Hanyoyin Shiga Aljannah Guda 30

Hanyoyin Shiga Aljannah Guda 30

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

Tag: Hanyoyin Shiga Aljannah Guda 30

HANYOYIN SHIGA

ALJANNAH 30

.

Wadannan Hadisai duk

sun tabbata daga

ANNABI S.A.W duk wanda ka dauka

zai kai ka/ki Aljannah:-

.

1. ANNABI S.A.W yace:

“duk wanda yayi

sallolin asuba da la’asar akan lokaci, zai shiga

ALJANNAH”

.

2. Duk wanda ya rike

karanta AYATUL

KURSIYYU bayan ko wacce sallah, babu

abinda zai hanashi

shiga ALJANNAH face

mutuwa”

.

3. Duk wanda yake karanta suratul MULK

kafin ya kwanta

bacci, zata cece shi

zuwa ALJANNAH”

.

4. Duk wanda yayi ALWALA sannan ya

kyautata alwalar,

sannan bayan ya gama

yace:- ASH HADU

ALLA’ILAHA

ILLALLAHU WAHDAHU LA SHARIKALAH, WA

ASH HADU

ANNA MUHAMMADAN

ABDUHU WARASULUH’

za’a bude

masa kofofin ALJANNAH guda

takwas, ya zabi ta

wacce zai

shiga”

.

5. Duk wanda yayi sallolin NAFILA goma

sha biyu a dare da

yini, Allah zai gina

masa gida a ALJANNAH”

.

6. Akwai wata kofa a ALJANNAH mai suna

ARRAIYAN,

babu mai shiga ta

wannan kofa sai masu

yawan AZUMI”

. 7. ANNABI S.A.W yace

yaga wani mutum yana

yawo a

cikin gidan ALJANNAH

saboda wata BISHIYA

daya sareta akan hanya kada ta

cutar da mutane”

.

8. Duk wanda ya riki

GASKIYA a

maganganun sa, zata shiryar dashi zuwa

ALJANNAH”

.

9. Duk wanda ya kiyaye

HARSHEN sa da

AL’AURAR sa, ANNABI S.A.W yace shi kuma ya

lamunce

maka ALJANNAH”

.

10. ANNABI S.A.W ya

gayawa sahabinsa kada ka yawaita

FUSHI zaka shiga

ALJANNAH”

.

11. Duk wanda yaje

duba MARAR LAFIYA, zai shiga

See also  The 99 Names of Allah in Arabic and English Meaning

ALJANNAH”

.

12. Allah Ya fadi a

Hadisin kudsi, duk

wanda BALA’I yazo masa, karon farko yayi

HAKURI, babu

abinda ya dace dashi

face ALJANNAH”

.

13. Duk MACEN da ta sallaci SALLOLINTA

biyar, ta AZUMCI

watanta, ta kiyaye

FARJINTA, tayi biyayya

wa MIJINTA,

zata shiga ALJANNAR ubangijinta”

.

14. ANNABI S.A.W yace,

duk wanda ya

lamunce min ba zai yi

ROKO ba, zan lamunce masa

ALJANNAH”

.

15. Wanda yayi

LADANCIN shekara 12

zai shiga ALJANNAH”

.

16. Duk wanda a

kokarin kare

DUKIYARSA aka kashe

shi, zai shiga ALJANNAH”

.

17. Duk wanda ya

toshe wata kofa, a

sahun JIHADI ko

SALLAH, ALJANNAH ta tabbata gareshi”

.

18. Babu wanda zai

MUTU bashi da GIRMAN

KAI, HA’INCI,

BASHI face ya shiga ALJANNAH”

.

19. KUNYA na cikin

IMANI, Imani na

ALJANNAH”

. 20. ANNABI S.A.W yace

duk wanda ya lamunce

masa

abubuwa guda 6, shi

kuma zai lamunce

maka ALJANNAH! •Duk maganan da

zakayi ka fadi GASKIYA,

•ka cika ALKAWARI

idan ka dauka,

•ka bayarda AMANA

idan an amince maka,

•ka kiyaye FARJINKA

•ka rintse IDANUNKA

daga kallon haram

•ka rike HANNAYENKA

daga zalunci”

.

21. Duk wanda ya kewa

Iyayensa BIYAYYA zai

shiga

ALJANNAH” .

22. Duk wanda ya

kasance mai yawan

ALWALA, kuma idan

yayi sai ya mata NAFILA

zai shiga ALJANNAH” .

23. Duk wanda ya

SHAIDA da kalmar

SHAHADA, ya shaida

Annabi Isa A.S bawan

Allah ne, kuma Aljannah gaskiya ce,

Wuta ma gaskiya ce,

Allah zai shigar

dashi ALJANNAH

gwargwadon aikin shi”

. 24. Duk wanda ya

zamto mai daukan

nauyin MARAYA, zai

kasance tare da ANNABI

S.A.W a ALJANNAH”

See also  Biography of Dr Ahmad BUK

. 25. Duk mai saukin kai

wajen saye da

sayarwan sa, Allah

zai shiryar dashi

ALJANNAH”

. 26. Duk ALKALIN da

yasan GASKIYA yayi aiki

da ita, zai

shiga ALJANNAH”

.

Wadannan kuma bacin yan Aljannah ne kuma

Shahidaine:-

.

27. Duk wanda gini ya

fado masa ya MUTU”

. 28. Duk wanda CIWON

CIKI ya kashe shi”

.

29. Duk wanda

ANNOBA tayi ajalinsa”

. 30. Duk wanda ya nitse

a RUWA ya zamo

ajalinsa”

.

ALLAH yabamu dama

da ikon aikatawa ko sanar da wasu

su aikata don Rabautuwa.

Leave a Comment

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Scroll to Top