Hayar Mace Hausa Novel
Tag: HAYAR MACE!
_(Destiny and se*ual story)_
_Oum Hairan_
*Note:* _Duk da cewar littafin nan ba free bane amma ina rokon Alfarma kada ki karanta min in kinsan bakida ƙarfin zuciyar ɗaukewa sannan na haramta karanta shi ga yan under 18, ban hana budurwa karantawa ba amma karki zargi Oum Hairan, karki duba ɓarnar dake ciki ki ɗauki sakon dake ciki zaifi miki amfani._
_Page one and two_
Dandazon matasan dake tsaye gindin bishiyar sune suka ɗauki hankalin matashiyar budurwar dake tafe sanye da doguwar riga baƙa tayi rolling baƙin dankwalin a kanta hannunta rungume da takardu da suke alamta da alama daga makaranta take.
Da sauri cikin faÉ—uwar gaba ta nufi gindin itaciyar har tana tuntuÉ“e takardun hannunta suna zubewa amma hakan baisa ta dakata daga kudurinta na kaiwa ga inda taga cinkoson matasan ba, can cikin hayaniyar da ba kowacce kalma ake fahimta ba taji ana cewa “Haba Mal Kabiru kai kuwa wanne irin É—an akuya ne da zaka tuso matarka har kwararo babu ko arzikin kallabi……”
Daidai lokacin matashiyar budurwar ta isa tsakiyar da’irar cikin kaÉ—uwa ta zube a Æ™asa tana cewa “Innanillahi Kumbo meye hakadin me kikayi masa ya dakeki haka Kumbo meye yasa bazaki rabu da Azzalumin……”
Rufe mata baki matar dake durÆ™ushe a gurin tayi tare da girgiza mata kai ta buÉ—e kumburaren bakinta tace “Danku nakeyi Safiyyah kul na Æ™arajin kince da mahaifinki azzalumi ba kalmar Æ´a me tarbiyya bace, nasani Dani da mahaifinku bamu bawa tarbiyyarku gudummawa ba saidai kuma ban gaza wajen nuna muku girman haƙƙinsa akanku ba Safiyyah akanku ne keda É—an uwanki, mahaifinku ya sakeni saki É—aya Kinga saura igiya É—aya aurena da ubanku ya Æ™are, saboda nace bazai turaki aikatau ba sannan bazai tura Safwan Libya neman kuÉ—i ba…….
Sharrrr idanun Safiyyah ya kawo ruwa me É—umi ta zame É—ankwalin kanta ta rufawa Kumbon ta ta kama hannunta ta miÆ™e ta haÉ—ata a jikinta tace “Kumbo ina yawan furta Miki ki daina kula Mutumin nan akan duk abinda yazo dashi idan abune me yuwuwa ayishi kawai idan kuma bamai yuwuwa bane dakansa zai barshi amma bana ganin daraja cikin kulashin da kikeyi kullum kuna gantalar mana da Æ™ima da darajar da dama ba ita ke garemu ba, muje gida na siyo Miki balangu me É—umi”
Nufar gidan nasu sukayi ginin ƙasa daya gaji da tsufa kwanon da aka rufa saman gidan duk yayi tsatsa gidan gidane na haya me ɗauke da ɗakuna bakwai sai bayi a can ƙarshen gidan sannan Madafi.
Wani dake gefe É—aya da alamun baikai kowanne girma ba shi suka nufa Saida Kumbo ta zauna sannan Safiyyah ta zaro jakar dake rataye a wuyanta ta buÉ—e ta dauko É—aurin ledar Æ™arami ta miÆ™awa Kumbo ta karÉ“a tana bin Æ´ar tata da kallo tace “Safiyatu ina kika samu kuÉ—i keda baki tafi makarantar nan da ko sisi ba har kika siyo nama?”
Zama tayi a gefenta tace “Na faÉ—a Miki ai muna tarin kuÉ—i kullum Naira Hamsin to shine yau aka fasa aka raba kowa ya samu dubu uku da É—ari biyar shine na siyo Miki balangu na É—ari biyar É—in kinga sauran canjin sai musayi taliya ko guda biyar ce sauran ma riÆ™e muyi cefane…….
