Inada Hujja Hausa Novels
Ayshat ÆŠansabo lemu
ASALIN LABARI
Zaune take ta tasa cup É—in shayi ruwan bunu a gaban ta,wanda ko arziÆ™in sukari babu a cikin sa.Tsuran ruwan lipton É—in ne kawai ta ke juya shi da cokali,ba tare da cewa akwai mahaÉ—in da xata haÉ—a dashi ta sha ba,hawaye ne masu tsananin xafi ke sauka bisa kuncinta ba tare da ta damu da ta tsaida su ba,daga gefen ta Æ™anin ta Aliyu ne ke zaune yana faman shan ruwan lipton É—in tamkar ya samu wani zuma.Sam bai damu da rashin mahaÉ—i ko rashin sukarin da babu a cikin sa ba,burin sa kawai dama ya ji wani abu na ratsa cikinsa don rabon su da saka wani abu a ciki tun jiya da rana.Yanzu É—in ma Khairiyyah ce ta tuno tayi ajiyan lipton É—in cikin kayan ta,shine har ta samu ta haÉ—a musu suna sha,kafin su ga dawowan Yayan su Ahmad da yace su jira shi ya fita ya dawo.Kanta ta É—aga takai duban ta can ma’ajiyan kayan makarantan ta inda ta ke ajewa,wasu hawayen suka zubo mata tana jin yadda zuciyanta ke sake É—aukan tsananin zafi na tausayin kansu da halin da suke ciki.Rabon ta da karatu shekara É—aya kenan tuni qawayen ta sun jima da shiga SS1 na sakandiri.Amma ita tunda ta samu ta gama JS 3 shiga SS1 É—in ya gagare ta.Gashi Allah ya É—aura mata burin son karatu,tana matuÆ™an son ta ga ta zurfafa karatu har zuwa matakin gaba da sakandiri,amma babu halin hakan wanda zai tallafe ta ta cinma gaci,babu tai masa katutu Æ™arfin sa ya gaza.A shekarun ta na goma sha biyar ya ci a ce ta shiga matakin Senior Secondary school.Kaman yadda qawanyen ta suka wuce,sai dai ita a lokacin da sakamakon jarabawan JSCE É—insu ya fito alokacin ne iftila’i ya faÉ—awa Malam,masu garkuwa da mutane sukai nasaran tafiya da shi, akan hanyan sa ta dawowa daga Zangon Aya,ya je aikin É—aukan Siminti da aka sauke sun kammala aikin ne za su dawo gida aka tare motan da su ke ciki akai garkuwa da su.Hakan ya zamo silan sake jefa rayuwansu Khairy cikin garari,har zuwa lokacin da Allah ya kuÉ“utar da shi da Æ™arfin ikon sa ya dawo gida.Bayan sun gama cire rai da sake saduwa da shi,don koda wasa sun san in dai sai an biya kuÉ—in fansa ne xai dawo gare su to sai dai ya rasa rayuwan sa a hannun masu garkuwa da mutanan.Cikin ikon Allah su na xaune da maraicen wata ranan Laraba sai gashi ya shigo gidan wurjanjan.Bayan ya shafe sati bakwai a hannun su,tunda ya shigo gida a tsananin galabaice ya shigo.Wanda kallo É—aya zakai masa ka san ikon Allah ne kawai ya kawo sa gidan,nan tsakar gida ya faÉ—i faÉ—uwan daya zamo silan samuwan laluran sa da har yau yake fama don saura kiris ya rage ya rasa sashin jikin sa na dama,hawan jini yai masa mummunan kamu Allah ne ya taÆ™aita abun bai nakasa sosai ba,tunda a yanzu an samu yakan dogara sanda ya fita zuwa masallaci amma baya ga masallaci baya nisa da gida sam,yana zaune a gida ne kawai yau ciwo gobe lafiya,sabida rashin samun shan magungunan sa yadda ya dace.Ga kuma tunanin halin da su ke ciki na Æ™unci da talauci,wanda hakan ke sake taka rawa wajen taÉ“arÉ“arewan lafiyan sa,ba su da wani gata sai Allah sai kuma É—an sana’an wankau da su ke yi idan sun samu,sai ko kitso da Khairiyyah ke yi da shine su ke samu su ci su sha,har su yi É—an Æ™ananun buÆ™atu na yau da gobe,randa ba su samu ba su kwana da yinwa.ArziÆ™in su kenan gidan da suke xaune na su ne da wani abokin arziÆ™in Malam É—in ya mallaka masa,wanda a halin yanzu ya rasu su ma iyalin sa sun tattara sun bar Zaria sun koma mahaifan mijin na su can Bauchi.Hakan yasa rayuwa ya sake tsananta ga Malam Lawal da iyalin sa dama Alhaji Harunan ne yake taimaka musu to shima gashi sun rasa shi.Khairiyyah ta sake juya cokali a cikin kofin shayin tunanin ta na katsewa a lokacin da ta jiyo muryan Aliyu yana faÉ—in”Yah Khairiyyah Inna na kiran ki.”
