*KAWA ZUCI*
*©SALMA AHMAD ISAH*
•°•Dedicated to A & A, AMINA AHMAD ISAH (AMEERA) And AMINA ISAH IBRAHIM (NANAMEERA).•°•
°Gaisuwa zuwa ga mutanen kirki, Khadeeja Abubakar Alkali a.k.a Khadeeja Candy da kuma Zainab A Baba a.k.a Abokiyar Hira. Adduarsu gareni ko da yaushe ita ce Allah ya yi riko da hannayena, alkairin Allah ya kai muku a duk inda kuke°
بسم الله الرحمن الرحيم
*01*
*Masarautar Dutse, Jigawa state…*
“Adda!”
Wata matashiya ta ƙira tana daga tsaye jikin kofar shiga ɗakin mahaifiyarta. Hajiya Samira matar sarkin Dutse ta farko, wadda kowa na fadar ke ƙiranta da Adda ta juyo a nutse ta kalli autar ‘yarta Muhibba dake tsaye a ƙofar ɗakinta. Kafin ta juyo ta aje carbin hannunta a kan dardumar da take zaune, ta shafa addu’ar da ta yi. Ta sake juyawa ta kalli Muhibba da ta zauna a saman gadonta.
“Me ya fa faru?”
“Nan da sati wani watan za mu koma school, kuma…”
Wani irin ihu da suka ji an kwalla a cikin sashin Addar ya sa Muhibba kasa ƙarasa maganar da take son faɗa. Kusan a tare suka dubi juna ita da Addan da gabanta ya faɗi, dan ko ba a faɗa ba ta san cewa ihun ba na kowa ba ne face ‘yarta Maryam.
“Adda abin nata ne ya tashi”
Cewar Muhibba tana juyawa da sauri ta fice daga ɗakin da gudu. Ita ma kanta Adda ɗin ba ta zauna ba, bayanta ta bi suka shiga sahin da ɗakin Maryam ɗin yake. Kafin su isa ɗakinta suka ci karo da ita a hanya, ta fito da gudu, yanda ta bangajesu ta wuce zai sa ka gane cewa ba ta cikin hayyacinta, sannan kuma ƙarfin ma ba na ita kaɗai ba ne.
“Wayyo Allah hannuna!”
Muhibba da ta buge hannunta da bango ta furta cikin jin zafin ciwon hannun nata.
“Malam yace kada mu taɓa bari ta fita, mu je mu kamo ta.”
A hanzarce suka fita babban falo, lokacin da Maryam ke gaf da ficewa daga sashin Adda gaba ɗaya, hakan ya yi dai-dai da shigowar SA’AD yayansu, kuma ɗan fari a cikin yaran Fulani Amarya matar sarkin Dutse ta biyu. Ganin abin da ya yi zato ne ya tabbata ya sa ya yi azamar kamo Maryam dake shirin bugeshi ta fita daga sashin.
“Ke Maryam! Maryam! Ina za ki je?”
Ya tambaya yana kokuwa da ita dan gaba ɗaya karfinta ta zage take son ƙwacewa daga riƙon da ya mata. Yanda take ƙwala ihu zai sa ka fahimci cewa ba a hayycinta take ba.
“Ku ƙyaleni! Sa’ad ku ƙyaleni! Wurin Abba zan je, ni wurin Abba zan je”
Gaba ɗaya idanuwanta a ƙafe suke, ihu take tana kokuwa da shi, Adda da Muhibba ko sun kasa yin komai, ita Muhibba ma kukan tausayin ‘yar uwarta take. Domin tana fama da wani irin ciwo ne da ba a san kansa ba, dan har ana zargin ko ta haukace ne… kuma wannan ciwon da take fama da shi ya hanata zama a gidan mijinta.
“Waye Abba? Kuma a ina yake?”
Sa’ad ya sake tambayarta.
“Abbana… Abbana”
Ta ƙara ƙaimi wurin kwaɗa ihun da hatta hadimai da bayin dake sashin sai da suka fito dan ganin abin da ke faruwa, duk da hakan ba wani sabon abu ba ne garesu, har cikin dare ma sai ta farka ta dinga iface-iface da buge-buge, abin dai sak ciwon hauka.
“Kin manta da ni ne Abban naki? Rannan ba kin ce ni ne Abba ba?”
Sai a lokacin ta tsaya da ihu tare da kokawar da take da shi.
“Abba?”
“Eh Abba, Ya Sa’ad Abbanki…”
Ta kuma yin shiru tana kallonsa kamar sha-sha-sha. Da ido Sa’ad ya yi wa Muhibba alama da ta kunna karatun al’kur’ani. Aiko da sauri ta kunna a wayarta, take Maryam ta dafe kanta tana faɗin.
“Abba ka ce su kashe”
“kina so su kashe?”
Ta yi saurin gyaɗa kai idonta a rufe.
