
Gurbin Ido Hausa Novel Part 1
[17/10, 3:16 pm] +234 706 255 0401: *GURBIN IDO*
_Ba ido bane_
*Mallakar*
*Safiyya Abdullahi huguma*
*Arewabooks username*
*HUGUMA*
©️®️ *ZAFAFABIYAR*
*ƊANƊANO*
*Page 01*
Faffada kuma yalwataccen daji ne iya ganinka,wanda ya wadatu da korayen tsirrai da kuma shukoki nau’i daban daban,masu tsaho da kuma gajeru,ciyawa tafasa da sauran tsirrai da ubangiji ya huwace musu su wanzu a wajen,wanda wasu ma dan adam bai san meye ba,wasunsu kuma magani ne da garkuwa ga jikkunan dan adam.
Yadda sararin yayi kore shar da nau’in tsirran da kuma yawaitarsu kadai xai bayyana maka cewa muna lokacine na yawaitar saukar ruwan sama wato lokaci na damina,duk da da cewa gurin waje ne mai cike da ni’ima da kuma albarka,albarka data sanya mawuyacine ka samu wajen a bushe ko kuma a qafe…..wannan dalili ya kawo wanzuwar fulani wajen a muhallin,suka kafa bukkokinsu suka kuma tashi gagarumar ruga a wajen….saboda waje ne daya dace da muradinsu da kuma buqatar dabbobinsu,wanda buqatar dabbobin nasu sama take da tasu buqatar.
Yammaci ne lis,wanda daqiqu kadanne ne zasu ratsa magariba ta shiga,lokacine da kowanne makiyayi yake qoqarin kada kan dabbobinsu zuwa gida inda zai turkesu saboda gabatowar dare,daga cikin wannan dajin mabanbantan tawagar shanu wani lokaci harda raguna da akuyoyi ke kutsowa cikin ainihin wajen da suke kira da gari a wajensu,kowanne tawaga na tafe ne da masu kula da ita,mutum biyu uku hudu har zuwa biyar idan sunyi yawa,yawancinsu maza ne,matan dake ciki daidaiku ne.
Da sannu sannu wadan nan dabbobi ke wucewa zuwa guraben da muhallinsu yake,kamar sun gama wucewa…..saiga wani garken na daban na bullowa a hankali.
Kyawawan shanu ne tunkiyoyi raguna da kuma awaki masu tarin yawa da daukar hankali,ba komaine ya kawo haka ba sai yanayin qoshi da kuma tsaft da garken keda yashi,kusan duk dabbar dake ciki fara ce…..sai wasu daga ciki dake da ratsin ruwan qasa……duka ba wannan ne abun mamakin ba,abu mafi daukar hankali shine Kyakkyawar matashiyar dake kara kaina daga hagu tsakiya xuwa daman dabbobin tana saita su,da fari zaka zaci ba ita daya ke wannan aikin ba,amma idan ka tsawaita dubanka a kanta zaka fahimci ita kadai dince,dauke da sanda guda daya tak.
Kyakkyawa kyau na musamman kuma na asali koda cikin fulanin,irin kyan da zaka tsammaci half case ce,maimunatu nada wani irin kyau na daban wanda ke sanya duk wanda yake baqon gani a gareta ke bata lokacinsa wajen binta da kallo,saidai kuma…..duk da wannan kyau nata babu mutum daya daya aboceta wajen tahowa gida,kusan kowa ya kado dabbobinsa ya barta,babu koda mutum daya ma cikin wadanda sukayi gaba dake waiwayota ko duba halin da take ciki bare yayi niyyar tayata ta samu ta iso gida da wuri.
Kusan itama hakan bai dameta ba,duk da tanashan wahala,amma ya zamar mata jiki,ta kuma saba da yanayin……sanye take da baqin saqi maimakon farin saqi da akasan mafi akasarin fulani na tu’ammali dashi,zaka iya hangen yadda kayan suka dangale mata sosai fiye da dangalewa ta al’ada da aka saba gani tattare da fulanin,don kuwa koda rigar maimunatu tayi dagewar da banda baqar rigar yadi data saka daga ciki,babu abinda zai hana mutum ya hango albarkatun qirjinta da suka fara tasawa,sai kuma yalolon baqin mayafin data sake rufe qirjin nata dashi,duk kuwa da cewa ba wani kauri ne dashi ba,bashi da maraba da abun tace koko,hakanan bashi da tsaho,don ko mazaunanta baikai ba,tun abun yana da girma da kuma kaurinsa take amfani dashi,amma har kwanan gobe ta kasa rabuwa dashi,saboda dumbin tarihin da mayanin yake dashi a gareta da kuma rayuwarta gaba daya.
Zanin jikinta shima a dage yake sasai,kanta na sanye da Hular kaba irin wadda fulani ke yawaita amfani da ita da suke kira da(malafare)sakamakon yawaitar zafin rana ko kuma tunanin saukar ruwan sama,wadda ta baiwa doguwar jelar gashin tsohon kitson dake kanta bayyana sosai,kitson DOKA inji hausawa,su kuma suce dashi(BIƊEJI)(mai tudu daga tsakiya)shine a kanta,don haka jelar ga sauko dama da hagu na fuskarta da kuma bayanta,abinda ya qarawa kyakkyawar fuskarta kyau da kuma bayyana asalin yarenta.
Kunnenta babu dan kunne,saboda bata dashi,bata ma ta’ammali dashi,amma hannayenta cike suke cankas da duwatsu kalar kore shar da kuma ja,irin shirin duwatsun da akasan fulani dashi,hagu da damanta gaba daya,masu yawan gaske,wasu daga ciki ma sun girme mata,amma dai wasu abubuwane da bata iya rabo dasu,tana jinsu ne tamkar fitar numfashinta.
Daga qugunta salkar ruwa ce ta duma da aka fafe daure tam,abu guda daya da take da damar tafiya dashi zuwa wajen kiwo,qafafunta kuwa wasu takalman roba ne rufaffu wanda baka rasa bafulatani dashi saboda yanayin shiga daji qayoyi da sauransu,shi kadaine fari a jikinta,duk da tsufar da yayi amma fes yake,da alama ya samu kulawa.
Cikin matuqar juriya da kuma jajircewa take wulga sandar tata tana maida dabbobin hanya,duk kuwa da cewa numfashinta baya sauka zuwa cikin cikinta saboda uwar yunwar dake sakadar hanjinta kamar zata tsinka mata su,cikin matuqar kulawa take kada sandar,saboda ko kadan batasan ta samu kowacce dabba a cikinsu,wannan kusan al’adarta ne,bata dukansu,saidai duk umarnin da zata basu suna ji suna kuma biye da ita,hakan ya haifar da shaquwa mai ban mamaki tsakaninsu,idan tana magana dasu wani lokaci,kai kace tana magana ne da mutane ‘ya uwanta.
Har mantawa take cewa ba bil’adama bane kamarta,sau tari takanji sunfi mata mutanen dake kewaye da ita take kuma rayuwa a cikinsu,idan tana tare dasu,tana jin kamar bata da wata sauran damuwa,tana daukansu ne kamar wasu ‘yan uwanta.
Sannu a hankali take ci gaba da kadasu cikin juriya da qarfin hali zuwa hayar da zata sadasu da gida.
Tafiya me matsakaicin nisa suka bayyana a rugar ummaru,faffadan riga mai dauke da bukkoki masu yawa,ga wadanda suka zaunu kuma sun fara gini na jar qasa da kara wanda suka tasheshi a matsayin katanga.
Ta bayan dakunan da suke mallakin wasu suka keta,jimawa kadan sai gasu a haggo(wajen daure dabbobi),ta waiwaya a hankali tana duban sararin gidan,babu matar daya zame mata wajibi duk sanda fa dawo ta shaida mata dawowarta,wannan qa’ida ce,wadda tsallaketa ko saba mata dai dai yake da saima kanta tashin hankali da rashin nutsuwa tsahon wasu kwanaki,idan ma batayi sa’a ba,cikin duka kwanakin da zasu biyo…..za’a yita kiranta da sunan da duk duniya babu sunan data tsana sama dashi
“Miwarti inna!” Ta bude dukka kaifi muryar da Allah ya bata tana qwalawa innar kira tare da shaida mata ta dawo,saidai yanayin zaqin da muryarta ke dashi,sam bata da amsa amo ko kuwwar da kiran xai isa inda takeso
“Inna miwarti!” Ta sake fadi,saidai da alama ko kusa da inda innar take basu jita ba.
Waiwaya tayi gefe guda,yarone dan kimanin shekara takwas,zaune yana wasa abinsa,yayi fututu,kai zaka ce daga sansanin gudun hijira aka tsamoshi,kai ta jinjina,tanason tace dashi wani abu amma tana tsoro kada cibi ya zama qari,bata da zabi illa ta aikeshi ya kira innar
“Laulo,yanoddanan inna” daga kai yayi ya dubeta yana yamutse fuskarsa dake harmutse da qasa
“Owalad’o(bata nan)” ya amsa mata a tsiwace yana maida kansa ga wasansa.
Kanta ta daga sama tana kallon sararin samaniya,hadari ne yake hadowa wanda bisa dukkan alamu ba zai dadeba zai bada ruwa daga yanzu zuwa kowanne lokaci,bata qaunar yanayi irin wannan,lokacin da take dawowa daga kiwo…..cike da gajiya qishi da yunwa,take fara ta turke dabbobin a muhallinsu….ta sanar da inna ta kuma shaida dawowar tata,ta wuce zuwa cikin gida,duk da cewa koda ta wuce din bata da tabbacin samun hutun da dukka jiki irin nata daya wuni yana kara kaina tsakanin jeji da jeji a tsakiyar dabbobi,ba shakka da biyu inna ke aikata hakan a gareta,sai taja da baya kadan ta jingina da wani turke tana ci gaba da duban sama,zuciyarta cike da addu’ar dawowar inna a wannan lokacin.
Cikin matuqar d’ar d’ar take a wajen,duk da ba karatu ne da ita ba mai yawa….amma ta sani xama a wannan lokacin cikin turakun dabbobi abune mai hatsari,bugu da qari ma,a al’adarsu tasan yadda suke taka tsantsan da wajen a lokaci irin wannan.
Sosai ta lula cikin duniyar tunani a dan zaman da tayi a waje,wanda har batasan laulo yabar wajen ba,hakanan batasan hadarin ya gama hade jikinsa ba waje guda,ya kuma fara busa iska dake hade da qura,saida qurar ta gifta ta gaban idanunta,daidai sanda ruwa ya fara sauka…..dai dai kuma lokacin da idanunta suka kai mata ga dabbobin da suka tarwatse a wajen.
Da sauri ta miqe cike da fargaba guda biyu,na farko ruwan saman da zai taba jikinta duk yadda taketa qoqarin kauce masa,na biyu kuma warwatsewar dabbobin data tabbatar da cewa saita sake wani aikin kan ta hade kansu.
Tana miqewa dai dai bullowar wata mata,doguwa ce sambal,farar bafulatana ta usul,sanye da fararen kayan saqi,ta yane kanta da babban mayafi kore shar da shi,a gurguje matar take,da alama itama tana gudun tabatan da ruwan saman zaiyi
“Maimunatu!”ta qwala mata kira bayan taja birki tana hangota tsakiyar dabbobin cikin dan ragowar hasken da duhun hadari dana dare ya fara hadiyeshi
“Na’am inna”
“Muguwa!……saboda bana nan ne shine kika barmana dabbobi su wulaqanta……seto me wanna nima ɓerde(sai na bata miki rai),ki kamasu ki kallaceminsu” daga haka ta sanya kai zuwa shiyyar da dakunansu suke ganin ruwan na sake qarfi.
Abinda ya daga hankalin maimunatu kenan,ta riga data saddaqar yau din mawuyacine ta samu barci matuqar ruwan yaci gaba da taba jikinta,wani irin jiki Allah yayi mata da baya qaunar ruwan sama,indai zai tabata to lallai zata kwana da zazzafan zazzabi,amma sai gashi innar ta wuce abinta ko a jikinta,nata burin dai kawai ta tattala mata dukiyarta.
Duk da yadda ruwan yake dukanta hakata dinga kamasu tana killacewa,ta daure wata saniya tana laluben danta da aka haifa wancan satin,santsin tabon dake wajen ya debeta,ta tafi suuuuu idanunta a rufe tana jiran ta jita a qasa,amma sai taji wani abu ya cake gaban qafafunta,abinda ya hanata faduwa kenan,ya kuma sanyata bude idanunta d asauri wanda tun kan ta bude din haske ya cika idanun nata.