Wacce ya kira da Khairiyyah ta sauke manyan idanun ta a kan sa,sam ita bata ji kiran da Innan ke jero mata ba.Ta miƙe cikin sauri tana aje cokalin hannun ta da take ta faman juya shayin da tunani ya gagara barin ta ta sha,haka ta fice zuwa ɗakin Inna tana amsa kiran da take mata da faɗin.
“Na’am! Inna gani nan zuwa.”
Da sallama ta shiga É—akin bayan an bata izinin shiga,ta isa kusa da Inna Salamatu wacce take zaune a gaban Malam Lawal tana juye masa kokon da Yayan su Khairiyyah Ahmad ya shigo musu da shi a cikin kofi.Ahmad na zaune daga gefe guda shima yana shan kokon cikin kofi,Khairiyyah ta dube sa tana faÉ—in “Yah Ahmad sannu da shigowa.”
“Yauwa sannu Khairy, Ba dai xaki daina yawan koke-koken nan bako?”
Ahmad ɗin ya faɗi tausayin su na sake mamaye zuciyan sa,yana sake jin cewa ya zama dole yayi anfani da lafiyan sa wajen dagewa da nema musu koda na abinci ne.Tuni ya jingine maganan Karatun sa shi ma,tunda ya samu ya kammala secondary da ƙyar ya aje batun karatun a gefe sabida rashin madafa,yanzu haka gareji yake zuwa yana kanikanci ɗan abinda yake samowa ne ake samu aci abinci,har a sai maganin daya samu wanda Malam ke sha.
Tunanin sa ya katsene da jiyo muryan Malam dake ma Khairiyyah magana yana faÉ—in “Taho nan kusa dani Mamana kinji,don Allah Ummul-Khairy na ki cire duk wata damuwa,ki zama me juriya akan duk halin da xaki tsinci kanki a rayuwanki.Sam bana jin daÉ—in wannan yawan kukan da kike akan irin jarabtan da muke ciki,karki manta Allah baya taÉ“a É—aura ma duk wani rai abinda bazai iya É—auka ba.Ubangijin mu yana sane da mu yana sane da halin da muke ciki Khairy,zai kuma kawo mana É—auki da izinin sa.Na sani rashin karatun ku yana damun ki to amma kiyi haÆ™ury ina ji a jikina zakiyi karatu ko ba yanzu ba zaki cika burin ki na zurfafa karatu Ummu.Don haka karki cire rai da rahaman ubangiji ku cigaba da addu’a kawai Allah zai kawo mana mafita.Maza É—akko wani kofin a zuba muku kokon ku ma ku sha ke da Aliyu kinji Mamana.”
