi bace Allah ya wargatsata.

Horn ɗin mota da naji a ƙofar gidanmu ne yasa gabana tsananta faɗuwa na miƙe kamar mara gaskiya ina ta zancen zuci.

“Aslamu alaikum ” naji an rangaÉ—o sallama batare da nasan maiyin sallamar ba, na amsa da wa’alaikumus salamu “na yafo Æ™aramin mayafina na fito domin inga mai sallamar.

Ina fitowa naga wani matashi hannunsa riÆ™e da mukullin mota yana kallona, nima kallonsa nake daga Æ™arshe “nace kana son wani abu ne ?”

Drivern yace “dama ance inzo mu tafi ne ” mtsw naja tsaki, a hassale nace inji wa ?nifa babu inda zani kaje ka cewa Abban ni babu inda zani karma ka kuma dawoww idan ka sake dawowa wallahi sai nayi maka ihu ince waiyo ga kwarto “.

Dajin haka driver ya haÉ—e hannayensa

biyu alamun ban haÆ™uri yace “naji bazan kuma dawowa ba, amma kizo o mu tafi jikin mahaifinki ya tsananta “,

Abinka da É—a da uba nayi sauri na shiga É—akina na ina kuka na É—auko wata Æ´ar Æ™aramar jakata wacce ke É—auke da kaya kala huÉ—u sai hijab biyu da niÆ™ab da safa na fito ina cewa “muje “muryata har rawa take.

Bayan drivern ya shiga nima na shiga gidan gaba muka shilla titi.

Cikin hukuncin ubangiji muka iso SharaÉ—a, a baki wani tangamemen gida naga drivern ya É—an tsaya yana danna horn alamun a buÉ—e masa, niko sai Æ™arewa tsarin gidan kallo nake, har ga Allah gidannan ya haÉ—u, sai kace ba’a talauci a duniya ?” na tambayi kaina ina daÉ—a Æ™arewa gidan kallo kamar Æ´ar Æ™auye .

Tafiyar da motar naji tanayi ne ya sani, mayar da hankalina ga inda muka dosa,

Muna shiga sai na raina kaina, sbda iya haɗuwa gidan ya haɗu, gashi ƙato ga flawoyi masu kyau ga gurare daban daban, kama daga gurin wanka harda gurin lilo, can gefe kuma wata haɗaɗɗiyar kujera ce mai masifar kyau.

Bayan drivern yayi parking yayi min izini da in fito, na fito da Æ´ar jakata wacce na É—ora a kan cinyata tun shigata mota,

“Biyoni muje ciki”

“To “nace masa ina bin duk inda naga yayi.

Wata hanya mukabi wacce ta sadamu da haÉ—aÉ—É—en palon gidan, nanfa naci gaba dabawa ido abincinsa ta fannin kallon kujerun dake zagaye a palon, daga ganin tsarin gidan zaka tabbatar da naira tayi kuka, balle ka shigo ciki,

“Kizauna ”

Drivern yace min na zauna kamar inda ya faÉ—a.

Gani nayi ya tafi ya barni, bakajin ƙarar komai sai na AC daTV, a halin yanzu kallonTV baya gabana sabda, burina kawai inji inda Abbana yake,

Na jima a zaune, kafin wata farar mata mai jiki a Æ™alla zatayi shekaru hamsin ta fito, farace tass fuskarnan tata tasha fashin goshi, hannunta kuwa yaji zobunan gold, cikin fara’a ta Æ™araso ta zauna kujerar dake kallon tawa kafin tace “ashe har kun iso “,to waye ya faÉ—a mata?”,

See also  Happy Birthday to Fatima Lawan Ahmad

Katse tunanin nawa nayi da cewa “eh ina yini hajiya “,

“Lafiya lau ya karatu ya Æ™oÆ™ari “,

Na amsa da lafiya lau ina mai sunkuyar da kaina ƙasa.

Miƙewa naga hajiyar tayi taje gaban wani katon fridge mai rijiya ta ɗauko min ruwan gora, ta buɗe wani bokiti ta ɗibo min cincin da ta ajiyemin a gaban wani tabur dake gabana, har yanzu bata zauna ba naga ta wuce ciki, bata jima ba sai gashi ta fito hannunta riƙe da plet na abinci, mai ɗauke da shinkafa da miya da vegetable, ta ajiye a gabana.