Tarwai ta bude manyan idanun nata da ruwa ya jiqe gashin idanun nata,kamar yadda ya jiqe na girarta da kanta yasa suka hade gaba daya,fuskarta ta sake haske ta kumayi tarwai da wani irin kyau.
Idan har idanunta dai dai suka nuna mata mutum ne tsaye a gabanta,matashin saurayi dauke da lema da kuma fitilar torch light mai tsananin haske.
Da sauri taja da baya cike da tsananin tsoro,saboda tunda take kaf kafin rugarsu bata taba sanin wannan fuskar ba,abune kuma mawuyaci indai kaidin haifaffen rugarne ka tashi bakasan dan wani gidan ba”tsaya mana” ya fadi da dan qarfin murya amma a tausashe,abinda ya dan bata nutsuwar tsaiwar,yadda take dubansa ya tabbatar masa data gamsu dashi ba,don haka yace
“Me kike a ruwa a daidai wanna lokacin a haggo?” Qas tayi da kanta saboda wadatuwar hasken da walqiya ta bayar a lokacin ya haska mata fuskarshi sosai,ta kuma so ta ganeshi
“Ina daure dabbobi ne” kamar xaiyi magana sai kuma taji baice komai ba,ya ajjiye lemar kansa gefe,ha saqale fitilar a jikinsa,ya fara kama mata dabbobin yana tayata dauresu.
Tsai tayi tana dubansa,sai kuma ta taka a hankali itama ta fara kama wadanda zaa daure din tana tayashi sunayi tare,lokaci lokaci tana satar kallonsa,kamar yadda shima yake satar kallon nata lokaci bayan lokaci,ta gaza gasgata idanunta,wani yau a rugar yasa hannunsa yana taimakonta?,abinda ba zata iya tuna lokaci na qarshe da hakan ya faru ba,rashin sabo da ganin hakan ya sanyata dari dari dashi,har zuwa sanda suka gama tas,ya qarasa wajen lemar ya dauketa yana rufeta,saboda bata da wani sauran amfani a wajensa,saboda abinda zatayi masa rigakafi dashi ya riga daya faru.
*ZAFAFA BIYAR*
*_Kundi kuma dausayin zaqaqa kuma da d’ad’an litattafan hausa masu cike da nishadi soyayya darasin rayuwa dana zamantakewa,tsantsar ilimantarwa da kuma fadakarwa_*
*Wannan karon ma gasu tafe da wasu taskirar tsararrun litattafan guda biyar*
SANADIN LABARINA
Hafsat rano
BABU SO
Billyn abdul
GURBIN IDO
Huguma
FARHATUL K’ALB
Miss Xoxo
INAYAH
Mamuhghee
Dukka guda biyar din akan
1k
Guda hudu:::700
Guda uku:::500
Guda biyu:::400
Guda daya:::300
*_Garzaya ki biya naki a fara a kan idanunki ta wannan account din_*
Hafsat Kabir Umar
2270637070
Zenith bank
*Saiki tura shaidar biyanki*
07040727902
*MASU KATIN WAYA ZASU TURAWA WANNAN NUMBER TARE DA SHAIDAR BIYA*
09134848107
*_KARKU MANTA…..HAR KULLUM,SIYAN NA GARI MAIDA KUDI GIDA NE_*
[17/10, 3:16 pm] +234 706 255 0401: *GURBIN IDO*👀👀👀
*Free page 02*
“Migodake” ta fada a hankali tana sharce ruwan fuskarta,dubanta yayi,ya sakar mata murmushi,wani abu me suna nutsuwa da sanyin halin daya karanta tattare da ita na dan qaramin lokaci yana burgeshi
“Karki damu,ba komai” kai ta jinjina,saita juya tana nufar cikin gidan tana qudundune jikinta waje daya saboda yadda sanyi ya fara ratsata,da alama akwai damuwa kenan,yayin da shi kuma ya juya ya dauki torch dinsa ya fara gangrawa yana barin wajen,saidai sau kusan uku yana waiwayarta kafin ta qule masa yabar ganinta,ya sauke ajiyar zuciya yana maida hankalinsa sosai ga hanya,zuciyarsa na qissima masa ita,tsahon wanzuwarsa a rugar bau taba kula da ita ba,hakanan bai taba ganin macen da Allah ya zubawa kyau me sanyi da tsari irinta ba,ko wacece ita?,da wannan tunanin ya isa kofar wani gida,wanda shi dayane kaf kafin wajen dake dauke da ginin qasa da bulo.
Babban tsakar gidane daya kasance wayam babu kowa saboda ruwan daketa sauka,yakai dubansa ga dakunan dake jere a tsakar gidan,har ya nufi wani daki daga ciki,sai kuma ya dakata ya juya akalarsa zuwa wani daki dake daura dashi,muqullin ya taba,a rufe dakin yake dole dai ya karbo muqullin,abinda yasa ya juya da dan sassarfa ya nufi daya dakin,yasa hannu ya dage asabarin da aka saukema qofar dakin saboda kaucema shigar ruwa.
Dumine ya fara dukan fuskarsa kafin hasken fitilar aci bal bal dake dakin ya cika masa idanu,matasan mata ne guda biyu da yaro namiji guda daya zagaye da fitilar,kowannensu d kwanon tuwo a gabansa yana ci,sai babbar mace guda daya da alamu suka nuna mahaifiyarsu ce zaune gefe daya tana dubansu,jikinta nannade da mayafi me kauri,da alama sanyi takeji
“noi saare daada”
“Jam….alhamdulillahi,ina ka tsaya?,inata taraddadi ruwan nan sai daya dakeka” murmushi ya saki
“Zan canza kaya daada,a bani maqulli” hannu ta miqa wata qwarya dake kusa da ita da alama a nan take ajjiye ajjiyenta ta dauko,ta miqawa daya daga cikin yaran
“Nabugol(karbi)” ta fadi,sai yasa hannu ya karba din,sannan ya miqe zuwa inda yayan nasa ke tsaye
Cikin girmama ya miqa masa muqullin yana cewa
“Hamma…..” Dakatar dashi yayi
“Micanjato kayaa sadam,ina zuwa”
“To” ya amsa yana murmushi,saboda ya qagu ya bashi labarin dake bakinsa,a nutse ya juya ya fice daga dakin ya sake nufar dakin da yayi nufin shiga dazu.
Batayi wani hanzari ba wajen isa dakinsu,saboda ta riga data jiqe,kuma koda ta isa dinma tasan bata da wani wajen zama daya wuce bakin qofa,dakinsu ne su biyu,amma kuma ya zama gaba daya kamar mallakin mutum guda,wato ‘yar uwarta gaaje.
Cikin kula da takatsantsan ta dage assabarin dakin,hasken fitilar dake dakin ya bayyana,motsin shigowarta ya sanya matashiyar dake amsa sunan gaje din daga kanta tana dubanta,gabanta akushi ne madaidaici cike da dambu tana ci,wanda shine yawa yawan cimarsu,tuwo ko dambu,ba kasafai zaka gansu da shinkafa ba
Wani kallo ta watsa mata kamar wadda taga qullin kashi
“Dirdutu malama(matsa malama)” tasan neman bala’i ne kawai irin na gaje,amma inda take tsaye ma sam bashi da alaqa da wajen da gajen ke zaune,sai ta matsa gefan don kawai a zauna lpy,ta miqa hannunta zuwa ga wata tsohuwar baqar jakar bacco dake saqale jikin bango,darajarta wajen maimunatu dai dai yake da akwati a wajen kowa,duk kuwa da cewa duba daya zaka yimata kasan cewa ta sha duniya ta kuma ji jiki,a nan din take ajjiyar duk wani abu nata,duk da dewa ba komai ta mallaka ba face kayan saqinta kala daya da take boyansa saboda sallah ko wani sha’ani idan ya tashi,duk da cewar ita din ba shiga jama’a take ba,rayuwarta na maqale da wani tabo da ya hanata duk wani ‘yanci da walwala da kowanne dan adam kan samu,laifin da bata da masaniya a kansa,bata kuma san sanda aka aikatashi ba.
Kayan jikinta ta zame ta matsesu da kyau daga bakin bukkar tasu,sannan ta dawo ta daura wani fallen zani guda daya da take rufa dashi,ta tara hannu a ruwa bunun dake sauka ta dora alwala,sannan ta dawo ciki ta tada sallah.
Sallar magrib ce kawai a kanta,saboda koda wajen kiwo bata wasa da sallarta sam,duk da ba ilimin addini gareta ba mai wani zurfi,amma tun kafin takai haka,zamanin da take rayuwa da mahaifiyarta ta koyar da ita yin salla da zarar lokacinta yayi,abu guda daya da ba zata manta da shi ba,ta kuma riqeshi har yau da kyau,kasancewarta mutum da bata da yawan mantuwa da kuma qwaqwalwa mai yawan riqe abu.
Da kyar takai sallar da takeyi din saboda tsananin yunwa,takai dubanta ga kwanon da gaje ke cin abinci,tuni ta hallakeshi,dan abinda yayi saura a ciki bazai wuce loma biyu ba,ya tabbata bata da abincin dare kenan duk da dan karen yunwan da take ji?,ta rasa wanne irin azanci ne wannan….tare inna ke hada musu abinci ita da gaje,bayan bambancinsu da gajen kwatankwacin bambacin sama da qasa ne,saboda gaje irin mutanen nan ne masu shegen cin abinci,kamar ci suka kawo duniya,duk yawan abinci sai sun tasheshi….yayin da maimunatu ta kasance wata irin mace,duk yawan yunwar da takeji dan abinda zata ci maka bai taka kara ya karya ba,har wani lokacin ma idan kawai nono tafi ganewa tasha shi ko ajiyayyar madara idan tana da sauranta,kusan duk sanda aka hada musu abinci da gaje sai gaje ta kusan cinyewa ko ta cinye ma sannan take tunawa da ita,duk da cewa a yawancin lokuta bar mata take yi,amma duk lokacin data ratso da tsautsayi irin haka tana jin yunwa tofa saidai ta lashi walqiya ko ta nemi ma duk abinda zata ci din,gajen duka duka sa’anni suke da maimunatu,har maimunatun ma ta bata tazarar kwanaki masu dan dama a duniyar.
“Gaje ya baki ragemin ba?”
“Idan kina da wani ma ki qaro min” ta bata amsa tana sude hannu tare da ture kwanon da qafa ta gicciye anan wajen tana sakin gyatsa.
Fararen idanunta masu sheqi ta dauke daga kan gajen,dan qaramin bakinta mai dauke da jajayen labba yana motsawa kamar zata ce wani abun,saidai ba komai zata fada din ba,zallar bacin rai ne qasan ranta,wanda bata isa ta furta ba,bata jun a daren zata iya runtsawa matuqat bata sanyawa cikinta wani abun ba,ga gajiya da takeji tana nuqurqusar qashinta tare da qaramin zazzabi da taji ya fara lasarta,wanda dama tana tsammanin zuwan nasa.
Tsam ta miqe tana leqen waje ta qaramin window din cikin ginin bukkar,ruwan yadan sassauta,amma yana sauka kadan kadan da dan qarfinsa,saita dage qofar ta sanyo kai zuwa waje.
Gabanta na faduwa amma ta daure ta qarasa qofar dakin inna,sallama tayi,shuru ba’a amsa ta ba,ta sake sallama,a sannan aka amsa daga ciki a tsawace
“Wai waye!?”
“N…..nice inna?” Kamar ba za’a fito ba sai kuma ta jiyo motsinta,ta dage labulen ta fito tana mata wani duba daga sama zuwa qasa
“Menene kuma?” Sunkui da kanta maimunatu tayi
“Yunwa nakeji inna”
“Shine kika zo ki cinyeni?” Amsar data sanya maimunatu daga kanta da sauri tana duban innar hadi da girgiza mata kai
“A’ah inna”
“To meye?,bayan kinsan na hada muku abinci da gaje?”
“Ta cinye inna”
“Kina kallonta ta cinye?,to babu wani sauran abinci cikin gidan,saiki kwanta haka,kyaci gobe”
“A’ah,ba za’ayi haka ba” sukaji an fada daga bayansu,rabewa maimunatu tayi gefe daya,ko bata juya ba tasan waye,mutumin da shi kadai yayi saura wanda yake dubanta da idanun rahama,ya qaraso garesu yana sanye da rigar ruwa,da alama dawowarsa gidan kenan.