Khariyyah ta share hawayen dake zuba mata tana me gyaÉ—a kai ta miÆ™e ta fice don É—akko cup É—in.Malam Lawal ya maida duban sa ga Ahmad yana faÉ—in “Amadu kana dai ganin yadda rayuwa take gara mana ko?Nasiha ta a gareka a kullum shine ka sake dagewa da mai da hankali akan aikin garejin nan.Ka nemi sana’a ta halak kayi don ka rufa mana asiri da Æ´an Æ™anninka da kai karan kanka.Ban yadda da yawon maula ko bin gidajen mawadatan mu ba,kunfi kowa sanin irin yadda kuka taso kuka ganni ina gudanar da rayuwata,ni me yawan zafin nema ne don kawai in tallafe ku in inganta rayuwanku tare da kare mutuncin kaina.Ina da Æ´an uwa mawadata kun sani amma baku taÉ“a ganin na je gare su da sunan naje maula ko bara akan ataimake ni ba,sai in su ne su ka ga dama su ka bani É—an abinda su kai niyya,ba kuma komi yasa hakan ba sai gudun wulaÆ™anci.Allah ya gani nayi iyakan yina har kawo yanzu da Æ™arfi na ya gaza lafiya ya kuÉ“uce min,duk da hakan kuma baka taÉ“a ji ko ganin na É—auki sandata ina bin gidajen masu hannu da shuni da sunan naje maula ba.Don haka duk wani É—a na da zai zama É—an maula bazan taÉ“a yin alfahari da shi ba,ku tashi ku nemi halak É—inku,kaine babba kaine kuma namiji don haka ka zama me kishin mu da sauran Æ´an uwanka.Duk abinda zaka samu ka tuna dasu ka tallafe su musamman Mamana da take mace,ka kuma ji tsoran Allah a duk inda kake ka xama me riÆ™e amana da gaskiya,domin sune matakin nasara Allah yai maka albarka ya dafa maka a dukkan lamuran da xaka sanya gaba.”
“Ameen Malam insha Allah zaka sameni me aiki da dukkanin nasihohin ka,bari in tashi inyi shirin fita garejin zamu tafi da Aliyu shima.Abin da na samu sai na aiko shi da É—an abinda xa’a ci da rana.”
“To shikenan tashi kaje Allah yayi albarka.”
Inna ta amsa da “Ameen ” ita kuma Khairiyyah da ta shigo riÆ™e da cup É—in ta isa gaban Malam É—in ta aje,ya dube ta da murmushi akan fuskan sa yana zuba mata kokon tare da tsare ta ta shanye a gaban sa,ana haka Aliyu ya shigo shi ma aka zuba masa ya sha,kafin Inna Salamatu ta sanar da shi zasu fita tare da Yayan sa Ahmad zuwa gareji.
Khairiyyah ne ta miÆ™e tana haÉ—a kufunan da suka gama shan kokon da su ta fice,don zuwa ta wanke ta maida su ma’ajiyan su.Ko da ta fito daga kitchen É—in É—akin da aka bar mata a matsayin mallakin ta ne,wanda yake falle É—aya ne É—an madaidaici me É—auke da katifa sai drawern kayan sawan ta da sauran tarkacen ta,tsaf É—akin yake cikin tsafta komi a kintse yake a kuma inda ya dace,wanka tayo ta dawo É—akin don shiryawa ni dai kallon ta kawai na ke sabida yadda komi na ta ke birge ni,kyakykyawace na nunawa sa’a da alamu idan ta gama xama cikakkar budurwa za’ai kallon diri da kyawu.Color É—inta me tsananin kyau ne sam ba fara bace sai dai akirata me hasken fata sosai ba mai duhu ba wanda turawa ke kira da (Brown skin) tana da hanci wanda ya tafi a miÆ™e zar tana da manyan idanu farare tas masu É—auke da lashe’s gazar-gazar,É—an Æ™aramin bakin ta yafi komi É—aukan hankali na,giran ta me cike da baÆ™in gashi cinkis tamkar anzana shi,shine abinda ya sake fiddo kyawun ta.Kaman yadda yalwataccen gashin ta da jelan kitson dake kanta ke reto bisa kafaÉ—un ta ya É—auki hankali na.Doguwace amma tsayin ba irin can É—innan ba,tana da murjajjan jiki me É—auke da lafiyayyan fata,kai kace a gidan hutu da jin daÉ—i take rayuwa.Cikin sauri-sauri take sanya kayan ta tana gamawa ta miÆ™e ta fice zuwa É—akin Inna don tambayan Mallam zuwa gidan su Maryam Waziri da take son yi ta duba jikin ta,don kwana biyu kenan bata zo Islamiya ba.