“Kici Æ´ata nasan ba lallai kinci abinci ba ”

“To “kawai nace na fara cakular abincin kamar wacce take koyo,

Ban wani ci da yawa ba na ajiye cokalin nasha ruwa, ina jira inji musabbabin kawoni gidannan amma har yanzu banji tace “komai ba “,

Sai da muka É—au tsawon lokuta a zaune kafin naji tace “kece Ilham ko ?”

Na amsa da “eh hajiya nice “good babanki ne yasa a taho dake a bisa yardarsa akan cewar zaki fara aiki a gidannan, da kuÉ—in da za’a biyaki a kaishi ayi masa magani “,

Gabana na tsanannta faÉ—uwa idona ya kaÉ—a yayi jajir nace “eh na sani ina Abban nawa ?”

Hajiyar tace “yana hospital ana yi masa aikin Æ™afar “,

“Wato har Abba yakai kansa batare da Æ™ara shawartata akan ko na amince da aikin na ko ?hmm lallai Abba “,

Na faÉ—a ina ce mata “to Hajiya ko zan iya ganinsa ?”,

“Eh zaki iya ganinsa sai dai ba’a gidannan yake ba yana asibitin Murtala “, a razane na dafe Æ™irji tare da cewa “asibitin Murtala kuma ashe abin yayi yawa, nida akace yana asibitin gidannan “na faÉ—a ina share hawayen da suke ambaliya a fuskata, Hajiyar ta É—aga waya ta danna number driver, bai jima ba yazo ya durÆ™usa a gabanta, cikin bada Umarni Hajiya tace “ka kai Ilham asibitin da aka kwantar da babanta, driver yace “an gama hajiya taso muje “na miÆ™e jiki a sanyaye, dole nabar kayan anan na wuce muka shiga mota muka lula asibitin.

Muna isa, driver yayi parking tare da cewa “kiyi sauri lokacin ziyara ya kusa Æ™urewa “nayi azamar fitowa, yana gaba ina binsa a baya, har muka shiga wani É—aki mai lamba 5, muna shiga na hango Abbana a kwance an naÉ—e Æ™afarsa da bandeji , iya yau ya rame sosai, nikam na rasa ganewa shin ciwon ne ya tashi ko kuma shine ya kawo kansa har yanzu ban sami mai bani amsa ba, tarin da naji yanayi ne ya sani Æ™arasawa kusa dashi ina cewa “Abba sannu ya jikin ”

Cikin murya irin ta marasa lafiya Abba yacemin “jiki da sauÆ™i na warke yau akayi aikin zuwa jibi idan sunga jikin ya warke sunce zasu sallamemu “,nace to alhmdulilh Abba yanzu gidan aikin kenan zan koma ?”Abba yacemin eh man ai sai kinyi na wata bakwai “,na zaro ido, saboda kar in tayarwa da Abbana hankali yasani É“oye damuwata nace masa karka damu Abba, lafiyarka ta fiyemin komai a duniya, farinciinka shine nawa, samun lafiyarka itace farinciki na “Abba ya shafi kaina yana sanyamin Albarka, shigowar likitan dake dubashi ne yasa na koma kan kujera, sai yanzu driver yace “baba ya jikin dai ?” Abba ya amsa fuska a sake, “na sami sauÆ™i alhmdulilh “,

Driver yace “zamu wuce toh “babu inda na iya haka muka dawo gidan su Hajiyar, wannan karon na sameta ita da wani saurayi wanda nake tunanin kamar na san fuskar, nazari na shigayi tare da tinanin a ina na taÉ“a ganinsa ?”,

Kyakkyawan saurayi ne dogo fari tass ɗan shekara 32yrs fuskarsa masha Allah, a taƙaice dai shiɗin ba mummuna bane,

Kansa na kan cinyar hajiyar yayinda gangar jikinsa ke kan kujera 3 sitter, da sallama na Æ™arasa kafin nace “hajiya mun dawo “Hajiyar na faÉ—aÉ—a fara’arta tace “Æ´ata zoki zauna “, ta nuna min kujera mai zaman mutum É—aya, yaron nata da naji ta kira da my son naji yace “momy wannan kuma wacece ?”,hajiyar ta shafi kwantaccen gashin kansa kafin tace “,ka mance maganar da akayi da dadynka jiya akan Æ´ar aiki da kuma rashin lafiyar mahaifinta ?”gani nayi ya taÉ“e baki haÉ—i da galla min harara, nikuma sunan data kirani dashi ne yai mugun É“atamin rai, wai Æ´ar aiki mtsw.