“To mu je ɗaki… A can babu karatun”
Ta buɗe idonta ta kalle shi. Ya gyaɗa mata kai alamar tabbatarwa, da wayo da komai ya jata zuwa ɗakinta, ya lallaɓata ta kwanta a saman gado.
“Ki yi bacci abinki, Abba ba ya son yana ganinki kina kuka… Kin ji?”
Ta jinjina kai tana sharar hawaye, bai fita daga ɗakin ba sai da ya kunna karatu, idonta a rufe yake, amma faɗi takw ya kashe, ya kashe ita ba ta so, har ta yi bacci bakinta bai yi shiru ba. Ganin ta yi bacci yasa ya fita ya barta kwance, a falo iske Adda zaune ta yi jigum, damuwar duniya duk ta bi ta isheta saboda wannan ciwon na Maryam, a saman carpet ya zauna yana kallonta.
“Adda na lallaɓata ta kwanta, na san zuwa anjima idan ta farka za ta dawo dai-dai kamar ba ita ba, ki kwantar da hankalinki”
Adda ta sauƙe gwauron numfashi tana jinjina kai, domin abin da ya faɗi ɗin haka ne, ciwon nata zuwa-zuwa ne, idan ya tashi sai ta birkice a kasa ganeta, idan kuma ya kauce sai ka ganta cikin nutsuwarta kamar ba ita ba.
“To Sa’ad… Allah ya saka da alkairi”
“Haba Adda! Sai kace bare? Ai ko bare zan yi wa wannan abin ballantana ‘yar uwata”
Adda ta yi murmushi.
“To Allah ya yi albarka”
“Amin… Amma zuwa yaushe za a kaita asibitin nan ne? Ya kamata a san me ke damunta”
“Hmmm Sa’ad ba na jin wannan ciwon na Maryam na asibiti ne, shi yasa ko da mai martaba ya zo min da zancen zuwa asibitin na ce ya bari mu gwada na gargajiya tukkuna, tun da shi ma Sadiq ɗin (Mijin Maryam) ya kaita asibitin nan sau ba adadi, amma an kasa gano inda matsalar take…”
“Tun yaushe ake na gargajiyar? Amma har yanzu babu wani sauyi, tun da dama ta ki ai sai a koma hagu, zan samu Takawa da batun kaita asibti, idan ya amince ni da kaina zan kaita, wannan karon wurin likitan ƙwaƙwalwa za mu je!”
Adda ta yi murmushi, domin duk lalacewar Sa’ad ta wani wurin ya fi ɗanta HAMMAD kyan hali, duk da shi ma Sa’ad ɗin sai a hankali.
“Abar aka sha ne?”
Kansa ya sunkuyar ƙasa yana sinsina jikinsa, dan ya san abin da take nufi, kuma ta canka dai-dai, dan bayan sashinta ya taho domin shan shisha ya jiyo ihun Maryam, dalilin da ya sa ke nan baisha ba, amma sai da Adda ta gane hakan. Wani murmuhin ta kuma, sanna ta miƙe ta bar shi a falon tana cewa.
“Ya kamata ace in an girma a san an girma…”
“Adda shisha fa ba kamar sigari ba ce!”
“Shi dai hayaƙi sunansa hayaƙi, kuma duka illa ɗaya sukewa gangar jiki… Idan mutum bai kiyaye ba dan mutuncinsa ya kiyaye dan lafiyarsa”
Kansa ya kuma sunkuyarwa, har ta ƙarasa fita daga falon bai ɗago ba.
*Unguwar Yalwawa, Dutse, Jigawa state, Nigeria.*
Wata budurwa ce zaune a tsakar gidan dake ɗauke da ɗakuna uku ginin ƙasa, tsakar gidan ta sha shara ƙwal, duk kuwa da ba siminti ko interlocks ne a tsakar gidan ba, wani irin lallausan yashi ne zube a ƙasa, wanda shatin tsintsiyar da aka share gidan da ita tai masa ƙawa cikin yammacin.
Allo ne riƙe a hannun budurwar, yayin da take rubutu bisa allon da alƙalamin dake riƙe a hannunta bayan ta dangwalo tawada dake cikin wani mazubi. Labulen ɗaya daga cikin dakunan gidan aka ɗaga, wata baƙar dattijuwa ta fito daga ɗakin, motsin saka takalmanta ne ya ja hankali budurwar nan dake rubutu a kan allo zuwa kanta.
“ZAHRA! Wai har yanzu Ruwaida bata dawo ba?”
Budurwar da aka ƙira da ZAHRA! Ta girgiza kanta, kafin ta ce.
“Har yanzu bata dawo ba Mama, ke ma kin san halin Ruwaida na shaɗanci, yanzu haka wasa ta tsaya a hanya!”