Da sauri maimunatu ta karbi kayan hannunsa tana tayashi saukewa hade dayi masa sannu da zuwa,inna na daga tsaye tana zabga mata harara amma bata kulaa da lamarinta,don ba zata iya ganinsa da kayan bata karba masa ba
“Yaya mutum zai kwana da yunwa……ki debar mata cikin nawa mana” tuni ta cika dama tayi fam da yadda yake nuna kulawarsa akan maimunatun,uwa uba kuma ya buda ledar hannunsa ya bata bread cikin tsarabar da yayo
“Wallahi ba zata ci ba….koda abincinka ne kuwa”
“Ka barshi bappa,zanci wannan” maimunatu ta katsesu da sauri,saboda tasan muddin jayayyar taci gaba to la shakka a kanta abun zai qare,inna zata yi mata hukunci ne wanda ba zataji dadinsa ba,sannan babu abinda zai sanya innar ta sauya rantsuwarta,saboda ba wai tsoro ko shakkar bappan take ba,duk da tasanshi farin sani,yana sakar mata ne,saboda kasancewar maimunatu daga tsatsonta ta fito,shi yasa yake dage mata qafa,baya zaqewa cikin al’amarinsu da yawa
“Shikenan,balejam(mu kwana lpy)”
“jam” ta amsa tana juyawa da dan hanzarinta tabar wajen zuwa nasu dakin.
“Kiji tsoron Allah fulera,kiji tsoron randa Allah zai kamaki da haqqin marainiya” daga haka ya dauka ledarsa ya rab’eta ya wuce ciki,ta bishi da harara,sannan ta sauke idanunta tabi hanyar maimunatun ta wuce da hararar itama har zuwa qofar dakin nasu,sannan taja qwafa tana sakin labulen
“Tsoronka da zanji,rashin godiyar Allah ne yasa baka ganin qoqarina ai,banda ni ma waye zai riqeta?” Taci gaba da mita abinta,saidai ko daga kai bappa jauro baiyi ba bare ya kalleta,idan da sabo ya riga ya saba da halayyarta.
Saman shimfidarta ta koma ta zauna sannan ta bude ledar biredin,a hankali ta dinga yaga tana turawa,cikin ranta tana godewa Allah da ya turo bappa jauro,da haka zata kwana da tsohuwar yunwarta.
Yadda biredin ya fara mata go slow a wuya ya sanyaya bisa dole ta miqe cikin raunin da jikinta ya fara yi ta lalubi wani tsohon kofi nata ta tsiyaya ruwa a jallonsu dake dakin,ta sake komawa ta zauna,tana ci tana korawa da ruwan,kafin sannan tuni bacci yayi gaba da gaje,wadda maimunatu bata da tabbacin tayi sallar magariba bare isha’i.
Jahilci ya sanya gaje da wata ire irensu sam basu baiwa ibadarsu muhimmanci,duk da cewa akwai makarantar islamiyya guda daya tal,wadda anan ake koyarwa da kowa da kowa cikin rugar tasu,maza da mata yara da manya,cikin hobbansa da malaman ahlussunnah sukayi suka kawo musu malami bafulatani irinsu yake zaune dasu.yana koyar dasu,saidai ba kowa bane ya fahimci alfanun hakan ba bare har yace zaije,da yawa wani kallo sukewa makarantar,dai daikunsu ke zuwa.
Tana da.matuqar buri da kuma sha’awar kasancewarta daliba a makarantar,saidai inama taga lokacin da zai zama rara(saura) a gareta tsahon wuni guda,wanda bata bautar komai,da gar zatayi.amfani dashi ta ziyarci makarantar da sunan daukan karatu,kullum aiki take,babu dare ba rana,ba asabar babu lahadi,kamar yadda babu alhamis babu kuma juma’a,koda makara tar bokonsu dake da dan karen nisa,koda yuashe maimunatu mafarkin zuwanta take,bare wannan dake kurkusa dasu,gaje nada dama mai yawa da zata iya zuwa makarantar,saidai sam ita ba wannan bane a gabanta ba,bata taba ma kwatanta zuwa din ba.
Dai dai lokacin da gari ya sake daukan shuru bayan daukewar mamakon ruwan saman…..dai dai lokacin da wata iska me sanyi ke kadawa,a wannan lokacin zazzabi ya fara saukar mata,yana murqushe duk wata gaba dake da sauram qwari a jikinta,takurewa tayi sosai waje guda,tana jin yadda zazzabin ke ratsawa ta qashi da tsokar jikinta,a hankali yana saukar mata da sanyi da wani irin radadi,saita cure waje daya,numfashinta na fita da qyar tana kokawa dashi.
Duk da cewa wannan din ba baqon yanayi bane tare da ita,amma shi ciwo ba’a taba sabo dashi,ta jima cikin wannan yanayin tana kokawa da numfashinta,tana hangen kanta tsakanin rayuwa da mutuwa kafin ubangiji cikin tausayinsa rahamarsa da kuma jin qansa ta fara samun sassauci,numfashinta ya fara komawa dai dai,saidai qirjinta dake riqe da kuma ciwon dake ratsawa cikin jikinta yana sandarta a hankali,har wani wahalallen bacci yayi awon gaba da ita.
***********
“Maimunatu!…..maimunatu…..” Can tsakiyar baccinta….sannan cikin tsakiyar kwanyarta taji ana ambatar sunanta,shurin da aka kaima gefan cikinta shi ya qarasa tabbatar mata da cewa ba cikin duniyar mafarki take ba,abinda ya sanyata zumbur ta miqe daga kwanciyarta,sai kuma ta sanya hannayenta guda biyu ta dafe kanta tana furta
“Innalillahi wa’inna ilaihi raji’un” saboda wani nauyi da taji kan nata yayi mata,baya ga dan karen ciwon da yake mata
“Ke yafi kamata a jawa innalillahi,akalluɗo(muguwa)” inna dake tsaye bisa kanta ta fada cikin fushi,bata ko motsa ba bare tace wani abu,kanta na qas tana jin yadda zuciyarta ke suya,jikinta ke tsami da kuma ciwo saboda ciwon dake jikinta
“Ananata haala maimunatu?(bakyajin magana maimunatu ko)da kika zo kika kwanta kina barshi,waye zai miki tatsar nonon,waye zai fita da dabbobin?,ko uwarki ce zatazo tayimin?” Idanunta ta runtse,tana jin xafi cikin zuciyarta fiye da kowanne irin zafi,koda wasa bata qaunar inna ta dinga sanyo mahaifiyarta cikin kowanne irin sha’ani ko laifi da zata aikata mata,ta kuma tabbatar ci gaba da shurunta xai bawa innar dama taci gaba da zagin nata ne,don haka cikin murya mai cike da rauni tace
“Minyauɗo inna(bani da lafiya inna)” idanu innar ta qanqance tana dubanta
“Wannan keta shafa,yahudillo durgul,wurtawa(zo ki tafi kiwo,fito)” ta fada a tsawace kamar zata finciko maimunatun.
Bata da sauran zabin da ya wuce ta miqe din kamar yadda inna fa buqata,duk kuwa da yadda takejin jikinta,ta dafa a hankali ta miqe tsaye,a sanda innar ke mata wani kallo
“Nikam kin zamemin alaqaqai masifa” saita juya ta fita zuwa waje tana zazzaga masifarta,idan lokacin ka shigo gidan zaka tsammaci wani mummunan abu maimuntun ta aikatawa innar.
Kayanta data saqale.jiya ta miqa hannu cikin juriya ta cirosu,hawaye me dumi ya subuce mata,ta zame zanin jikinta,ta fara shirya kanta a cikinsu,babu batun wanka bare akai ga abinci,dama bata lafiyarta take ba
“Wurtawa fa maimaunatu” ta tsinkayo muryar innar tana fada cikin salo na azalzala
“Mihosh shawai filkul(dan kwali zan dauko)” maimunatun ta fada tana duqawa a hankali ta dauki dan yalolon dan kwalinta ta dora kan sassalkan gashinta dake cure waje daya cikin kitson doka(bijaɗe a fulatance),sannan ta matsa zuwa bakin kofa tana laluben wuffajen ta(asalin rufaffen takalmin da fulani ke amfani dashi wajen kiwo.
Ba zata iya duqawa ta sakasu yadda ta saba ba,dole sai datakai qasa ta zauna dirshan sannan ta samu damar sanyasu ga qafafuwanta,ta miqe tana riqe da sandarta tana takowa zuwa tsakar gidan nasu iska na kadata.
Kamar kullum babu kowa a tsakar gidan,daga inna dake can rumfar da suke girki,sai gaje dake zaune tana cin tuwo,tuwon da take da tabbacin da safen akayishi,amma bata da darajar da za’a bata ta sanyawa cikinta,ko don darajar bautar da zata fita yi musu.
Ganin tuwon ya tuna mata da guntun biredinta na jiya,ta sanya hannu ta dafe qaramar jakar da take daureta a qugunta taji tudunsa tabbacin yana nan,sanna ya fara takawa zuwa ma’adanar dabbobin,muggan kalaman inna sunayi mata rakiya,har zuwa sanda ta kammala kunce na kuncewa,ta kuma fara kadasu suka dauki hanya.
❤🔥❤🔥❤🔥❤🔥❤🔥❤🔥❤🔥❤🔥❤🔥❤🔥❤🔥❤🔥
*_ZAFAFA BIYAR din samari ne a rayuwar INAYAH,kowanne a cikinsu akwai wani murdadden Al’amari da ya shata layi tsakaninsa da ita,wawakeken sirri wanda a koda yaushe take kiransa da SANADIN LABARINA_*
*_Amma babban abun mamakin a koda yaushe shine,ita dai tasan cewa BABU SO tsakaninsu MEYA KAWO SHI?_*
*_Duk da haka tana tunanin yun qundun bala ta fitar da FARHATUL K’ALB a cikin ZAFAFA BIYAR din samarinta,duk da batason su zame mata GURBIN IDO wanda har kullum ba ido bane_*
😄😄😄😄😄😄😄
*YA KUKAJI SALON MASU KARATU?*
*YADDA SALON YA BAMBANTA DAKO YAUSHE HAKA LABARAN SUKA BAMBANTA DA DUKKA LABARANMU NA BAYA*
INAYA(riba biyu)___mamughee
SANADIN LABARINA___Rano
BABU SO___Billynabdul
FARHATUL K’ALB___Miss xoxo
GURBIN IDO____Huguma
*ZAKI YARDA AYI TAFIYAR NAN BABU KE MADAM?*
*_GARZAYA KI BIYA NAKI KUDIN KAN FARASHI KAMAR HAKA_*
Biyar:::1k
Hudu:::700
Uku::::500
Biyu::::400
Daya:::300
*_zaki saka kudin ta wannan account number din_*
HAFSAT UMAR KABIR
2270637070
Zenith bank
*Saiku tura shaidar biya zuwa ga*
07040727902
*IDAN KUMA KATIN WAYA NE ZAKU TURA TA NAN TARE DA SHAIDAR BIYAR*
09134848107
*_THANKS FOR CONTINUES PATRONAGE_*🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰
[17/10, 3:16 pm] +234 706 255 0401: *_GURBIN IDO_*
*Huguma*
*Free page 03*
Duk wani taku da takeyi tana yinsa ne da taimakon sandar dake riqe a hannunta,a yau madadin sandar ta zame mata ta saita dabbobin da take jan ragamarsu,sai ta zame mata mataimakiya wajen sanya diga diganta zuwa qasa.
A yau din da baki ta.dinga saitasu tana basu umarni,duk da yadda magana ke mata wuya ainun,duk kalma daya idan xata fitar sai taji kamar kanta zai tsage,sun dan dauki lokaci kafin su isa inda suke qyale dabbobin,kowacce ta ni’imtu ta kums amfana daga rahamar ubangijinmu.
Tana isa kamar koda yaushe,mabanbantan makiyaya dake wajen kowa ya fara qoqarin tattare dabbobinsa don gudun afkawa ko cakuduwa da nata dabbobin,ba yaune farau ba,nan da anjima kadan ma tana iya ganin wajen babu kowa sai ita daya da nata dabbobin,abune data saba da ganinsa,canfi ne da suka riga suka dasawa ransu,wanda batasan ranar da zai goge ba,hakanan babu me cire musu shi sai mahaliccinmu.