So take tayi sauri taje ta dawo don kada azo yin kitso ko su samu wankau ya zam bata nan,ko da ta tambayesa ta sanar dashi inda zata ya bata izinin zuwa,tare da sanar mata cewa da ta je ta dubo jikin Maryam É—in tayi sauri ta dawo gida kada ta yadda ta zauna,daga haka taima Inna sai ta dawo ta fito ta sake komawa É—akin ta,Hijab É—inta wankakke tas ta ciro daga drawern kayan ta ta sanya,ta fito fes da ita ta sanya takalmin ta ta fice daga gidan.Bayan tayi addu’an fita gida kaman yadda ta saba,duk wadda ya ganta ya ga natsatstsiyan matashiyan budurwan yarinya da ta samu tarbiya me nagarta.
******Lokacin da Khairiyyah ta dawo tun daga ƙofar shiga gidan na su ta ja ta tsaya,tana sauke manyan idanunta akan ƙatuwar motan da ta gani fake a ƙofar gidan su.Tsananin mamaki take yi tare da jin bugun zuciyan ta na sauyawa,tsora da fargaba na mamaye zuciyanta,ta shiga jan ƙafafun ta da taji sun mata nauyi tana takawa zuwa cikin gidan,zuciyan ta na ayyana mata wasu irin baƙi ne su kai da su ka zo a cikin irin wannan ƙatuwar mota haka?
Tana sanya kanta cikin zauren ta fara jiyo maganganu Æ™asa-Æ™asa na baÆ™in muryoyin da bata sani ba,hakan ya sa ta É—aga Æ™afa ta shiga cikin gidan bakinta É—auke da sallama,idanunta suka sauka akan dattijon mutumin tare da wata mace a gefensa wacce itama da alama shekaru sun fara tura mata,Inna ce ta amsa sallaman da tayi yayin da mutanan duk su ka waiwayo su na sauke ganin su akan Khairiyyah,wacce tayi saurin risinawa tana gaida su cike da ladabi.Suka amsa da tsananin sakin fuska bata sake jiran komi ba ta nufi É—akin Inna ta shiga,da Aliyu ta fara yin tozali kwance bisa É—aya daga cikin kuzajjiyar doguwan kujeran da suka mallaka a É—akin,kansa naÉ—e da bandeji fuskan sa ya haye yayi suntum da kumburi.Wani faÉ—uwan gaba ta ji ya sameta ta isa kusa da shi da sauri tana faÉ—i a fili “Subhanallah! Aliyu me ya sa me ka haka?”
“Tsautsayi ne ya same sa Khairy,waÉ—annan mutanan da kika gani ne suka kaÉ—e sa abakin titi akan hanyansa ta dawowa gida,Allah ma yasa mutanan Æ™warai ne da har su ka tsaya su ka dubi raunin da yaji har su ka kai shi asibiti.”
Inna ce me wannan maganan tana isa kusa da inda Aliyu ke kwance tana sake duba shi,Khairiyyah cike da alhini da tausayin Æ™anin na su ta dubi Inna Salamatu tana faÉ—in “Allah sarki Aliyu Allah ya baka lafiya,kaman na san ba lafiya ba ina ganin mota a waje naji gabana ya faÉ—i.”
Sallaman Malam Lawal da shigowan sa cikin É—akin dogare da sandar da yake doddogarawa ne ya hana Inna sake magana,ya dubi Khairiyyah yana faÉ—in “Mamana kinga tsautsayin daya sami qanin ki ko?Allah ma ya taÆ™aita da iya rauni ne kawai yaji babu karaya,kuma Allah yasa mutanan kirki ne suka kaÉ—eshi,da wasu ne yadda zasu gansa mara galihu sai suyi tafiyan su ba tareda sun tsaya ba.Amma wannan dattijon arziÆ™i ne da alama daga shi har me É—akin sa sun san darajan É—an adam.”
“Hakane Malam nima mutanan sun birgeni,dubi yadda su ke ta faman bamu haÆ™ury,Allah dai ya saka musu da alkhairy ya kiyaye gaba.”