“Eh ta yanda ni kuma za a ji daɗin zubar mini da kukata a hanya ba! Kai Allah ya shirya mana”
Mama ta ƙarashe tana ɗaukar buta ta shige bayi, yayin da ita kuma Zahra ta ci gaba da rubutunta. Kamar daga sama haka wata yarinya ‘yar kimanin shekaru goma sha biyu ta faɗo gidan da gudu, abin daya sa Zahra ta tsorata ke nan, dan ba ta zayi zaton cewar Ruwaida ce ta faɗo gidan cikin irin wannan yanayin ba, dan haka ta dubeta yayin da take aje allon hannunta a ƙasa tana faɗin.
“Ke lafiya kika shigo a haka? Ko wani ne ya biyoki?”
Ruwaida da tun da ta faɗo gidan take kallon hanyar soro ta dafe ƙirji tana maida numfashi, saboda gudun da ta sha, gumi ta sharce dai-dai lokacin da Zahra ke kuma tambayarta abin da take yiwa gudu.
“Hummm! Su Farida ne fa suka biyo ni da gudu”
“Me kika Musu?” Zahra ta cilla mata tambayar, sai a lokacin Ruwaida ta samu damar aje takalmanta dake riƙe a hannu, wanda aka sha gudun fanfalaƙi dasu.
“A hanyar dawowata daga gidan Inna mai kanwa na gansu a ƙofar gidansu Fati ita da Fatin suna ɗana da keken Khalil yayan Farida, shi ne suka ce na turosu, da ina turasu sai na turasu da ƙarfi, shi ne fa suka faɗa cikin kwata…”
“Suka faɗa kwata? Ko kika jefa su kwata?”
Mama da fitowarta daga bayi ke nan ta faɗa tana aje butar dake hannunta.
“To ba-ba su suka ce na turasu da ƙarfi ba?”
Ta faɗi tana turo baki.
“Wannan kuma keda su ne, dan na san ba haƙura za su yi ba sai sun rama… Ina kukata?”
Mama ta tambaya tana miƙa hannunta alamun a bata kukar miyar da ta aiketa dan ta je ta siyo mata. Ruwaida ta yi narai-narai da ido, sannan ta soma ja da baya tana kallon Mama.
“Kin jefar a hanaya ko?”
Zahra ta tambaya tana dubanta.
“A’a ban jefar ba, da ina turasu a keken ne ledar ta fashe, shi ne-shi-shi ne kukar ta zube a ƙasa!”
“Kai! Wannan yarinya! Wannan yarinya! Allah ya shiryeki! Kuma ke da Adali (Babban yayansu) dan Wallahi ni dai ba ni da ɗari biyun siyan wata kukar, idan ya zo sai ki masa bayanin abin da ya faru, ba ruwana a ciki!”
Jin batun za a haɗata da babban yayansu Adali yasa nan take hawaye suka taru a idonta, dan ta san karonta da shi ba daɗi, da ace Saamari yayansu na biyu ne za ta iya sha a hannunsa, dan shi kam yana sake musu sosai suyi wasa da dariya, ba kamar Adali ba sai su yi wata uku ba su ga dariyarsa ba.
“Dan Allah Mama ki yi haƙuri, Wallahi ba da ganga na zubar miki kukarki a hanya ba”
Mama ta mata banza ta shige ɗakinta. Nan da nan Ruwaida ta rikice ta koma gefe ta fara kuka tun kafin zuwan Adali, dan ta san yau ba makawa sai ta doku a hannunsa. Ita ko Zahra gaba ɗaya yanda ta bi ta birkice ne yake bata dariya, ba ta hana kanta daurewa ba, dariya ta yi mai kyau, wadda ta fitar da kyakkyawar loɓar dake duka kuncinta.
“Anti Dimple dan Allah ki saka baki kar Mama ta faɗawa Zazzabi, dan Wallahi idan ya sani yau ba abinda zai hana ya dakeni”
Zahra ta kuma yin dariya tana rufe robar da take zuba tawada a ciki, sannan tace.
“Laifinki ne ai, ba kya jin Magana Ruwaida, kafin ki fita ma fa sai da Mama ta ja miki kunne a kan kar ki tsaya wasa, ki yi maza ki je ki dawo, amma da yake kunnen ƙashi gareki sai da kika tsaya wasan”
Tana gama faɗin hakan ta miƙe tsaye riƙe da allo da kuma robar tawadar da ta yi amfani dasu ta shiga ɗakin da suke kwana ita da Ruwaidan. Jim kadan ta fito daga ɗakin, hannunta rike da naira ɗari biyar sabon bugu, ta nufi wurin da Ruwaida ke zaune tana kuka ta miƙa mata.
“Ta shi ki je ki siyo wata kukar”
Ai ko da sauri ta miƙe tsaye tana share hawaye.
“To Anti Dimple… Na gode”
Zahra ta yi murmushi tana dubanta.
“A rage ƙin ji dai”
Ba ta tsaya jin abin da Zahran ke faɗi ba ta fita da gudu, Zahra ta girgiza kai tana murmushi.
“Kai Allah ya shirya Auta!”