A yau dinma bata damu ba kamar kowanne lokaci,bayan ta tabbatar da sun iso inda ya dace,saita fara zame jikinta daga cikinsu,tana wara manya kuma fararen idanunta da kalarsu ta jirkita saboda zafin ciwo dana zazzabi,tana neman inuwar da zata dace da ita.
Babbar bishiyar mangwaro ce,mai yawam sanyi da kuma inuwa,wadda bata da wani tsaho.mai.yawa amma sai yawan ‘ya’ya,daga nan inda bishiyar take basu da nisa da inda zata hangi dabbobinta,hakanan ba nisa da inda zata gangara dasu susha ruwa da zarar lokacin hakan yayi.
A hankali ta zame malafare(hular kaba da suke amfani da ita” ta ajjiye a wajen,duk da hular ba nauyi gareta ba,amma sai takejin kamar ta dora wani dutse saman kanta,ta zare jakar dake qugunta itama ta ajjiyeta,da zata iya kwanciya zatayi,amma tana jin nauyin sallar da batayi ba takai mata ko ina,don haka ta juya zuwa sashen da ruwa ke gudana,ta daura alwala ta dawo ta tada salla saman dankwalin kanta data cire ga yane kanta da mayafin da akoda yaushe bata rabo da yafashi,duk kuwa da cewa baqon abune cikin al’adarsu,zata iya cewa ma kaf fadin rugar ita daya ce cikin matasan yara masu shakaru irin nata dake amfani dashi.
“Maimunatu!…..maimunatu” da sauri ta daga kanta daga durquson da tayi masa,tana ware idanunta cikin matuqar kaduwa da razana,murya mafi muni da razanarwa a wajenta…..muryar da mamallakin muryar abubuwane da tunda take a rayuwarta bata taba jin abinda ta tsana cikin duniyarta sama dasu ba
“Yaushe ya dawo?” Ta jefawa kanta tambayar tana wurga idanunta don tantance daga wanne bangare yake dosota.
Daga can nesa ta hangeshi,tsabar kauri da qarfin muryarne ya sanya ta dinga jinta kusa da ita kamar yana gab da ya cimmata,qasa tayi sosai don kada ya hangota,sannan ta miqe a hankali,ta tattare dankwali hula da jakarta waje daya ga wurga saman bishiyar da take zaune qasanta,karo na farko da tayi ala wadai da rashin iya koyan hawa bishiya irin nata,saita saita mayafinta ta lullube jikinta da kyau,sannan ta zagaya ta bayan bishiyar ta lafe sosai a jikinta,ta yadda zata iya hangoshi,zuciyarta na wani buguwa ɗik ɗik,tana cike da fata da kuma addu’ar rashin samun sa’ar ganinta.
Dube dube da waige waige ya shiga yi,yana kuma sake qwala mata kira iya qarfinsa,fuskarsa a firgice da alama ya zaqu da son ganin nata,bai kuma tsammaci rashin samunta a wajen ba,dube dube yaci gaba dayi,yana sake kiran sunan nata dai,har zuwa sanda ya sare,jikinsa da zuciyarsa kuma suka gaya masa bata a kusa
“Kayyasa” ya fada da kaushin murya,yana kaiwa bishiyar dake kusa dashi karta da wani kakkaifan abu dake hannunsa,da sauri ta zame kadan saboda gudun samuwar ciwo a jikinta,saura kadan kartawar da yayi ta hada da tsintsiyar hannunta,ta dauke numfashinta cak sanda yake sake takowa da baya,sai kuma ya dura wata ashariya,yasa giyaa zuwa gaba ya taka ya fara barin wajen.
Bin bayansa tayi da kallo farincikin boye masan da tayi yana saukar mata,kwata kwata kuma ko sau daya bata taba yiwa buderi kallon mutum mai hankali ba,hasalima tsoro yake bata ainun,buderi kenan,baqin bafulatani na usul,wanda ke ciie da wasu irin baudaddun halaye na wauta jahilci da hauka,irin nau’in haukan da jahilcin ne ke haifar dashi,zuciyarta cike take da mamakin me yasa shi din baya gudunta kamar yadda sauran samarin qauyen ke gaza rabarta bare su furta mata kalmar so?,me yasa shi bai gujeta ba?,ta jima tana yiwa kanta wadan nan tambayoyin.
Sai data tabbatar da cewa ya yiwa wajen nisa sannan ta fito,zuwa sannan zazzabin jikinta yayi wata irin saukar da babu shiri,sai sauran dumi,ciwon kai mai tsanani saboda razana da bayyanar buderi da kuma ciwon jikin da har yanzu tana jinsa shima,ta tako a hankali ta dawo ainihin wajen da ta fara zama da farko,tana tattare jikinta waje daya.
A nutse yake takowa yana kuma sake nazarin rigar tasu,yanayin yadda ko yaushe take bunqasa da tarin dabbobi da albarkar kiwo kusan ya zarce na kowacce ruga dake maqwabtaka dasu,ni’imar dake wajen ta banbamta daya sauran yankuna,hakan shi ya sanya yanayin wajen da rayuwarsu t bambanta data sauran sassa.
Tun daga qasan ruhinsa zuwa saman fuskarsa cike take da wani irin nishadi,tun daga daren jiya da yayi gamo da ita…..har kawo warhaka da yake takowa cikin rugar tasu daga doguwar tafiyar da yayi zuwa cikin ainihin garinsu,tunaninta,siffa da kuma kamanninta basu bace daga idanunsa ba,duk sanda siffarta zata wulqa cikin idanu da tunaninsa sai ya samu kansa da subucewar murmushi,wani lokaci hatta da haqoransa sukan bayyana,nuni da girman nishadin da zuciyar tasa take ciki.
Goye yake da baqar jaka,yana sanye da baqin wandon jeans,sai asalin rigar fulani dake jikinsa mai gajeran hannu,daga ciki kuma t.shirt ya sanya mai dogon hannu saboda hana bayyanuwar dantsen hannunsa,saman kansa ma hular fulanince,sai qafarsa dake sanye da wani rufaffen baqin takalmi na danqo.
Ba qaramin qara masa kyau da haiba kayan sukayi ba,sun kima fidda ainihin salsalarsa na bafullacen usul,duk da kana dubansa zakasan cewa ya dan banbamta da sauran matasan fulani irinsa dake rayuwa cikin rugar,akwai wani banbanci na daban da kuma haske tattare dashi.
Hakanan kawai zuciyarshi ta bashi yabi ta gefan ruwan,yana da tabbacin hakan zai qara masa nishadi,bayi wata wata ba yabi shawarar zuciyarsa,yana tafe yana kallon yadda dabbobin dake baibaye da gefannin kogin keta kaima cikinsu ruwan.
Da kallo yaci gaba da.binsu yana sake takawa izuwa gaba,babban abinda ke sake hanashi sakewa da garin kenan,had’akar ruwan sha a gurbi guda tsakanin dabbobi da kuma al’ummar yankin,daya daga cikin burin da yake dashi idan har Allah ya cika masa burinsa,banbance ruwan shan dabbobi dana mutanensa.
Dauke idanunsa yaso yi,saidai daga gefe guda dab da rafin wani abu ya dauki hankalinsa,ya rage sassarfar da yake a tafiya,ya sake qura mata idanu saboda tabbatar da hasashensa,shin itace koba ita bace,bashi da sauran zabi.bayan ya tabbatar da ita dince illa bin umarnin zuciyarsa dake azalzalarsa yakai gareta,ko zai rabauta da daddadan sautin nan da take magana dashi a koda yaushe.
“Assalamu alaikum” ta tsinkayi sallama daga gefanta,bata tsorata ba duk da bataji takun tafiya ba darajar sallamar da aka gabatar mata,sai ta cira kanta dake boye tsakanin qafafuwanta.
Fes ta zubesu a kansa,tadan tsura masa idanu na wasun gajartattun mintuna,qwaqwalwarta da zuciyarta nason tuna mata fuskar,ba tare da daukan dogon lokaci ba ta harbo mata wayeshi,mutumin da ya fara taimakonta tsahon xamanta a rugar ummaru,bai kyautu ba ace ta manta fuskarsa haka da wurwiri ba.
Dukkan jarumta da juriyarta ta tattaro,ta sake masa murmushi wanda yayi fidda wani boyayyen kyau dake kwance saman fuskarta
“Yallijam(ina yini)” ta furta da sassanyar muryarta tana sauke qafafunta dake takure cikin jikinta kai tsaye sukayi masauki cikin ruwan dake gabanta,sai daya maida mata da murtanin murmushinta,yana jin wani.abu na narka zuciyarsa sannan ya amsa mata
“Jam….alhamdlh” ya amsa mata idanunsa bisa kanta,tana wasa da qafafunta cikin ruwan
“Nobaluɗa ke`yen(ya kika kwana jiya)”
“Lafiya alhmadlh” ta amsa masa tana masa kallo daya,saita maida idanunta ga ruwan ganin ita yake kallo
“miyatti fa,na gode sosai da alkhairinka na jiya”
Karamin murmushi mai sauti ya sake sannan yace
“ko’en waɗi ken yen?(me akayi jiyan?” Dubansa ta danyi cikin mamaki,sai kuma ta kawar da kai ganin kallonta yake,shuru ne yadan ratsa a tsakaninsu,kafin ya buda bakinsa a hankali cikin nutsuwa yace da ita
“Anaunaaki nke’yan?(bakiji ciwo ba jiya?)” Hannayenta ta kalla a hankali,tana jin yadda jikinta yake mata babu dadi
“Eh” ta amsashi a hankali,sai shuru ya sake wanzuwa a tsakaninsu,jifa jiya yake satar kallonta,yana son sake mata magana ne,akwai abubuwan da yakeson sani game da ita,bazai yiwa kansa qauron baki ko ya cuci kansa ba,kansa tsaye zai iya fadima kowa cewa daga jiya zuwa yau din ta sace zuciyarsa,ta kuma tafi da hankalinsa,dan zaman nan kuma da sukayi na wasu gajerun mintuna ta sake burgeshi qwarai da yanayin tsarin dabi’arta,yawan shuru shuru da kuma alamun cikakkiyar nutsuwa,dukka sun nuna kansu tattare da ita
“No’indema surbajo(ya sunanki ne ‘yammata?)” Ya fada yana kallonta,fuskarsa qunshe da murmushi,yanayin yadda ya furta maganar tasa maimunatu jin wani banbarakwai
“Inde’an maimunatu,daada ta tana cemin diyam” ta fadi maganar wani abu yana motsa zuciyarta,don har sai da hakan ya nuna a saman fuskarta,kai ya jinjina
“endema eweli (Sunanki nada dadi….ni baki tambayi nawa sunan ba” satar kallonshi kadan tayi,bataga amfanin tambayar nashi ba,saidai tana duba da alkhairinsa gareta,don haka tace
“No’indema” murmushi ya saka kadan sannan yace
“Ibrahim…..anfi kira na da himu” kai ta jinjina kawai ba tare data ce komai ba,dukkansu idanunsu kan ruwan dake wucewa ta gabansu
“Deko tata nwulo?(yaushe zaki tafi gida?)”
“joni(yanzu)” ta samu kanta da fada,duk da ainihin abinda yake cikin zuciyarta kenan,saidai tana tunanin komawar,bataso taje ta tadda bud’eri cikin gari yana jiranta,tanajin kamar taci gaba da zamanta cikin jejin,saidai kuma dole ta koma gida,ko don yadda takejin yanayin jikinta a yanzu.
“Amma kamar lokacin komawa bai qarasa yi ba ko?” Himu ya fada bayan ya gama qarewa sama kallo,wadda keda sauran rana tarwai,kai ta gyada,sai taji bata sha’awar fada masa qarya,yar kulawa daya nuna mata daga jiya zuwa yau takejin girmanta har ranta,tunda abune da bata saba ganinsa ba
“Minyauɗo(bani da lafiya)” tayi maganar kanta a qas,zuciyarta na karyewa
“Subhanallah” ya fada cikin rudewa kadan yana dubanta
“Tun yaushe?”
“Jiya” ta amsa masa a taqaice
“amma hanjun foɗi gurtoyiɗa durgul?ginɗimu?(Amma shine kika fito kiwo,me yasa?” Shuru tayi ba tare data furta komai ba,shi kuma yayi tsaye yana jiran amsarta,amsar da bata da ita,tunda batasan me zata gaya masa da zai fahimta ba.
Ganin bata da niyyar cewa komai,da alama shuru shuru da rashin sonyin magana cikin jininta da halayyarta suke,sai ya miqe yana ajjiye jakar dake goye a bayansa yana cewa
“kowanna tama?(me yake damunki?”