Da sauri ta Æ™unshe kuÉ—in jin takun mahaifin nasu gabanta ne ya faÉ—i lkcn da taji yana cewa “ku sarakan ciki ko wato ke Safiyyah ba Æ´ar arziki bace, kowacce É—iya tana neman albarkar mahaifinta ke bandake saboda asararriya ce wannan gantalalliyar watsattsiyar uwar taki kika kawowa kuÉ—i har kina maganar asai abinci nufinki Ni nakasa kenan ko? To bani kuÉ—in ko naci ubanku dagake har uwar taki…..”
Ƙwace kuÉ—in Kumbo tayi ta miÆ™e tana cewa “Aikuwa banga dalilin da zaisa baka taÉ“a bawa yarinyar nan kuÉ—in makaranta ba a zubin Æ™osan da takewa Hadiza take samu ta biya kuÉ—in makaranta har tayi rara ta aje abinta to Kabiru koni baci mata kudinta zanyi ba tunda ba wata uwa nake tsinana mata ba in bikin Zuwai Æ™awarta yazo ta sai ankon bikin”
Hannu ya É—aga zai zubawa Kumbo mari Safiyyah tayi saurin riÆ™ewa da Muryar kuka tace “Don Allah Bappi ka daina sha’awar dukan Kumbo ya kamata ace ko don darajarmu dake tsakaninku ku rinÆ™a saurarawa juna, Kumbo ki bashi indai waÉ—annan canjin ne daya taÉ“a lafiyarki wataran zai iya sake illataki kina ganin dukan da yayi Miki kwanaki Saida kikaci kuÉ—i badon Allah yasa Mal me Almajirai ya taimaka ba da bamusan ya zamuyi ba to ina amfanin hakan”
Fusge hannunsa yayi ya sake nufar Kumbo ganin da gaske Mal Kabiru Æ™ara tara mata gajiya zaiyi yasa babu shiri ta É—auki kuÉ—in ta cilla masa tayi waje da gudu tana cewa “Kayi da wata ba A’ishatu ba mahaukaci” da hargowa ya fito yana cewa “A’i Ni kike cewa mahaukaci to wlh yau saina tura Miki takaicin da kika daÉ—e baki shaÆ™a ba ina raga Miki saboda yaran nan amma ke baki gani ko? Zaki gane ba tsoronki nakeji ba yau É—innan bakar munafuka kinsa mal me Almajirai ya takuramin Saida na dawo dake…….”
Tsaki tayi tace “Indai wannan watsattsen auren naka ne ai dashi gara tallan gwanjo nidai cikin shekara ashirin banga uwar abin dana É—orar ba banda baÆ™in ciki auren É—an giya ko asara….”
Safiyyah dake raÉ“e jikin gini inda sabo ta saba da wannan cece-kucen na iyayenta kullum a haka suke babu me ragawa wani tsakaninsu kowa gani yake É—an uwansa bai isaba itakam da tanada wajen zuwa da tabar wannan ruÉ“aÉ“É“en gidan nasu me cike da hargitsi kala² zame jikinta tayi ta nufi gidan maÆ™otanmu Mal me Almajirai da matarsa Sahura, tana shiga ta nemi guri kusa da Inna Sahura ta zauna ta rushe mata da kuka, Inna ta saki muciyar tace “Ni Sahura ina ganin rayuwa Safiyyatu ke kullum bakya rabuwa da damuwa da Æ™uruciyarki ki rinÆ™a sawa kanki damuwa…..”
Cikin kuka tace “Meye yasa kowanne gida kowanne ma’aurata zaka riskesu cikin walwala da son suga sun faranta rayuwar junansu amma banda Bappi da Kumbona kullum basu da burin da yafi suga sun Æ™untatawa juna?”