“Wai Zahra saboda ɗaurewa ƙarya gindi kuɗi kika sake bata ta siyo wata kukar?”
Cewar Mama daga cikin ɗakinta, Zahra dake ɗauraye tukunya domin ɗora sanwa ta amsa da.
“Ya zan yi da auta? Ai ni rashin ƙiwarta yasa bana ƙin yi mata duk abin da ta naima”
“Ni na so ace kin bari Adalin ya zo ya zane mana ita… Tun da ita ba ta san ranar da za ta yi hankali ba”
Ita dai Zahra murmushi ta kuma yi, lokacin da take haɗa ita ce domin hura wuta a murhu.
“Assalamu Alaikum!”
“Wa alaikassalam”
Zahra ta amsa sallamar da aka yi cikin muryar Saamari yayanta da take bi, wanda suke ƙira da Saama, kanta ta juya ta kalli hanyar soro, inda Saaman ya shigo, sanye cikin jersey da wandonta dake nuna cewa daga filin ball yake, sai kuma takalmansa na ball ɗin da suke riƙe a hannunsa. Duk wuyan rigarsa ya jiƙe da gumi, ga kuma kayan jikinsa duk sun yi datti, alamun dai yau ball ɗin tasu ta yi daɗi. Kallon Zahra dake kallonsa ya yi, ya sakar mata murmushi sanda take masa sannu da zuwa.
“Yauwwa Dimple sannu!”
Ya ƙirata da sunan da kowa ya santa da shi a unguwarsu, ba a unguwa kaɗai ba, hatta a makaranta kowa da hakan yake ƙiranta, abu ne mawuyaci ka ji an ƙirata da Zahra ba tare da ka ji an haɗa da Dimple ba, domin ko magana take sai ka ga Dimples ɗinta biyu na loɓawa, ballantana kuma a ce ta yi dariya ko murmushi.
“Ina Mama?”
Ya tambaya yana zama a kan kujerar da ta tashi daga kai ɗazu.
“Tana ɗaki”
Ta ba shi amsa tana kallon ƙofar ɗakin Maman. A lokacin ita ma Maman da ta ji Shigowar Saaman ta ɗaga labulen ɗakinta ta fito tana dubansa.
“Ga ni, me za a bani?”
“Yanzu laifi ne dan na dawo ban ganki ba na tambaya kina ina?”
“Ai fa. Ni ke nan ban isa na je ko ina ba za a zo a fara mini bi ta da ƙulli dukan kabarin kishiya”
Ita dai Zahra murmushi kawai take tana dubansu.
“Mama ke nan… Ina Auta?”
“Yanzun nan ta tafi gidan Inna mai Kanwa siyan kuka”
Zahra amsa shi.
“Awara na gani a hanya, shi ne na tsaya na sai mata”
“Ai ko yanzu za ka ga ta dawo”
In ji Zahra. Ita ko Mama ɗakinta ta koma tana faɗin in dai Ruwaida ce ga su ga ita nan.
*Paris…*
Wata jar mota mota ƙirar Pagani Huayra BC ce ke tsuga gudu a kan titin Autoroute du nord, waƙar Runaway ce ke tashi a cikin motar, baƙin matashin dake tuƙa motar da hannu ɗaya ya kure sautin wakar, yayin da yake kallon hanya yana shafa gefen fuskarsa da hannunsa ɗaya. A gaban wani kyakkywan gini ya faka motar, dai-dai kan alayin da aka zana domin aje motoci a gefen titi. Sai da ya cire shade ɗin da suka saya ƙanun idanuwansa, kafin ya cire safety belt, ya buɗe murfin motar hakan ya bawa sanyi damar sirnanowa zuwa cikin motar. Wata kyakkyawar shopping bag dake aje a front seat ya ɗauka, sannan ya fita daga motar, ya soma ƙarewa wurin kallo sanda yake rufe motar.
Wani shago dake cikin jerin shagunan dake wurin wanda aka rubuta “MALINA BOUTIQEU” a samansa ya nufa yana gyara zaman puffer jacket ɗin dake jikinsa saboda sanyin da ake. Mai gadin ƙofar shiga ya buɗe masa da sauri har da sara masa. Dube-dube ya kama yi sanda ya shiga cikin kyakkyawan boutiqeu ɗin, wanda aka cika shi da kaya kamar kamafanin ƙera kayan sawa.
“Bonne mantinee Monsieur!” (Good morning sir)
Ɗaya daga cikin ma’aikatan wurin dake sanye da kayan da ma’aikatan boutiqeu ɗin ke sawa ta faɗi cikin harshen faransanci fuskarta ɗauke da murmushi.
“Bonne journee Claire” (Good day Claire)
Ya amsa yana dubanta, kafin ya jefa mata tambayar da ta san dole ita ce abu na gaba da zai furta.
“Ou est votre dirigeant?” (Ina Madam ɗinku?)