“Zazzabi ne”
“qila inpab ɓoje(wataqil malaria ce)” shuru tayi masa,duk da tasan cewa ba malaria din bace,har zuwa sanda ya yiwa jakar ma’ajiya
“imi wara(Ina zuwa” ya fada yana takawa zuwa wata hanya da zata fiddaka daga wajen kiwon gaba daya.
Binsa tayi da kallo,ko waye shi?,me yasa yake rabarta?,baisan wace ita ba?,maganganun ‘yan rugar tasu dangane da ita bai iskeshi ba?,saita maida idanunta ta lumshe ta sake budesu kan jakarsa daya ajjiye gefanta,ta kalli jakar me kyau da ita,kuma fes take,da alama tsafta ta wadaceta,tun ganin farko data masa zuwa yanzu ta tabbatar ga banbanta da dukka sauran mazan qauyen,ta kwantar da kanta saman cinyarta tana tariyo magangun da sukayi dashi daga jiya zuwa yau.
*Arewabooks username*
*HUGUMA*
❤🔥❤🔥❤🔥❤🔥❤🔥❤🔥❤🔥❤🔥❤🔥❤🔥❤🔥❤🔥
*_ZAFAFA BIYAR din samari ne a rayuwar INAYAH,kowanne a cikinsu akwai wani murdadden Al’amari da ya shata layi tsakaninsa da ita,wawakeken sirri wanda a koda yaushe take kiransa da SANADIN LABARINA_*
*_Amma babban abun mamakin a koda yaushe shine,ita dai tasan cewa BABU SO tsakaninsu MEYA KAWO SHI?_*
*_Duk da haka tana tunanin yun qundun bala ta fitar da FARHATUL K’ALB a cikin ZAFAFA BIYAR din samarinta,duk da batason su zame mata GURBIN IDO wanda har kullum ba ido bane_*
😄😄😄😄😄😄😄
*YA KUKAJI SALON MASU KARATU?*
*YADDA SALON YA BAMBANTA DAKO YAUSHE HAKA LABARAN SUKA BAMBANTA DA DUKKA LABARANMU NA BAYA*
INAYA(riba biyu)___mamughee
SANADIN LABARINA___Rano
BABU SO___Billynabdul
FARHATUL K’ALB___Miss xoxo
GURBIN IDO____Huguma
*ZAKI YARDA AYI TAFIYAR NAN BABU KE MADAM?*
*_GARZAYA KI BIYA NAKI KUDIN KAN FARASHI KAMAR HAKA_*
Biyar:::1k
Hudu:::700
Uku::::500
Biyu::::400
Daya:::300
*_zaki saka kudin ta wannan account number din_*
HAFSAT UMAR KABIR
2270637070
Zenith bank
*Saiku tura shaidar biya zuwa ga*
07040727902
*IDAN KUMA KATIN WAYA NE ZAKU TURA TA NAN TARE DA SHAIDAR BIYAR*
09134848107
*_THANKS FOR CONTINUES PATRONAGE_*🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰
[17/10, 3:16 pm] +234 706 255 0401: *_GURBIN IDO_*
*LAST FREE PAGE 05*
*AREWA BOOKS::HUGUMA*
Cikin kwanakin da suka biyo baya gaba daya kusan rabi da rabi na dawowar maimuntu daga kiwon ibrahim ne,wasu lokutan yakanyi gaba wani lokaci kuma tana biye dashi a baya,har sukai gida,ya tayata daure na daurewa ko sharar wajen idan bata samu tayi ba,sudan taba hira sannan ya wuce zuwa gida. Duk da cewa fiye da rabin hirar shi kadai yake abarsa,na maimunatun baya wuce eh ko a’ah. Haka kawai fa tsinci kanta da jin dadin tarayyarsu ita dashi,sai takejin wani canji na zuwa ma zuciya da rayuwarta,gaba daya wannan kadaicin babu shi,tana jin kamar ta samu wani bango da zata raba ko ta jingina dashi ko yaya yake,sabanin daa da bata da wanda zai magana da ita,magana da ake kirame dadi,idan taji magana daga bakin wani to fada ne,idan taji hira akanta to ta tsangwama ce,wani lokaci takan jima kwance duk sanda taje bacci,tana tuno irin hirarrkinsu da ibrahim,wani abun takan saki murmushi ne ta kuma juya ta gyara kwanciyarta.
Ta bangaren ibrahim din wani matsayi na musamman yakeji maimunatu na sake damu cikin ruhi da zuciyarsa,a dan zamansu ya fahimci abubuwa masu tarin yawa tattare da ita,ta banbanta qwarai da duka yaran rugar tasu,tana da wata irin nutsuwa da fasahar magana wadda ya jima baiga irinta jikin wata ‘ya mace ba,komai nata na hankali ne da sanin ya kamata,yakan zauna yana kallon yadd take iya controlling dabbobinta da baki kawai ta hanyar basu umarni,lokaci dai daiku ne takanyi amfani da sandarta wanda xaiyi wuya ma kaga hakan.
Yadda take tausayin dabbobin kamar ‘yan adam,bayan dukka alamu sun nuna sun fita samun gata da kulawa,duk da har yanzu bata taba bude baki tayi masa wata magana data shafi gidansu ba,yadda take communicating dasu kawai abun burgewa ne,duk da shima cikakken bafullace ne amma ba kasafai yake ganin hakan ba,lokuta da dama idan ya tsokanetan saidai tayi murmushi kawai,wanda kusan wannan din dabi’arta ne.
Ko sau daya himu baiyi nufin zuwa ga gaje ba kamar yadda daada ta buqata,wani lokaci ma sai ya rako maimunatu yake tunawa da batun,saidai yana ganin ba abu bane mai yiwuwa,yana da tabbacin komai zai daidaita da zarar bappansa ya dawo,wanda ya qara kwanaki kan wadanda yace zai dawo,saboda jiran haduwar kudadensa dake hannun mutane.
**************Yammacine lis,wanda yake busa wata ni’imtacciyar iska me dadi,yanayi ne da ya yiwa halittu da dama dadi,bawai ga dan adam kawai ba,hatta da sauran tsirrai da kuma dabbobin daketa kai kawo suna kiwo a farfajiyar wajen da ya zame musu wajen yini.
Daga can qasan bishiyar idan kakai kallonka wajen,bafullatana maimunatu ce cikin baqin saqinta,zaune saman koren hiramin da himu ya shimfida mata,shi kuma yana zaune daga gefanta saman wani dan mulmulallen dutse da bai cika girma ba.
Murmushine ke fita daga saman fuskarta,murmushin da kana kallonsa kasan kunyace cike dashi,ko a iya zamanta idan ka.kalla da kyau kasan a takure take,hannayenta sarqafe cikin juna tana kallonsu,yayin da shi kuma ibrahim ya zuba mata dukka idanunsa yana jiran amsar tambayar daya jefa mata.
Wani irin nauyi ibrahim din ke aza mata duk lokacin da ya zaunar da ita irin haka yana karanta mata kalaman soyayya……daga qarshe kuma a yau din ya tirketa kan lallai sai ta furta masa da bakinta tana sonshi,saboda bai taba jin hakan daga bakinta ba.
Wani abune kuma ita din da bata jin zata iya gaya masan,kalma ce data ji ta girmi kanta matuqa,koda baya kallonta ba zata iya fada ba,bare yadda yake zaune yana kallonta.
,sirara kuma jajayen labbanta ta motsa a hankali
“midelli…yamma tayi” dauke idanunsa yayi daga kanta yana murmushi,duk da yasan yau din sun gota lokacin komawarsun,amma tayi hakanne don ta kaucewa tambayarsa,yana mamakin kunya irin tata kawaici da kuma kamewa,sai ya miqe kawai ya dauki sandarta da a yanzun shike amfani da ita idan zasu koma gida.
Kamar ko yaushe ya tayata suka kammala komai,yayi tsaye daga jikin wata rusashiyar bukka dake daura da wajen yana dubanta cikin murmushi
“Shikenan,tunda ba zaki bani amsa ba maimunatu zan tafi,sai jaaango?” A kunyace tayi murmushi tana kauda kanta gefe daya,ya sauke qafarsa da ya harde waje daya ya fara takawa a hankali yana barin wajen
“Ka gaida gida” ta fada cikin siririyar muryarta da ba kasafai ya fiya jinta ba,sai daya waiwayo cikin jin dadi ya kalleta yana jinjina kai sannan yaci gaba da takawa,hakanan taji kunya ta kamata,abinda yasa ta juya da sauri da nufin shigewa zuwa shiyyar da dakunansu suke. Saidai kuma cak ta tsaya,saboda ganin inna tsaye daura da ita,da alama taji komai ta kuma ga komai.
Kallon da innar kawai ta tsareta dashi ya sanyaya mata gwiwa ya kuma sanya mata fargaba me tarin yawa,gabanta ya fara faduwa da wani mugun qarfi,duk da haka ta ari dakiya taci gaba da nufar inda innar ke tsaye tana ci gaba da kallonta
“Immoi’onni?(waye wancan?)”innar ta fada a tsawace cike da tuhuma da kuma zargi,yanayin yadda tayi mata maganar ya jefa tsoro a zuciyar maimunatun,ta qanqame jikinta waje guda,tana jiran jin saukae duka daga wajen innar,don wannan din ba sabon abu bane a wajenta
“Tambayarki nakeyi waye wancan din?”
“Sunansa ibrahim…..ya tayani qaraso da dabbobi gida ne”
“Meye hadinki dashi?” Inna ta sake tsareta da tambaya,saboda zargin da ya shiga ranta,taso taha fuskarsa amma kuma haqarta bata cimma ruwa ba,saidai batajin wanda take tunani dinne,don bata da shakka akan alqawari da yarjejeniyar dake tsakaninsu
“Babu komai” ta amsawa innar kanta a qasa,tana matse hannayenta waje guda,tana jin yadda zuciyarta ke ci gaba da bugawa fat fat
“Yauwa…..gwara ki rufawa kanki asiri,ke ta buɗeri ce,shi daya zai iya rufa miki asiri ya aureki,don haka kada ma ki batawa kanki lokaci ki yaudari kanki kice zaki saurari wani,kaf fadin karkarar nan bana jin akwai wanda zai iya daukarki idan bashi ba,koda an samu to yayi miki qarya,saboda haka ki kiyaye” daga haka tayi gaba zuwa garken dabbobin,tabi tana dubasu daya bayan daya tana kuma irgasu kamar yadda ta saba duk sanda maimunatun ta dawo,kai zaka zaci tana duba kaya data bawa qasurgumin barawo ajiya ne.
“Wuwuɗandu(ki share wajen)” ta bata umarni tana fita daga garken tayi gaba abinta,duk yadda takai ga gajiya hakanan dole babu yadda zatayi haka ta laluba kayan sharar ta fara gyaran wajen,duk da cewa a dazun kafin su tafi ta gyara wajen,batasan me ya bata wajen hakan ba,duk da tasan ko ba yaro idan innar taso bata wahala,zata qirqiro mata aikin ko kuma wanda yayi kama dashi,duk dai don kada ta huta,bata qaunar ganinta a zaune ko da na minti daya ne.
°°°°°°°°°°°°°°
A nutse yayi sallama cikin rumfar innar yana yafe da koren hiraminsa,dawowarsa kenan daga sallah sadam yace masa innar tana kiransa.
Abinda ya bashi mamaki shine ganinta da yayi a tsaye tana kai kawo daga wancan bangon zuwa wannan,idanunta dake cike da fushi ta daga ta dubeshi,ba tare data amsa sallamarsa ba kai tsaye tace dashi
“Joɗa(zauna)” kasa zaman yayi,sai ya duqa daga gefe kawai yana kallonta,ta tako gabansa a hankali tana dubansa
“Inaso naji bayan ni wace mahaifiyar kake da ita?” Sosai tambayar ta bashi mamaki,har ya tada kai yana dubanta sosai kafin ya kauda kansa ganin itama shi take kallo,yaro ne shi mai tsananin biyaya,don haka bazai iya hada idanu da daadan ba
“Babu daada….amma wani abune ya faru?” Sake baci ranta yayi
“Ni kake tambaya wani abune ya faru himu?,ashe ni ba uwarka bace?,ashe ban isa na gaya maka magana kaji ba?,tun a waccar ranar ban rabaka da maimunatu ba?,ban gaya maka babu kai babu ita ba?,shine kasa qafarka kayi wancankali da maganata akan diya mace saboda bani da wani muhimmanci a wajenka?”