“Oh momy yanzu taje ta gyaramin part É—ina Ibrahim na nan zuwa anjima “waro ido nayi, sbda a halin yanzu na ganoshi sarai, ga kuma yanayin maganarsa kamar ta mace, wato shine ko ?”lallai zan gasa maka aya a hannu ” na faÉ—a ina kawar dakai daga kallonsu.

Nasan shikam bai ganeni ba, amma ni na ganesa, sbda wannan Æ™aton gilashin danasa wanda ya mamaye ilahirin fuskata, jira kawai nake inji hajiyar tace “tashi ki tafi “, amma shiru ina zaune kamar gunki, ganin hajiyar bata sake wai-wayata ba, yasani kallon TV badan ina fahimtar abinda akeyi ba, kawai dai mutanen dake drama nake kallo a tashar arewa24.

Bayan wasu sa’oi,

Najiyo muryar hajiyar na cewa “ke Ilham jeki gyara part É—in my son anjima yanada baÆ™o “na amsa da toh “dama burina inbar gurin nagaji da zama agurinsu,

“Ina ne part É—in?”

“My son oya jeka nuna mata yau tazo fa “,

Fuska a yamutse haɗi da kallon ƙyama da wulaƙanci, ya yaso bai cemin komai ba ya fita a ƙofar shigowa palon Hajiyar nima na bishi,

Mun É—anyi tafiya sannan naga mun iso wata Æ™ofa mai É—auke da mudubi, yana zuwa ya danna wani abu a jikin bango naga Æ™ofar ta buÉ—e, ya shiga nima na shiga, irin haÉ—uwar palon hajiya kusan iri, É—aya da nasa, amma a nashi palon akwai wani tangamemen Frame mai É—auke da photonsa wanda ya baiyanar da kyawun fuskarsa, gashi gunin ban sha’awa murmishi yake, niko nace “duk wannan cin maganin da yakeyi dama yana dariya ?”,

“Inkin gama nuna Æ™auyancin kizo ki wanke min toilet ki gyaramin ko ina nabaki 30mins “rai a É“ace na kallesa sai kuma na sunkuyar da kai, banason in nuna raina ya É“aci ya sami damar turamin haushi, batare daya nunamin toilet É—in ba ya fice yana waÆ™a Æ™asa-Æ™asa.

Zubewa nayi akan kujera tare da zuba tagumi nace “shikenan na Æ™anantar da kaina na shiga uku, koma zagina mutan gidan sukayi haka zan daure Allah ka wadatamu “,

Cikin azama na miƙe na buɗe wata ƙofa wacce nake da tabbacin nan ne bedroom ɗinsa, sbda gado dana gani da mudubi da drowa, gadon na fara gyarawa kafin nace na wanke toilet nama rasa ya zanyi in tsara abinda zanfara, duk abinda yazo min shi nakeyi, tashi ɗaya na gama gyara komai cikin hanzari na kunna burner nasa turaren wuta ƙamshi ya game ɗakunan duka..!

 

 

*GAWURTATTU BIYAR,5🤚TAFIYAR TA MUSAMANCE*

 

 

 

1, *MU GANI A ƘASA..🔥*

_Ummu Affan_

 

2, *ABIN CIKIN ƘWAI..🥚*

_Ummu Maher_

 

3, *GUNTUN GORO..*💥

_Mom Islam_

 

4, *GISHIRIN ZAMAN DUNIYA*🌎

_Mrs Bukhari_

 

5_ *AUREN WATA TARA👩‍❤️‍👨*

_Miss Hajo_

 

 

Guda É—aya N300

Guda biyu N500

Guda uku N600

Guda huÉ—u N700

Guda biyar 1k

 

*ZAKU TURA KUÆŠINKU TA WANNAN HANYAR👇*

 

 

Fatima Rabiu Sunusi

0037219728

StanbicIBTC Bank.

 

 

Shaidar biya tanan 👇

0810 433 5144

 

 

Masu tura katin MTN👇

0814 179 9224

 

………..🥚👩‍❤️‍👨💥🌎….

 

*ƳAN NIGER GA HANYOYIN BIYAN KUÆŠINKU👇

 

Guda biyar 1000f

Guda huÉ—u 700f

Guda uku 600f

Guda biyu 500f

Guda É—aya 300f

Kai tsaye ku tura da katin Airtel ta wannan number 08141799224

 

 

 

*MUN GODE DA KASANCEWA DA GAWURTATTU TAKUN FARKO*

Leave a Comment

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Scroll to Top