“Elle est dans son bureau, veuillez prendre un siege, je vais l’apperler pour vous” (Tana office ɗinta, pleace have a seat, yanzu zan ƙira maka ita)
Ya jinjina kansa yana shirin zama suka jiyo muryarta tun daga cikin office ɗinta tana dakawa wata ma’aikaciyarta tsawa.
“… Fi ce daga nan kafin na sauya miki kammani, ni na ce ki kawo min coffee mai zafi?”
Duban juna suka yi shi da Claire, sai ya fasa zama ya nufi office ɗin nata, yana daf da riske office ɗin ma’aikaciyar da ya san ita akewa tsawar ta fito tana sharar hawaye, binta ya yi da kallo, ya ga yanda ruwan coffee ɗin da aka watsa mata ya ɓata mata gaban riga. Duk da halin ƙunci da take ciki ba ta kasa gaishe shi ba, bai kai ga amsa mata ba aka sake buɗe ƙofar office din, wata farar budurwa ta leƙo tana binsu da kallo. Fara ce, kuma sosai, irin farin fararen fata, siririya ce, mai kyakkyawan dirin jiki, ga dogon baƙin gashinta da ya ji gyara yana reto a gadon bayanta, sanye take da peplum top green color, da white slit skirt, dogayen wedge booties dake ƙafafunta ne suka ƙara mata tsayi, fuskarta ta sha kwalliya kamar ‘yar tsana. Da ka ganta ka ga ‘yar kwalliya kuma ‘yar ƙwalisar zamani, kuma ba sai an faɗa ba, kallo ɗaya idan ka mata ya wadatar ka shaida ba musulma ba ce. Manon Durand ke nan, matashiyar model, kuma ‘yar kasuwa. Da harara ta bi bayan ma’aikaciyar da ta bar wurin, kafin ta kalli masoyinta, lokaci guda ta saki murmushi.
“Boobu kai ne?”
Ta ƙarashe tana nufo shi, kana ta rungume shi kaɗan tana murmushi.
“Na yi kewarka Boobu!”
Da ƙyar ya ƙaƙalo murmushi ya jefeta da shi, dan shi sam murmushi ba ya cikin abubuwan da ya saba yinsu.
“Ni ma haka… Ga rigarki nan!”
Cike da farin cikin kyautar Jersey ɗin da ya bata ta buɗe baki, sai kuma ta sa hannu ta karɓi shopping bag ɗin hannunsa, a gabansa ta fito da sabuwar jersey ta PSG (Paris Saint-Germain) Baby pink color da ratsin baki a jiki, bayan rigar ta juya tana ɗagata sama, kafin a fili ta karanta sunan da aka rubuta a bayan rigar.
“WAKILI!…”
Ta kuma kallonsa idanuwanta na ƙyallim murna, side hug ta sake masa tana cewa.
“Thank you HAMMAD!”
“The pleasure is mine Baby…”
“Mene ne wanna a fuskarka?”
Ta ta tambaya tana taba gefen fuskarsa da ta ga ya kumbura alamun an daki wurin, dan shi kam ba fari ba ne ballantana wurin ya yi ja, yanzun ma ba dan ya kumbura ba ba lallai ta gane da ciwo a wurin ba, Hammad ya ɗan shafa wurin yana girgiza mata kai.
“Is not a big deal… A training ɗinmu na yau Nicolas ya bugeni da ball!”
Manon ta haɗe rai tana matse jerseym daken hannunta.
“Ya kamata ka ɗauki mata a kan Nicolas, abin nasa ya fara wuce gona da iri, babu wanda bai san cewa duk abubuwan da yake maka da gangan yake ba”
Ganin ta fara fusata yasa Hammad ya rike hannunta dake riƙe da jersey.
“Ki kyale shi Baby, za mu ɗauki mataki a lokacin da ya dace…”
Hayaniyar da ta soma tashi a kofar shigowa ce ta ja hankulansu zuwa can.
“Anais wai waye yake tada min hayaniya a ƙofar shago ne? Sau Nawa zan ce ku daina barin mabarata na taruwa a ƙofar shagona?”
Cewar Manon a tsawace tana kallon yanda mai gadin kofar shigowa ke kokawa da wani mutum da yake son shigowa shagon, domin kofar ta glass ce, hakan ya basu damar ganin komai.
“Madam ba mabaraci ba ne, Yallaɓai Hammad yake son gani…”
Anais mataimakiyar Manom ta basu amsa, hakan yasa Marie da Hammad suka dubi juna, kafin ta kalli Anais.
“Je ki kore shi, idan ya ƙi tafiya ku ƙira ‘yan sanda!”
“To Madam!”
Anais ta amsa, kafin ta juya Hammad ya dakatar da ita.
“Dakata Anais…”
Anais ta bi umarni ta hanyar dakatawa.
“Zan gan shi”
“Amma Boobu…”
Marie dake shirin masa magana ta dakata saboda kallon da ya mata, ita kanta ta san yana ɗaga mata ƙafa, amma idan ta kai shi bango to ba sa kwashewa da daɗi.