“Ba haka bane inna…”
“To yaya ne?” Shuru ya gifta wanda bai gaza qasa da second hudu ba
“…….ko kuwa maganar yuuma ce ta shiga kunnenka fiye da tawa ni mahaifiyarka?” Girgiza kansa yayi da sauri
“Ko kadan…..kada ki saka sunan yuuma don Allah daada,ba ruwanta,batasan me akeyi ba tun wancan ranar data fita a dakinki”
“Ibrahim!” Ta kirayi cikakken sunansa,abunda ya sake tabbatar masa zata yanke tsatstsauran hukunci ne,kuma kowanne irin hukunci ne hakan zata fadeshi ne ba da wasa ba
“Daga yau…..idan ka sake ka sake zuwa inda maimunatu take Allah ya isa ban yafe maka ba,sannan koda bayan raina ka sake ka aureta ban yafe maka ba” qarasa zama dirshan yayi a qasa maimakon tsugunon da yayi,ba qaramin kaduwa da hukuncin nata yayi ba
“Innalillahi wa inna ilaihi raji’un” ya dinga maimaitawa kansa a qasa,bai taba zato ko tsammanin hukuncin innar zaiyi tsaurin haka ba
“Don Allah inna ki sassauta kiyi haquri,maimunatu bata taba yi miki komai ba,banda…….” Tsawa ta dakeshi tana katseshi
“Banason na sake jin komai daga gareka,wannan shine hukuncina na qarshe,tashi ka fita!” Ta fada a zafafe tana nuna masa qofa,sai da ya dafa qasa sannan ya miqe
“Himu” ta kirashi sanda yakai qofa
“Na baka kwana hudu kacal,ka shirya fara zuwa wajen gaje kamar yadda na gaya maka,umarnine nake baka” bayajin xai iya cewa da ita komai,don haka kansa da yayi masa nauyi kamar ya dauki kaya ya gyada mata sannan ya fice daga dakin yana jin jikinsa kamar zazzabi na shirin rufeshi.
**********Sake juya rufaffen takalmin danqon hannunta tayi don ta tabbatar dabarar data yi masa zata kaita gida,ita kanta batasan adadin liqin data yi masa ba,wani gurin da garwashin wuta da leda,wani gurin kuma tana samun zaren lilo ta zarge inda yake shirin rabewa dashi.
A hankali ta duqa ta ajjiye takalmin a qasa ta zura qafafunta,tadan motsa qafar ta tabbatar yayi,sai ta sauke ajiyar zuciya,tana godewa Allah da ya sake fiddata a yau dinma dai still,takalmin bai mata tutsu ba,batasan ya zata kasance mata duk randa hakan ta faru,itadai shi daya ta sani a matsayin takalmin da take dashi,wanda ita kanta batasan adadin kwanakin ko shekarunsa ba a duniya bare ta iya tantancewa.
Sake waiwayawa tayi hagunta da damanta,har yanzu bata debe tsammani da ganin himu ya bullo ba,duk da cewa lokacin zuwan nashi ya gota sosai,tana da tabbacin babban abune ya tsaidashi,saidai tana fatan koma meye ya kasance yana lafiya qalau.
Waiwaya tayi sashen wata saniya ke zaune,gefanta jaririn san data haifa ne a dazu jimawa kadan bayan isowarsu wajen,ta tabbatar inna batasan cikin ya isa haihuwa ba,da ba zata bar mata ita zuwa wajen kiwo ba,dole idan lokaci yayi himun baizo ba,haka zata hada da kula da sauran dabbobin,da ita wannan sabuwar haihuwar su wuce gida,yau din tana jin gajiya sosai a jikinta,ita kadai cikin wajen,cikin tsoro da fargaba saniyar tahaihu a wajenta,wanda ita kanta tasan babbar kasada tayi,saboda samuwar matsala ta mutuwar uwar ko abinda aka haifa,dai dai yake da samuwar matsala cikin tata rayuwar,ko daya innar batasan wata aba wai ita asara ba bare haquri da ita idan ta sameta,haka ta dinga kai kawo har haihuwar ta kammala.
Saman dan dutsen da himun ke zama ko yaushe idan yazo ta koma ta zauna,idanunta nakan abun hannunta na shirin duwatsu green da jaa,tasa yatsanta guda daya tana wasa dasu,ta warasu wani lokacin ta hadesu,tana tuna lokacin da innarta ta zura mata su,har yanzu lokacin yaqi bacewa cikin idanunta.
Ta jima zaune a nan,tana jin wata kewa da kadaici suna shigarta,lokaci lokaci tana daga kai ta dubi yanayin yadda dabbobin ke kai kawo sannan ta sake maida kanta.
Karo na qarshe data daga kanta ta tabbatar lokaci yayi da ya dace su koma gida,ta sauka daga kan dutsen a hankali,ta gyara zaman hularta sannan ta dauki sandanta ta fara ratsawa ta tsakaninsu tana hada kansu.
A gaba take sanyasu mafi yawancin lokuta,idan taga zasu canza hanya ko zasuyi wani abu ba dai dai ba takan tsawatar musu,suna ji kuma suna fahimta yawancin lokuta,yau dinma haka ne,hannunta na dauke da sabuwar haihuwar da daya daga cikin shanun tayi.
A hankali baqaqen lafiyayyun motocin guda biyu ke kutsowa cikin rugar,tana haura duk wani tudu da kwari da kuma kwazazzabo dake kan hanyar ba tare da mutanen dake ciki sunji komai wata jijjiga ko wahala ba da ire iren wadan nan hanyoyin ke dashi a duk sanda mota zata ratsasu ba,hakan ya faru ne sanadiyyar kyau da lafiyar motar,wanda hakan yake da nasaba da irin tsadar da kowacce mota guda daya ke da ita.
Motar farko mutum hudu ne a ciki,driver salmanu,sai wani zaune a gefansa hayatu,daga seat din baya kuwa dattijuwar macace,hakimce cikin shiga ta alfarma,kyakkyawar lallausar blueblack din atamfa ce wadda tayi matuqar haska farar fatarta,duk da akwai tsufa tattare da ita,amma yanayin da take ciki na hutu da kuma jin dadi ya hana bayyanuwar tarin shakarunta,daga shekara sittin da takwas,ya maidata zuwa ‘yar shekara hamsin,idan ka cika qwaqwafi kuma ka qara mata da uku,hankalinta na ga window din motar,tana duban hanyoyin da suke wucewa,wanda sukanyi gamo da mutane jifa jifa,duk mutumin da suka gifta sai ya bisu da kallo,saboda abune baqo a wajensu,zasu iya irga sau nawa suka samu labari ko sukaga shigowar mota rugar tasu,wasu sukan cika da fargabar su waye suka shigo musu?,wasu kuma kyau da motar ke dashi ne yake daukar hankalinsu har sai tayi nisa ta bacewa ganinsu.
Daga gefan dattijuwar kuwa kyakkyawar matashiyar budurwa ce wadda duka duka ba zata haura shekara ashirin ba a duniya,shigarta kadai zai gaya maka cewa ta fito daga gidan ilimi wayewa da kuma wadata,kacokam ta tattara hankalinta ga wani littafi dake da shafuka masu dan dama,da alama nazari takeyi.
“Salmanu……..saukemin gilashin nan…..naga alama wannan baqin abun da kuka lafta masa bazai bar idanuwa suyi kallo yadda ya kamata ba” ta fadi tana hade gira.
Karaf matashiyar ta daga kanta daga kan littafin
“Haba anni….me kuma za’a sauke miki kiji?,an kunna ac ne fa,ta yaya za’a sauke glass,kuma ta hakan ma ai ana ganin komai,tunda ba dare bane” harara ta juyo ta watsa mata
“Ke….kiyi ta kanki,ni ba dake nake ba,toke da wanne mataccen idon ma kike iya gani daga nan din?,idon da komai za’ayi saida gilashi?,salmau zaka saukemin ko kuwa?”
“Za’a sauke anni” yayi maganar yana sauke mata da hanzari kamar yadda ta buqata.
Sai da aka sauke mata gilasan tas sannan ta sake matsawa jikin window din tana fara’a
“Yawwa,yanzu naji batu,amma daa an qunshe mu kamar ‘yan kidnapping,ni ba baqin hali gareni ba da kullum xan fita zance a rufeni cikin gilasai” sarai matashiyar ta fahimci da ita take,kuma idan da sabo ta saba ko kuma tace sun saba da halin anni,duk wanda ke zaune da itama ya riga da yasan halinta sarai,don haka sai ta maida mayafin da yake kafadarta zuwa saman kanta,ta kuma rufe littafin saboda hasken ya mata yawa,karatun bazai mata dadi ba ta maida jakarta,ta ciro wayarta a maimakon littafin ta soma qoqarin kunna data,saidai yanayin rashin network mai kyau ya hana wayar tata amfani,dole ta maidata itama jakar.
“Ma sha Allah,kai ma sha Allah,lallai na jima rabona da adamawa,wai” anni keta fadi,fuskarta na nuna alamun jin dadin tafiyar sosai.
A dan rude maimunatu ta maida hankalinta ga marabar hanyar da shanunta ke tsallakawa saboda jin wani sauti,hango motocin suna tahowa yayi matuqar daga mata hankali,na farko yadda zata tsaida dabbobin da sukayi nisa da tsallakawa ta bawa motocin dama su wuce,na biyu kuma motocin sunyi matuqar sanya mata fargaba da tsoro kamar yadda suka sanyawa mutanen da suka baro a baya,su waye a ciki?,me sukazo yi cikin rugar tasu?,wadanne irin motocine wadan nan da sam bata taba ganin koda me shigen kamarsu ba?.
Yadda suke sake kusanto inda suke ya sanyata yunqurawa da hanzarinta ta fara bawa dabbobin nata umarni da dukka salon da tasan suna iya karbar umarni da hani daga gareta,tanayi tana kutsawa ta cikinsu tare da dan daga muryarta.
“Kai salmanu……dakata” anni ta fada da sauri,idanuwanta suna sauka akan maimunatu,sosai ta zuba mata idanu cike da mamakin yadda take iya bawa dabbobin umarni da baki take kuma iya sarrafasu ba tare da takai duka ma ko daya daga cikinsu ba,idanun anni ya sauka ga dan qaramin dabbar dake hannunta,fari qal dashi sabuwar haihuwa,abinda yaja hankalinta kenan zuwa ga garken dabbobin,ta dinga binsu da kallo daya bayan daya
“Ma sha Allah,wadan nan dabbobin gaskiya na qwarai ne,sun samu kiwo da kulawar data kamata”
“Abinda nake fada a raina kenam hajiya yanxu hajiya,babban abun mamakin yadda qaramar yarinya kamar wannan take iya kula dasu gaba dayansu” cewar hayatu shima idanunsa akan maimunatu
“Bari hayatu,kaga inda ake mata,ba irin ‘ya’yanmu ba cima zaune da komai suna zaune ake musu” anni tayi maganar tana tabe baki.
Dariya ce taso qwacewa matashiyar amma ta danneta,sai murmushi da ya fita a fuskarta,yayin da hayatu da kuma salmanu suka dan dara kadan,saboda sunsan da wadda take,a tsakaninsu suka dinga tattaunawa,har zuwa sanda maimunatu ta ratsa ta gaban motocin suka wuce da dukka dabbobin,tana dan duba da kuma waiwayen motar tana mamakin yadda suka dakata mata suka bata dama ta wuce.
Ajiyar zuciya ta sauke me qarfi bayan data tabbatar sun tsallake lafiya,abinda ya taba faruwa da ita shekarun baya bai sake maimaita kansa ba,wanda ita daya tasan bala’i da masifar daga fuskanta a sannan,har yanzu tana iya tuna sanda motar ta taho a guje,bata kuma damu data tsaya ba ganin dabbobi suna qetarawa,tana hango sanda motar ta banke dan dalonta da take matuqar ji dashi,ya zube a qasa jini na fita ta hanci da bakinsa,ta bishi da gudu ta tsugunna a gabansa tana kuma saboda ta tabbatar bazai tashi ba,taji mugun cin birkin da motar tayi,da fadan da wata murya ke mata tsaye a saman kanta,fadan da yafi kama da a dakeka a hanaka kuka saboda cikin xafi da fadar maganganu marasa dadi ake yinsa,abinda ya sanyata daga kanta ta dubi.mai maganar.