A tare Khairiyyah da Malam su ka amsa da “Ameen.” Malam É—in na sanya hannun sa cikin aljihu ya zaro kuÉ—i masu yawa yana faÉ—in “Kinga abinda Dattijon ya bayar Salamatu yace a sake siya masa magani.HaÆ™iÆ™a Allah me rahama ne ga bayin sa ta hanyoyin da ba su yi zato ba,tabbas wani tsautsayin sai ya janyo maka alkhairy,ungu Mamana irga ki ga nawa ne kuÉ—in?”
Yaƙare maganan da miƙawa Khairiyyah kuɗin wacce tuni ta cire Hijab ɗin jikinta tana zaune a ƙasa kusa da kan Aliyu,ta amshi kuɗin fuskan ta na bayyana farin cikin ta itama da samun waɗannan kuɗi.
“Laaah! Malam wallahi har naira dubu goma ne kuÉ—in.”
Khairy tayi maganan cike da tsananin mamakin yawan kuÉ—in,murmushin farin ciki na sake bayyana akan kyakykyawan fuskan ta,suma dukkanin su da alama sunyi mamakin yawan kuÉ—in,Malam ya amsa yana me zama a bisa É—aya kujeran one seater dake É—akin yana duban Inna yake faÉ—in “Masha Allah,Allah mun gode maka da wannan ni’ima daka kawo mana,abinda za’ai yanzu Salamatu zaki tashi kuje nan kasuwan tudun wada ke da Mamana ku gwado mana kayan abinci dai-dai misali da duk wani É—an abin da mu ke da buÆ™ata.”
Inna ta gyaÉ—a kai cike da Æ™aunar mijin ta,daya kasance ba shi da wani buri irin ya gansu cikin wadata da walwala,shi yasa har gobe ba ta nadaman kasancewansa miji kuma uban Æ´aÆ´an ta duk da babun sa,domin tayi imani talaucin da suke ciki jarabawan su ne ita da shi domin da zafin nema yanasa a fita daga Æ™angin talauci tabbas da tuni sunyi hannun riga da ba-bu tunda daÉ—ewa,domin Malam mutum ne shi me zafin zuciyan neman na kansa da yin duk wani aikin Æ™arfi don yaga ya rufa musu asiri sunfi Æ™arfin ci da sha da sutura zuwa karatun yaran sa bakin gwargwado,amma da yake haka Allah yaso ya gan su babu yadda su ka iya.Ta sauke a jiyan zuciya tana faÉ—in “To shikenan Malam bari mu hanzarta da ma gashi rana ta fara yi ba tare da mun san abinda za mu ci ba,amma ka É—auki koda naira dubu biyu ne ko dan siyan maganin ka.”
Yadda tai maganan cike da narke murya alamun magiya yasa Malam Lawal sakin Æ™ayataccen murmushi,Æ™aunar matansa na sake huda jinin jikin sa,tabbas ya sani samun mace haÆ™urarriya me É—inbin tawakkali da haÆ™uri da ba-bu irin Inna Salamatu sai an tona cikin wannan xamanin,bata taÉ“a nuna masa gajiyawa da halin da su ke ciki ko tai masa gorin talauci ba,sai ma yadda take aiki da jikin ta da lafiyan ta don a taru a rufawa juna asiri.Ya dube ta cike da Æ™auna yana faÉ—in “Karki damu Innan su ku je da kuÉ—in duka ba sai na É—auki komi ciki ba,sai dai Khairy ta É—auki kwalin maganin can sai ku siya mun kwali biyu,sauran kuÉ—in ku siyo duk abinda ya dace,zaman mu babu abinci ba Æ™aramin É—aga min hankali yake ba,ina baÆ™in cikin mu wayi gari ba mu da abinda za mu ci,amma bakomi Allah na sane damu kuma ina da yaÆ™inin zai kawo mana mafita cikin rahaman sa da tausayinsa ga bayin sa,kuyi maxa ku je ku dawo É—in.”