“Ki je office ki jirani ina zuwa”
Rasa damar musa masa yasa ta juya ta nufi offfice ɗin, shi kuma ya nufi kofar dan ganin mutumin da yake son haɗuwa da shi.
__________________
_TO kamar yadda aka saba yanzu ma gani ɗauke da wani sabon labarin, da fatan shi ma za ku karɓe shi kamar sauran…_
_KAWA ZUCI paid book ne, a kan ₦400, free pages ɗina ba su da yawa, dan haka za ku iya fara biya tun daga yanzu, domin morewa karatunku cikin kwanciyar hankali._
#SalmaAhmadIsah
#Candy
#Bahadejia
#ƘawaZuci
~~~~~~~~~~~~~
*KAWA ZUCI*
*©SALMA AHMAD ISAH*
*02*
*Kauyen Kinkin, yankin kabilar Hadzabe, kusa da tafkin Eyasi, arewacin Tanzania, Africa.*
Matasan ƙabilar ta Hadzabe ne su biyar durƙushe a saman wasu ciyayi, yayin da suke fakon wata barewa da take cin ciyawa a cikin daji. Gabaki ɗaya su biyar ɗin na sanye da tufafi iri ɗaya, bayan T-shirt da wando sai wani zani da ko wannensu ya ɗaura bisa kafaɗarsa, sarƙoƙin dake wuyansu kuwa sun wuce ƙirge.
“Nikamba jittiko nabsi kokuram, shidafo” (Nikamba kai zaka fara harbinta, yanzu)
Cewar wani sirirn saurayi cikin samarin biyar da yaransu Hadzane, ga ɗaya daga cikinsu da ya ƙira da Nikamba.
Saurayin mai suna Nikamba ya jinjina kansa tare da ɗaga hannunsa na hagu dake rike da kwari, sannan ya daga na daman dake rike da kibiya, ya saita barewar da ta yi nisa a cin ciyawar da take, sai da ya tabbatar da ya saitata yadda ya kamata, kafin ya saki kibar, kan kace kwabo barewar ta faɗi ƙasa tana shure-shure, sakamakon kibiyar da Nikamba ya harba ta sameta a gefen wuyanta. A sukwane samarin suka miƙe suna ihu tare da sowa suna ta kuranta Nikamba cikin yaransu mai suna Hadzane .
***
Zaune take a bakin wata bukka, ta aje wani gajeren sashin dutse da ta ɓantaro, ta saka wani ƙashi mai kaifi tana zane bisa dutsen. Bayan wata doguwar shirt da wani dauɗaɗɗen zani da aka saƙa da zaren audiga irin saƙar kabilarsu babu komai ajikinta. Shi ma kuma zanin ba wai ɗaura shi ta yi gaba ɗaya ba, ta ɗaure shi a kafaɗa ɗaya ne kamar dai dinkin da a zamanance ake ƙira da one shoulder, duk da dauɗa da ta yi wa fatar jikinta cover ba za ka kasa gane cewa fatar jikinta baƙa ba ce.
Wani irin ƙugin yunwa cikinta ya yi, alamun yana buƙatar abinci, da sauri ta dafe cikin nata tana zare ido, ƙashin dake hannunta ta aje, sannan ta shiga sosa kanta tana kallon zanen da ta yi jikin dutsen, zanen dogayen tsaunikan da suke kewaye da ƙauyensu ne, kuma ta zanasu a siga mai ban mamaki, domin kana kallon zanen zaka gane cewa ƙwararriya ce a fagen. Dutsen ta ɗauka tana kallon abin da ta zana da hannunta, sai kuma ta yi murmushin da ya bayyanar da daffafun haƙwarenta wanda dauɗa ta musu kwalliya. Har wani kore-kore suka yi, kamar gansa kuka na rayuwa a jikinsu. Iface-ifacen da ta soma ji a cikin ƙauyen yasa ta gane cewa samarin da suka tafi farauta yau wanda suka haɗa da yayanta sun dawo.
“Nikamba?”
Ta furta sunan tana miƙewa tsaye, kafin ta falla da gudu ta bar sashen bukkar tasu, dan gidan ba a kewaye yake ba, kamar dai sauran gidajen ƙauyen. Wata mata da dauɗar dake jikinta ba zai bari ka ce ga kalar fatar jikinta ba ce ta fito daga cikin bukkar, wata T-shirt ce a jikinta, wanda alamu suka nuna cewa milkcolor ce a baya, amma yanzu ba ka isa ka tabbatar da hakan ba saboda yanda datti ya fitar da rigar daga hayyacinta, duk duniya wannan rigar ita kaɗai ce rigar da take da ita, ita ma ɗaya daga cikin ƙungiyoyin tallafi da suke zuwa ziyartar ƙauyuka irin nasu ne suka bata. Ba ma ita kaɗai ba, kusan duk kayan zamani da za ka ga a jikin wani na ƙauyen to masu kawowa tallafi ne suka ba shi. Saboda a da can baya jama’ar ƙabilar Hadzabe ba sa saka tufafi, da tafiya ta yi tafiya ne suka fara saka wasu tufafi na fatar dabobbin da suke farautowa, domin farauta na ɗaya daga cikin al’adun da ƙabilar ta shahara a kai. Sai dai duk da yanzu zamani ya fara shigarsu ba su daina ta’ammali da kayansu na al’ada ba, domin iyaka tufafinsu kawai suka sauya, har yanzu suna saka sarƙoƙi irin na al’adarsu da su da dai sauransu.