Kalmomin da zata gaya masa masu zafi take nema amma ta rasa,saboda ita din ba gwanar rashin kunya bace,bata ma iyata ba sam,to dawa zatayi bayan dabbobin sune qawayenta?,abu na qarshe da take ganin xata iya shine watsa masa harara gami da tsaki mai nauyi,kafin ta sauke kuwa aka sauke mata wani zazzafan mari da ya sanya wuta ta dauke mata gaba daya,ta daina gane komai,bata tashi dawowa hayyacinta ba sai bayan wani lokaci.
Ko a yanzun data tuna sai data runtse idaunta,tana tuna zafin marin saman fuskarta,abinda ya biyo baya kuwa ta gefan inna azaba ce ta cita mai yawa,bata damu da yadda fuskarta ta tasa ba saboda marin data samu akan abinda ita ke da gaskiya,ta tattara laifin gaba daya a kanta,tare d adora alhakin mutuwar dan maraqin saniyar a wuyanta.
Ajiyar zuciya ta sauke sanda suka iso gida,kamar kowanne lokaci ta daga murya ta sanarwa innar ta dawo,bata ajjiye dan jaririn a hannunta ba sai data qaraso ta miqa mata shi,bakinta har kunne,kai kace jika aka haifa mata na dan mutum
“Dama kinsan ta kusa sauka amma baki garzayo kin kirani ba?” Innar ta fadi haka cikin tuhuma,bata amsa mata da komai ba,itadai tana duqe tana daure wasu akuyoyi,banda abu irin na dan adam,ta samu uwa da dan lafiya,bata damu da yi mata sannu na wahalar datayi da naggen ba har ta sauka lafiya,ta buge fa tuhumarta,wanda tayi imani cewa inda ta barta a can ta taho kiranta wani abu mummuna ya faru,lallai ba zata daga mata qafa ba.
Tunda taji maimunatun tayi shuru tasan ba zata tanka mata ba,ita kanta ta santa da wannan halin,a wasu lokutan idan tayi mata irin hakan,yaxo akan gabar da take cikin fushi ko takejin haushinta,kamata take ta nada yadda ranta yayi mata suga.
*Daga yau free pages sun qare,paid pages zasu biyo baya in sha Allah,hanzarta biyan naki kudin koki bibiyemu ta shafukanmu dake arewabooks*
❤🔥❤🔥❤🔥❤🔥❤🔥❤🔥❤🔥❤🔥❤🔥❤🔥❤🔥❤🔥
*_ZAFAFA BIYAR din samari ne a rayuwar INAYAH,kowanne a cikinsu akwai wani murdadden Al’amari da ya shata layi tsakaninsa da ita,wawakeken sirri wanda a koda yaushe take kiransa da SANADIN LABARINA_*
*_Amma babban abun mamakin a koda yaushe shine,ita dai tasan cewa BABU SO tsakaninsu MEYA KAWO SHI?_*
*_Duk da haka tana tunanin yun qundun bala ta fitar da FARHATUL K’ALB a cikin ZAFAFA BIYAR din samarinta,duk da batason su zame mata GURBIN IDO wanda har kullum ba ido bane_*
😄😄😄😄😄😄😄
*YA KUKAJI SALON MASU KARATU?*
*YADDA SALON YA BAMBANTA DAKO YAUSHE HAKA LABARAN SUKA BAMBANTA DA DUKKA LABARANMU NA BAYA*
INAYA(riba biyu)___mamughee
SANADIN LABARINA___Rano
BABU SO___Billynabdul
FARHATUL K’ALB___Miss xoxo
GURBIN IDO____Huguma
*ZAKI YARDA AYI TAFIYAR NAN BABU KE MADAM?*
*_GARZAYA KI BIYA NAKI KUDIN KAN FARASHI KAMAR HAKA_*
Biyar:::1k
Hudu:::700
Uku::::500
Biyu::::400
Daya:::300
*_zaki saka kudin ta wannan account number din_*
HAFSAT UMAR KABIR
2270637070
Zenith bank
*Saiku tura shaidar biya zuwa ga*
07040727902
*IDAN KUMA KATIN WAYA NE ZAKU TURA TA NAN TARE DA SHAIDAR BIYAR*
09134848107
*_THANKS FOR CONTINUES PATRONAGE_*🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰
[17/10, 3:16 pm] +234 706 255 0401: *_GURBIN IDO_*
*Arewabooks::HUGUMA*
Free page 04
Sallamarsa ta yanke mata dan qaramin bacci mai dadi data fara yi,ta daga kanta tana amsa masa,da murmushi ya bita,hannunsa dauke da baqar leda qananu guda biyu,inda ya tashi dazun ya koma ya zauna,sannan ya bude ledan yana cewa
“Ga magani kisha” idanunta ta lumshe gami da budesu lokaci guda cike da.mamaki,yau ita ake cewa ga magani?,anya kuwa ita dince……maimunatu?,bata sauka daga wannan mamakin ba ta sake jin muryarsa yana sake miko mata wata ledar
“Amma ki fara cin wani abun tukunna,na sani idan baku da lafiya bason cin abinci kuke ba,haka innata ke fama dasu zubaida idan basu da lafiya” ya qarashe maganar yana miqewa
“Bari na baki waje,amma idan bakisha maganin ba zan dawo” saiya juya yayi nesa da ita,yayin da ta rakashi da kallo har sai data daina hangoshi,sannan ta janye manyan idanunta ta mayar kan ledojin,ta sanya hannu ta jawosu tana budewa.
Ledar farko magunguna ne,qwayoyi tablet sosai,sai leda fa biyu dake dauke da gurasa mai kyau,wani yawu ta hadiya,duk da yanayi na lalurar rashin lafiya da take amma sai da tsohuwar yunwa ta taso mata,batayi qasa a gwiwa ba ta dauka ta fara ci,tana ci tana lumshe idanunta tsananin azabar yunwar data tarawa cikinta,dama don bata da lafiya ne,amma duk sanda inna ta gwada mata irin wannan rashin imanin……a nan gurin kiwo take samun daya daga cikin naggen ta tatsi nono mai dumi tasha,duk da ta sani,yawanci da safe shine lokacin tatsar,amma dole tasa wasu lokutan take hakan,idan kuma ta samu ta faki idon innar sanda take tatsar da sassafen ta ɗaɗɗaki wani,shine zata wuni nata damu ba,yunwa kuma bata addabeta ba kamar yanzun,har shan nonon ya zame mata jiki,ya koma kamar shine abincin nata,abinda yasa ko kadan bata da wani jiki kwata kwata,duk sirantaka irin ta bafullace tata ramar ta fita daban.
Bawai don ta qoshi ba ta janye hannunta,a’a,tayi hakanne saboda kunya kara da alkunya,kada yazo ya taras ta tashi da ita,ta bude ledar maganin wanda ya sanya ledar ruwan pure water guda daya,ta daga pure water din ta jujjuya shi a hannunta,ba zata iya tuna sanda tasha ruwan leda ba a rayuwarta,saita koma kan magungunan,ta balli kowanne kamar yadda taga anja sandunan layi ajiki ta kora da ruwan.
Idanunta ta mayar tana sake lumshesu,tana jin yadda numfashinta yadan fara daidaita albarkacin gurasar data ci tun kafin magani ya soma mata aiki,a hankali take zuqan iskan wajen tana kuma sauraren koke koken dabbobi dake kai kaw a wajen,jikinta yana mutuwa murus kamar wadda aka yiwa dukan tsiya.
Tun daga nesa ya kafeta da ido,idanunta dake lumshe sai suka sake qarawa fuskarta kyau,yana ganin baqonnin yanayi tattare da ita,yana son sanin wace ita sani na haqiqa,da kuma dalilin da yasa take kebance kanta take nesa da jama’a haka.
Sallamarsa ta sanyata bude idanunta
“A henyi?(Kin gama?)” Kai ta gyada masa tana kallon qasa,kunya tana cikata,tanajin yadda tayi abun kunya,na yadda zata zauna taci abinda ya futo daga hannun saurayi
“hokkoyon dunni sauro(miko min sandar can)” ya fada yana nuna sandarta dae gefe,sai data kalli sandar sannan ta maida dubanta kanshi,ya fahimci me take nufi,don haka murmushi kawai ya sakar mata,ya taka da kansa zuwa gefanta ya dauki sandar,ga bishi da kallo mamaki fal zuciyarta
“waye shi?” Tambayar da taketa nanatawa kanta kenan.
Daga nan inda take tana iya hangen yadda yake tattare mata kan dabbobin nata cike da hikima da kuma qwarewa wadda ta lunka tata,da alamu shima din gwanine wajen iya kiwo,bai dauki wasu lokuta masu dama ba ya dawo gareta,yana sabe da sandar kan kafadarsa
“indillo(Muje ko?)” Yace da ita,dubansa tayi sanna ta janye idanunta gefe daya,sam maganar batayi mata ba,ta yaya zata jera dashi har cikin gari?,akwai idanun mutane masu yawa a kanta,sannan tana da kunyar da ba zata iya aikata hakan ba
“ummadillen(Tashi mu tafi),ko ba zaki iya tashi ba?”ya sake maimaitawa a tausashe,a hankali ta girgiza masa kai
“Kaje kawai,na gode,zan qarasa kaisu gida da kaina,na gode qwarai” idanu yadan zuba mata kadan,sai ya sauke ajiyar zuciya yana sauke sandar daga kafadarsa,ya fahimci me take nufi,tabbas ga cika bafulatanar gaske.
“Shikenan,zan kora miki su,tumudilli tokkirawaya gaɗa taajan banna wala kyettaiɗo ingwandi(idan na tafi ki biyo bayana,karki damu,ba wanda zai gane tare muke)” duk da hakan yayi mata,amma kuma batason dora masa wani nauyin kuma ko dawainiyarta,saidai kafin ta sake cewa komai yayi gaba,dole ta miqe,ta dauki malfajenta ta mayar saman kanta,ta dauki jakarta ta daura tabi bayansa.
Bata sani ba ko shima ya kula,sharewa kawai yayi,ko kuma bai kula din ba…..da gaske ita daya ta lura,yadda mutane keta binsa da kallo a sanda aka ganshi yana kora shanun da ita ke da hakkin kula dasu,yayin da ita kums ke biye dasu a baya,kasan samun nutsuwa tayi kwata kwata,jinta take a daure,har sai da suka isa gida,ya miqa mata sandanta idanuwansa akanta,fuskarsa dauke da murmushi
“Sai jaaango?” Ya fada yana sake nazartar kyakkyawan fuskarta
“Miyatti” ta amsa masa a gajarce,sai ya jinjina kansa
“Alla ɗaudane jamu(Allah ya qara lafiya)kisha magungunanki da kyau”
“to Allah jaɓe” ta fada tana jin nauyin mixanin kyautatawarsa a gareta.
Ko sanda himu yake nufar gida tunaninta ne fal cikin ransa,kamar yadda murmushi yaqi barin fuska da bakinsa su huta,sosai yake ji cewa yayi gamo da Matar aure,ta kuma zo dai dai lokacin da ya kamata ace tazo din,bayajin zaiyi nauyin baki ko jinkirin shaidawa innarsa,duk da cewa babansu baya nan,amma dai yana da kyau innar ta sani,ta kuma shaidawa baban da zarar ya dawo.
Da sallama ya shiga faffadan tsakar gidan nasu,kishiyar mahaifiyarsu wadda asalin sunanta shine rahama….amma sauran dangi da ‘yan rigarsu na kiranta da ramatu,su kuma yaran gidan suna kiranta da yuuma,tana duqe gaban murhu,ta kammala kwashe tuwon dare tana wanke muciyar cikin tukunyar tuwon himu ya shigo.
Fuskarta dauke da fara’a take amsa sallamar tasa,macace mai matuqar kirki haquri hagen nesa da kuma sanin ya kamata,duk da kasancewarta wadda Allah bai azurtata da haihuwar yaro ko daya ba,amma sam bata kasance mai baqin hali gabyaran mikin nata ba,mutum ce mai sauqin kai,wadda take kallonsu ibrahim tamkar ita ta haifesu,tana kulawa da kowanne daya daga cikinsu,duk da zamantowar safara’u mahaifiyar ibrahim mace mara haquri da biyema zuciyarta a wadansu lokuta,amma yuuma ta danne,suna zaman lafiyar daya sanya jama’a da dama cikin karkarar ke sha’awar zaman nasu,ba tare da sunsan cewa fiye da kashi tamanin cikin dari na zaman nasu haqurin yuuma ne ya qawatashi.