Kusan a tare Inna da Khairiyyah su ka miƙe don cika umurnin sa,su kai masa sai sun dawo su ka fito sanye da Hijaban su a jiki,tafiya su ke su na tattauna matsalolin su da yadda rayuwa ke gara mu su,Inna na sake kwantar ma Khairiyyah da hankali tana nuna mata muhammancin haƙury akan duk halin da bawa zai tsinci kansa a ciki watarana zai wuce,ya zama tarihi har su ka tari a dai-daita sahu su ka shiga kafin su kame bakin su bayan sun sanar da ɗan sahun inda xasu sauka.
Bakin gwargwado sun siyo kayan abincin da zasu ci,wanda a Æ™allah zai mu su kaman kwanaki huÉ—u zuwa biyar,cike da farin ciki su ka dawo gidan su ka ajiye komi a inda ya dace bayan sun zube kayan Malam ya gani ya sama siyayyan albarka,tare da yin addu’an fatan alkhairy ga wanda ya basu kuÉ—in.
Koda Aliyu ya tashi daga bacci Inna ce tai masa wanka ta gasa masa jikinsa,Jallof ɗin taliya da suka dafa ta kawo gaban sa ta aje bayan ta sanya masa kaya,da kanta ta ciyar da shi Khairiyyah dake gefe riƙe da magungunan sa da ta ɓallo ta miƙa masa tana masa sannu,bayan ya shanye maganin sai Inna tace ya ɗan zauna har abincin yabi jikin sa sai ya sake kwanciya.
Ƙarfe huÉ—u Khariyyah ta fito cikin shirin tafiya islamiyyah,tana sanye da Maroon É—in Hijab wanda shi ne matsayin uniform na islamiyan,sosai kalan yake mata kyau matuÆ™a,kafaÉ—an ta rataye da jakan littafan ta,taima su Inna sallama ta fice su na mata fatan dawowa lafiya, a Æ™asa suke takawa xuwa islamiyan kasancewan basu da nisa can Æ™asan layin su ne,tafe take tana jin nishaÉ—i a cikin zuciyanta,tana tsananin son karatu(Both) boko da islamiya kuma Allah ya bata Æ™waÆ™walwan É—aukan karatun,tana da masifan Æ™oÆ™ary a hadda da islamiyan na su,shiyasa malaman ke alfahary da ita,lokacin da suka fuskanci matsalan school fees(kuÉ—in makaranta) na son kawo ma karatun Khairiyyah matsala sai suka yafe mata biyan kuÉ—in makarantan baki É—aya,hakan ba Æ™aramin faranta ran Khairiyyah da iyayen ta yayi ba,Malam da kansa ya je har makarantan yai ma malaman godia.Yanxu matsalan dake damun Khairiyyah yana cin xuciyanta bai wuce matsalan rashin cigaban karatunta na boko ba,gashi har an dosa shekara guda,wannan tunanin da tayi ne ya rage walwalan ta,haka dai ta ke takawa sannu a hankali har ta karya kwanan da zata É—auki hanyan makarantan direct,idanunta ta sauke akan Æ™aton gidan da aka gina cikin watanni uku kacal,gini ne na gani na faÉ—a wanda kaf anguwan dama sauran layukan dake gaban su babu gida kwatankwacin sa,tun da ake ginin duk wanda ya zo wucewa sai ya tsaya ya kalla bare kuma yanxu da aka kammala komi tarewa acikin sa kawai ya rage wa ma su shi,gini ne da ta sha ji mutane na faÉ—in irin na Æ´an Abuja ne,idan tace gidan baya birgeta to tabbas ta yi Æ™arya shi ya sa duk sanda zasu wuce ta gaban gidan ita qawarta abokiyan jerawanta zuwa islamiya Ruky Sulaiman sai sun tsaya sun morewa kallon sa,tana tasbihi ga Allah daya yo ma su arxiÆ™i da marasa shi,tana cikin Æ™arewa gidan kallo ne taji an dafa kaÉ—unta ta baya,cikin sauri tayi saurin waiwayowa idanunta na sauka akan RuÆ™ayyah Sulaiman.Wacce ta kasance Qawa a gun ta kuma maÆ™otan juna da suke suna abin arziÆ™i sosai,kuma aji É—aya suke a Hadda da Islamiyya baki É—aya.Ganin Ruky ce hakan yasa Khairiyyah sakin bayyanannen murmushi cikin muryan ta da yake a narke cike da Æ´ar shagwaÉ“a ta ke faÉ—in “Kai Ruky Sulaiman kinfa so tsorata ni.Ina nan ina kallon aljannan duniya sam bana gajiya da Æ™arewa gidan nan kallo,da alamu mamallakin gidannan ba Æ™aramin dukiya ya tara ba.”