“AKIRA!”
Matar ta ambaci sunan da ƙarfi tana hangen ƙurar AKIRA da ta kusan kaiwa tsakiyar ƙauyen da gidajen cikinsa ba su fi a ƙirga ba, saboda ba su da wani yawa na ku zo mu gani.
“AKIRA nujjara batikim?” (AKIRA ba za ki dawo ba?)
Ta sake faɗi cikin harshen Hadzane da suke magana da shi a ƙauyen, amma Akira ba ta juyo ba ballantana ta dawo, ba ta taka birki ba sai da ta isa tsakiyar ƙauyen nasu, inda fadar sarkin ƙauyen nasu take, duk mutanen garin sun fito domin ganin abinda samarin ƙabilar da suka fita farauta suka farauto. Ta cikin jama’ar garin ta kutsa ta shiga gaban filin domin ganin ɗan uwanta dake kan gaba.
“Nikamba!”
Ta ambaci sunan dan uwan nata cike da farin cikin ganinsa. Nikamba dake ɗaya daga cikin samarin da suka je farautar wanda suke durƙushe gaban sarkin garin yana musu kalamin jinjina yan juyo ya kalleta, murmushi ya sakar mata tare da ɗaga mata hannu.
***
A saman dogayen tsaunikan da suka kewaye ƙauyen na Kinkin, a saman korayen ciyayin da suka lulluɓe dogayen tsaunikan, Akira ke tsugunne gaban wutar da Nikamba ya kunna, shi kuma Nikamba na zaune kusa da ita yana gasa naman da suka farauto yau, bayan an raba a fada an bawa kowa kasonsa.
Ta ɗaga kanta sama, tana kallon hasken farin watan da ya zame musu abokin raya dare, dan bayan hasken farin watan ƙauyen nasu ba ya amfana da hasken komai idan dare ya yi sai hasken wuta shi ma idan sun hura ke nan. Nikamba ya janye naman da ya kara a wuta yana gasuwa, sannan ya shiga juya shi yana kallo domin tabbatar da gasuwarsa, saitin hancinsa ya kai yana sinsinar naman, kafin ya saka yalayen hakwaransa ya yagi naman yana jinjina kai.
“Akira jo tu oje” (Akira dandana ki ji)
Ya furta cikin harshen Hadzane da aka san ƙabilar ta Hadza na amfani da shi wurin magana. Jin Akira ba ta amsa ba ballanatana ta karɓi naman da ya miƙa mata yasa ya kalleta, ta tattare gwiwoyinta ta ɗaga kanta sama tana kallon farin wata, murmushi ya yi wanda ya bayyanar da haƙwarensa da suka dafe da datti. Kafin ya saka ɗayan hannunsa ya dinguri kanta, hakan yasa ta juyo da sauri ta kalle shi.
“Guggu mukilla?” (Tunanin me kike?)
Kanta ta girgiza tana gyara zamanta, ta juyo gaba ɗaya tana fuskantarsa.
“Nikamba?”
“Hmm”
Ya amsa shi ma yana kallonta.
“Kiku nitalu an bakifu ji kuna?” (Yaushe za ka akaini cikin birni?)
Nikamba ya yi ‘yar dariya, domin ta tuna masa wani wuri da har gobe ba ya fatan komawa, wurin da rayuwa a cikin daji tare da namomin daji ta fiye masa shi sau ba adadi, wurin da aka taɓa muzanta shi, inda aka nuna masa cewa shi ba ɗaya yake da sauran ‘yan adam ba, dan kawai shi ɗan daji ne. Jin shirunsa ya yi yawa yasa Akira ta shiga jijjiga shi.
“Ni bikira Nikamba?” (Ka fada mini mana Nikamba)
Nikamba ya dubeta, yanda ta ɓata fuska kamar za ta yi kuka yasa ya sake dukan kanta.
“Rayuwarki a cikin wannan ƙauyen ta fi daɗi sama da rayuwar da ake gudanarwa a cikin gari, waɗannan mutanen da suke jin cewa sama suke da mu saboda suna amfani da kayan more rayuwa na zamani ba za su taɓa kallonki da daraja ba!…”
“A nan ɗin ana kallona da daraja ne?”