Murmushi tayi tace “Safiyyah kenan zuwa yanzu Yakamata ace kin saba da wannan yanayin Æ™addarar taku, iyaye ne kuka haÉ—u dasu dukkansu babu haÆ™uri babu kawaicin rayuwa kune haÆ™uri ya kama mahaifiyarku da tanajin magana da tuni ta daina sauraron Mal Kabiru bare takaisu ga duka amma itama A’isha taÆ™i bari kedai da kike mace ina horonki da kada ki É—auki halin mahaifiyarki na rashin haÆ™uri zakisha wuyar rayuwa da namiji”
Hannu tasa tana share mata hawayen tace “Danma Mal Kabiru yaÆ™i ne da masoyan nan da suketa zuwa da yabaki dama kin fitar da gwaninkin Yatuh da tuni kin huta da wannan kallon takaicin to yace shi ba kowanne irin namiji zai bawa aurenki ba”
Shiru ce ta ratsa can ta miÆ™e tace “Inna Sahura idan Kumbo ta daina kulashi suma zasu koma irinku a daina jin kansu?” Da sigar tausayawa tace “Abubuwa zasu ragu kam amma a daina gabaÉ—aya sai a hankali tunda ba’a faro rayuwar da haka ba…..”
“Safiyyah! Ke Safiyyah!! Kina ina ne ko sai na karya Miki Æ™auri….” Jikinta na tsuma da rawa ta cire mayafinta ta nufi wajen da gudu, can ta hangeshi jikin wata luntsumemiyar mota ya ranÆ™wafa da alamun magana sukeyi da wanda ke cikin motar.
Tunda ta nufo motar idanun wanda ke cikinta yake kanta harta iso ta durÆ™usa tace “Gani Bappi!….” Da zafinsa ya juyo yace “Ke…ke do Allah tashi Yatuh banason shirme Alhaji ka ganta dubeta sosai ka ganta dai babban Molu ce” tana miÆ™ewa na cikin motar yana fitowa, wani farin Balarabe ne a ganin Idanunta sanye Da kayan Hausawa ya É—ora baÆ™ar hula a saman baÆ™ar hularsa.
Kallo yakeyi mata irin na Æ™urulla wannan yasa Safiyyah yin Æ™asa da kanta tace “Bappi…..” RanÆ™washi ya zubanta yace “Alh bakace komai ba wannan harka kasan harkata ce kawai banason wannan arziÆ™in ya wucceni…..”
Batayi tunanin mutumin ya iya Hausa ba Saida taji yace “Yaronka yayi sosai inason yaro me yawan abubuwa zan ninka maka kuÉ—in indai yaronka yayi abinda akeso yayi” wata shashashar dariya Bappi yayi yace “Saini Uban Æ´an iska kawalin zamani abin kunya gaba na bashi ba baya ba Safiyyah ai kamar ta tafi Fatakwal ta gama maza maza muje ki É—ebo kayanki koda yake tsaya naje na É—ebo miki ke jeki haka ma a siya a can”
Karin wasu littafai da zaku so
-
Matar maza 3
-
Zuciya ta
-
Mahaukaci ko boyayyen masoyi
-
Wuka a makoshi
-
Aure da haihuwa
-
Husna Hausa Novel
-
Musayar Zuciya
-
Gangar Shedan
-
Angon mata biyu
-
A gidan mu take
-
Bafulatanar Rugga
-
Matar yaro
-
Mr Bello
-
Mijin Buzuwa
-
Gidan Uncle Complete
Tunda ya fara rawar jikin take kallonsa har Saida ya dire tace “Ina zani Bappi?” DaÆ™uwa ya watsa mata yace “Harkar arziÆ™i zaki tafi wannan da kike ganinsa bazan tsaya Miki bayaninsa ba a hankali zaki fahimci wanene musu gardama ko taurin kai a matsayinki na Æ´ar talaka matsiyaci irina ba naki bane, Safiyyah na bawa Alh Urwat hayarki daganan zuwa wani lokaci idan kinje komai da ya kamata ki sani game da ma’anar HAYAR MACE zaki sani….” “HAYAR MACE! Bappi meye hayar Mace?”
_Kamar yanda na rubuta a sama ba free bane paid ne saidai yazo da sassauƙan farashi Naira 200 PC 500 zaku iya turo kati MTN ta WhatsApp number 09013718241 ko ta acct 0255526235: gtbank ko ta first bank 3184512451 Fauziyya Tasiu Umar, ƴan Niger kuma katin Airtel zaku turo._
_Please ina tuni don Allah kada ki biya min littafina kuma ki zageni domin na rubuta a farkonsa bana buƙatar surutu domin bazaisa na fasa rubutashi ba._