Barka da gida yayi mata ta amsa tana masa sannu da zuwa
“Inna walaɗon(inna bata nan ne?)”
“o’o immoder,one ɓayi e’ummakiɗo(A’ah tana ciki,don bata jima da tashi daga nan ba),kila barci ne ya saceta,don tacemin bata danjin dadin jikinta sosai” kai ya gyada sannan ya sake tambaya
“Yaran nan fa?,su safiya?”
“inna’onliliɓe,amma ɓeɓadake wartuki(Innar ce ta aikesu,amma suna gab da dawowa)” har ya taka zaiyi gaba sai ya sake tambayarta
“Yaushe baaba yace zai dawo ne?” Murmushi ta sake
“Yau kuma ‘yan tambayar ne a kusa himu?,rana wata yau in sha Allah” kai ya gyada yana murmushi,yaji dadin jin cewa bazai jima ba zai dawo gidan,ya tafi ikko ne da wasu shanunsa zai saidasu,wanda dama.yawanci can yake kaisu,shi kansa ibarahim din yafi zama a can,mafi yawan rayuwarsa ta can ce wajen wani dan uwan baaban nasa,yanzu ma gajiya yayi da zaman can din ya dawo gida yadan huta sannan ya koma,uwa uba kuma sun samu hutun semester,don acan din bai zauna ba yana karatunsa.
Ya daga labulen dakin ya samu barcinne kuwa ya dauketa,sai ya sauke ya wuce dakinsa,yayi abinda zaiyi a ciki sannan ya fito ya fara daura alwalar magriba,bai kammala ba innar ta fito tana daura dankwalinta
“denattoi ɗa himu(yaushe ka shigo himu?)” Ta fada tana dubansa,ita din duk da bafullatsna ce amma sam ba ruwanta da wannan kunyar da kaara tadan fari
“Ban jima ba,na leqo na samu kina bacci,ya jikin naki?”
“Alhamdlh,nasha ragowar maganin nan daka taba kawomin kwanaki kafin na kwanta,kaga kuwa har ya fara sakina”
“To alhmdlh,hammiyami jula miwarta(bari nayi sallah na dawo)” ya fada yana warware hannun rigarsa,a bakin kofar shigowa gidan sukayi kacibus da qannensa,yammata masu tasowa su biyu,yace maza su shige gida an fara kiran sallah,suka amsa masa amma suna binsa da.kallo,saboda labarin da suka samu a kansa tun a hanyarsu ta isowa gida.
Bayan sallar isha’i ya shigo gidan,babu kowa tsakar gidan sai yuuma dake zaune daga bakin kofar dakinta ita daya,gabanta fitilar aci balbal ce,sai qaramar redio da bata rabo da ita saboda jin labarai,sannu da gida yayi mata,ta amsa masa tare da shaida masa abincinsa na wajen innarsa,ya amsa mata yana wucewa kai tsaye zuwa dakin innar,bayajin dadin yadda wasu lokuta safiya da zubaida ke barin yuuma ita kadai,duk da lokaci lokaci zaka samesu wajenta,yana matuqar jin tausayinta,saboda rashin haihuwa abune mai ciwo da kuma sanya mutum cikin kewa da kadaici.
Da sallama ya shiga dakin,ya taras dasu sunata hira abinsu dukkansu,safiya zubida da sadam qaramin qaninsu,sannu da xuwa sukayi masa,ya samu waje yana zama
“Ra nyam kima,hokkumoki sadam(ga abincinka,sadam mika masa)” inna ta fada,sai sadam din ya mika masa,yaja kwanon ya bude ya fara ci bayan yayi bismillah,ba qaramin son tuwon yuuma yake ba,bama shi kadai ba,hatta da jama’ar gidan,saboda yadda ta iya girki,duk da innar tasa ma ba baya bace.
A hankali yake cin abincin yana kuma jefa baki a hirar tasu,saidai fiye da rabin hankalinsa nakan ta yadda zai gayawa inna maganar dake bakinsa,a qa’ida da yuuma zaiyi zancan,amma ya sani idan yayi hakan ransa ne xai baci wajen innar,saboda batason hakan,tafiso kowace magana suke da ita su sameta kai tsaye su shaida mata,itama yuuman tunda ta fuskanci haka,da sunzo sun gaya mata zata ce
“Kun gayawa innarku?” Idan sukace a’ah,takan ce
“Ku sameta ku fara shaida mata muji abinda xata ce”.
Sai da ya gama cin tuwon tas ya wanke hannu sanna ya gyara xamansa cikin jin nauyi da kunya yace
“iwodi haala kaginmi gaɗen Inna….(akwai maganar da nakeso muyi inna)”
“Shine tun daxu kaketa wani mutsu mutsu ka kasa gayamin?,tawi’aayanka,mojetta bi’owaka(idan baka gayamin ba wa zaka gayawa duk duniya?)” Ta qarashe da sigar tambaya tana kafeshi da idanu,yasan me take nufi,sai kawai yayi murmushi yana cewa
“Babu”
“iminamma(ina saurarenka)” dan jim yayi kadan sannan yace
“Inna…..na samu yarinyar da nakeso fa”.
Zuba masa idanu tayi saboda yadda maganar tazo mata a bazata,bata tsammaci jin maganar ba a wannan lokacin,saboda tuntuni tana da tsari da kuma muradi a kansa,amma duk da haka saita danne wannan a ranta,tace dashi
“Emi namma,immoi ‘onni?(ina jinka,wacece?)” Kansa yadan shafa kadan sannan yace
“Sunanta maimunatu”
“Maimunatu ta gidansu laulo” muryar zubaida ta ratsa hirar tasu,da hanzari inna ta juya tana duban zubaida saboda yadda maganar zubaidan ta dauki hankalinta,yayin da himu shima ya juya yana kallon zubaidan saboda baisan waye laulo din ba,saidai idan ita dince yaji dadin yin maganar da zubaidan tayi,saboda baisan ta yadda zai kwatantawa innar ita ba yadda zata fahimta
“Da gaske ita kake nufi himu?”
“Gidansu na kusa da hanyar fegin maraba” mummunar faduwa gaban inna yayi,tabbas maimainunatun ya hango,take hankalinta yayi mummunan tashi,maimunatu ‘yar uwa ga gaje?,gaje dai ‘yar inna furaira
“Yuuma…..yuuma…..warnano wakka haala kawela(zo kiji wani mummunan labari)” ta fara qwalawa yuuma dake xaune qofar dakinta kiran,abinda ya sanya himu zubawa innar idanu cike da mamakin meye ya gigita innar tasa haka?,har take irin wannan kiran?.
“Ku tashi ku fita” innar ta fada tana waiwayawa gasu safiya dake zaune tun dazu suna kallon kallon a tsakaninsu,tsam suka miqe suna masu ficewa kowacce bakinga fal da magana,dai dai sanda yuuma ta shigo dakin a rude
“Lafiya kuwa?” Ta tambayi inna tana laluben wajen zama hankalinta a tashe,sai da inna taja wani dogon numfashi mai nauyi ta furzar da iska sannan tace
“Yaron nan ne yakeson dauko mana jaraba rana tsaka” sake tashi hankalin yuuma yayi tana duba inna tace
“Subhanallahi,jaraba wacce iri?” Kai inna ta gyada cike da jin xafi tace
“Wai yarinyar nan maimunatu ya gani yakeso?”
“Maimunatu?….maimunatu?” Yuuma ta maimaita sunan tana son tuna aka wace ake magana
“Diyam ta gidansu laulo” take yuuma ta fahimta,sunan kuma ya fado mata a rai,saboda ita daya keda sunan kaf rugar,hakanan kuma mahaifiyarta kadai ke kiranta da sunan,sai ta sauke ajiyar zuciya,alamun tashin hakalin da ya taso tun daga zuciya zuwa fuskarta ya fara zagwanyewa
“Hankalina ya tashi sosai innar sadam,na dauka wani abun tashin hankalinne”
“Yo akwai tashin hankalin da yafi wannan yuuma?””ai abinda yasa nace haka innar laulo…..kaf fadin rugarnan anyi ittifaqi babu yarinyar dake da nutsuwa da kuma kamun kai da tarbiyya irin maimunatu…..”
“Amma kinfi kowa sanin ainihin wacece ita ko?”
“Wannan duk camfi ne ko ince hasashe….duk cikin masu hasashen babu wanda yake da tabbas kan abinda yake fada koda kuwa a gaban Allah ne,dukka abinda al’umar rugar nan keyi ba komai bane illa jahilci zalla da kima gurguwar fahimta gami da mummunan zato,koda ba zato bane hakanne,babu wanda ya taba kama maimunatu da wani mummunan aibu da za’a qita,a karan kanta maimunatu bata da wata matsala ko illa…..” Idanu inna ta zubawa yuuma,a hankali a kuma sanyaye tace
“Yuuma…kodai don bake kika haifi himu ba kike qoqarin wanke maimunatu gami da kore kowanne aibu daga gareta?” Ba yuuma kawai ba,hatta da ibrahim sai da maganar ta tabashi,qas yayi da kanshi yana jin babu dadi a ransa,yayin da yuuma ta rintse idanu,maganar tana sauka saman zuciyarta da wani irin dafi mai zafi,dai dai maganar take da saukar mashi saman zuciyar tata,duk yadda take zaman kawaici da innar laulon….bata taba gwaba mata magana me zafi akan yaranta ba irin wannan
“Kaico!….kaico!” Yuuma ta fada tana girgiza kanta
“Inama ace Allah ya bani d’a na cikina wanda yakai shekarun ibrahim….kai koda ace bai qarasashi ba,matuqar ya isa a daura aurensa,da ba shakka na tabbatar miki da cewa magana nake Miki da zuciya daya…..Allah ya kyauta,kiyi haquri bisa shishshigin da nayi miki” yuuma ta fada bayan ta yunqura ta miqe,zuciyarta na wani irin tafasa,wanda tana fita qofar dakin hawaye ya silalo mata.
Shuru ne ya ratsa dakin na wucin gadi,cikin ranta innar laulo tana jin kamar bata kyauta ba,wata zuciyar kuma na gaya mata daidai ne abinda tayin,zallar mugunta ce kawai tasa yuuman bada wannan shawarar a gaban himun,bayan tasan kowa gudu da qyamar yarinyar yakeyi,ko ita bata sake ganinta tana hulda da yarinyar ba
“Amma inna abinda kika yiwa…..”
“Kaga dakatamin” inna ta tsaida ibrahim dake Shirin nuna mata rashin dacewar abinda tayin
“Kada kace min komai,maganar maimunatu kada na sake jinta a bakinka,domin kuwa ba kai ba,koda wanda na isa na gaya masa yaji ne bazan bari ya aureta ba,bare kai dan cikina,bama maimunatu ba,banason ka sake kawomin maganar kowacce yarinya,na riga na zabar maka matar aure tun shekarun baya…..kaje gidansu maimunatun ka nemi gaje ku dai daita”.
Karin wasu littafai da zaku so
-
Matar maza 3
-
Zuciya ta
-
Mahaukaci ko boyayyen masoyi
-
Wuka a makoshi
-
Aure da haihuwa
-
Husna Hausa Novel
-
Musayar Zuciya
-
Gangar Shedan
-
Angon mata biyu
-
A gidan mu take
-
Bafulatanar Rugga
-
Matar yaro
-
Mr Bello
-
Mijin Buzuwa
-
Gidan Uncle Complete
Powered by: www.mynovels.com.ng
Tsaf kwanyarsa fa birkice,ta yaya zaizo da maganar maimunatu inna ta umarceshi da auren gaje?,gaje dai da ya sani?,ya akayi suka zama ‘yan gida daya ita da maimunatun?,babu kama ta siffa ko dabi’a ko qanqani a tsakaninsu,wanne aibu ne ma wai da innar ke magana a kai da har zai zama hujjar raba sabuwar tarayyar da yanzu aka fara kiwonta tsakaninsa da maimunatu?.
*FREE PAGES ZASU KARE NE ZUWA GOBE IN SHA ALLAH,ZAKI IYA BIYAN KUDINKI TA WADAN NAN HANYOYIN*
Hafsat umar kabir
2270637070
Zenith bank
*Saiki tura shaidar biya ta nan*
07040727902
*Idan katin mtn ne kuma zaki tura ta nan tare sa shaidar biya*
09134848107
*Thanks for choosing zafafa biyar*
Leave a Reply