Ruky ta dubi Khairiyyah itama tana sakin murmushi,tare da kallon gidan tana faÉ—in “Tabbas kam yana da kuÉ—i sosai a yadda naji su Yah Kamal na labari,sun ce ma wai nan da sati biyu masu gidan zasu tare anan za su yi azumi har zuwa sallah shi da iyalin sa.”
Khairiyyah ta jinjina kai tana faÉ—in “Masha Allah to Allah sa su zame mana maÆ™wabta na gari,don ni lamarin masu kuÉ—in yanzu yana bani tsoro yadda sam babu tausayin talaka da sanin darajan sa a zukatan su inba za su bautar da shi bane.”
Yadda Khairiyyah tayi maganan cikin tsananin raunin murya,yasa Ruky sake jin tausayin su ya kamata.Ta sani duk da suma talakawan ne amma sau dubu sunfi su Khairiyyah wadata tunda su dangin mahaifinsu suna taimakon su akai-akai,ba kaman su Khairy bane da basu da kowa a garin sai Allah sai wanda ya dubi Allah ya tallafa musu.Har su ka jera su ka isa islamiyan na su ba su daina tattaunawa akan halin masu kuÉ—in yanxu ba waÉ—anda da yawan su basa son taimakon talakawa.
Ƙarfe Six na yamma aka tashe su still tare da RuÆ™ayyah suka jero zuwa gida,gida uku ya raba tsakanin gidan su Ruky da na su Khairiyyah,sun zo daf da Æ™ofar gidan su Ruky su ka tsaya su na sallama da juna,RuÆ™ayyah ta dubi Khairiyyah tana faÉ—in “My Khairiyyah idan an taso skull gobe zan zo ki É—an kwashe min kaina,daga nan kawai sai mu wuce Islamiyyah tare zan taho da shiri na.”
Khairiyyah ta zabgawa RuÆ™ayyah harara tana faÉ—in “Ai tun da na ji yadda kika karya murya wajen kiran sunana na san zancen kitso ne,to shikenan Allah ya kaimu goben lafiya ki gaida Guggo.”
“Zata ji Khairy ke ma ki gaida min Inna.”
Cewan Ruky tana shigewa gida ita kuma Khairy ta kamo hanyan zuwa gida,zuciyanta cikeda kewan karatunta na boko data rasa,wasu hawaye taji na son taruwa mata tayi saurin maida su tana tuna nasihan Malam a gare ta ” _Khairy ki miÆ™a lamuranki ga Allah tare da godema ni’iman sa gare ki,ki sani kinfi wasu gara ke kin kai matakin aji a uku a sakandiri É—in sannan kika tsaya.Kin iya rubutu da karatu hatta É—an turancin nan kina ji kin kuma iya shi bakin gwargwado,wasu na nan cikin duhun jahilci na babu Arabi ba Bokon,ke kuma duka Allah yai miki ni’ima da samun su bakin gwargwado,don haka ki gode masa idan da rabon zaki cigaba sai ki ga Allah ya kawo wani hanyan._ ”
Tunanin ta ya katse ne a lokacin da ta iso ƙofar gidan su,ta sauke ajiyan zuciya tana jin zuciyan ta na yin sanyi a duk sanda take tuna irin rarrashi da nasihan Malam a gare su,tana sake jin ƙaunar sa na sake ratsa zuciyan ta.
Da Yah Ahmad suka kusa gwabza karo zai fita,tayi saurin ja da baya tana faÉ—in “Sorry Yah Ahmad.”
Ya balla mata harara yana faÉ—in “Allah ya shirya ki Khairy mutum yai ta tafiya baya kallon gaban sa.”
Tasaki dariya tana raɓa shi ta wuce zuwa cikin gida
Shatu ÆŠansabo ce 👌🏻