Ta tari numfashinsa kafin ya kai ƙarshe.
“Duk ranar Lahadi sai sun yi addu’a ta musanmman a kaina, kai kanka ka san zaman dole suke da ni, kowa ya tsaneni, kuma sun ce babu wanda zai taɓa sona saboda tsinuwar abar bauta ce a kaina. Nikamba a wasu lokutan ina jin da ace ni ce na samu damar da ka samu ta karatu a cikin gari da ba zan taɓa barinta na dawo cikin wannan ƙauyen ba. Domin rayuwa a nan babu marabarta da mutuwa, na sha fatawa kaina mutuwa saboda wata ƙila idan na mutu komai zai ƙare”
Nikamba ya sauƙe numfashi, sannan ya sake matsawa kusa da ƙanwarsa. Ya miƙa mata naman dake hannunsa ta kalle shi, kafin ta kalli naman ta sake kallonsa, ya mata alama da ta karɓa, ta karɓa ta soma yaga tana ci.
“Kina ji ko Akira?… Ni na je na yi rayuwa tare da sauran mutanen dake cikin gari, kuma rayuwar da na yi a cikinsu ta koyar da ni abubuwa da dama, abu mafi muhamanci da na koya daga garesu shi ne yaren da suke magana da shi a cikin Tanzania, sai kuma wata kalma mai sunan banbanci da suka taɓa faɗa mini…”
Ya ɗan yi fasali yana grigiza kansa, ita kuma Akira dake cin naman da ya bata ta tsaya tana ta kallonsa, duk duniya idan da akwai abin da take so the most bai wuce labarin yanda wasu mutane ke rayuwa a cikin gari ba, domin duk sanda masu kawo musu tallafi ko ‘yan jarida za su ziyarci ƙauyen nasu tana ɗaya daga cikin masu zuwa kallonsu, domin yanda Nikamba ke bata labarin rayuwa a ckin gari yasa ta fara sha’awar rayuwa a wurin. A tunaninta wannan wata hanya ce da za ta rabata da ƙauyen Kinkin, inda ba ta taso ta ga komai ba sama da ƙunci, damuwa, kyara da tsana. Hankalinta ta maida kan Nikamba da ya ci gaba da faɗin.
“Mts sun ce akwai banbanci tsakaninmu da su, sun ce ba za mu taɓa zama irinsu ba, sun ce mu ba kamar mutane muke ba… Akira? Idan har mu ba mutane ba ne yaya sunan hallitarmu?”
Tambayar da ya mata ta sa ta yi dariya.
“Zan so a ce wata rana na haɗu da hallitar mutane a cikin muhallinsu… Zan so ace na zama ɗaya daga cikinsu!”
“Ina fatan hakan, duk da abu ne mai wuya ki iya rayuwa a cikinsu, domin su ba sa cin abinci irin namu, tufafinmu da muke sakawa a yanzu yana kama da nasu, tun da su suka ba mu su, amma kuma sam ba sa shiga irin tamu. Na san yaren da ake a Tanzania ba zai baki wahala ba tun da na koya miki Swahili, amma idan har rayuwa ta kaiki wurin da ba nan ba zai kasance wani sabon ƙalubale ne gareki koyan yaren da suke magana da shi?”
Akira ta dube shi cikin alamar kokwanto tana faɗin.
“Da ma bayan Swahili akwai wani yaren?”
“Sai dai mu ƙirasu da yaruka… yarukan duniya sun fi a ƙirga, sannan akwai ɓabilu da ban da ban, akwai garuruwa, akwai yankuna, akwai ƙasashe, kafin kuma ita duniyar kanta…”
Nikamba ya ci gaba da bata labarin rayuwa a cikin sauran mutane, domin abu ne da ba ta sani ba, ba ma ita kaɗai ba, idan ka ɗauke Nikamba da wasu abokansa uku, babu wani rai dake ƙauyen da ya taɓa experiencing yadda rayuwa take a cikin gari. Su ma su Nikamban wata ƙungiya da ta zo daga cikin Tanzania ta ɗauki nauyin fitar da su cikin gari domin koyar da su yanda rayuwa take a cikin gari, har ta kai ga an sakasu a makaranta, tsangwama da kyara da suke samu daga wurin sauran jama’a yasa suka gudo, domin tsabar muzanci har a waya ake zuwa ana ɗaukansu ana cewa ga birran Africa, Wannan dalilin yasa zamansu a cikin garin bai yi tsayi ba suka dawo inda suka fi wayo.
*Masarautar Dutse, Jigawa State, Nigeria.*
SA’AD POV.
A hanzarce ya sauƙo daga stairs, ya shiga main falo na sashin Fulani Amarya wato mahaifiyarsa yana saka links a jikin hannun rigar shaddar dake jikinsa, a lokacin ya lura da wanzuwar mahaifiyarsa dake zaune a falon, likitarta na zaune kusa da ita tana ɗaura mata blood pressure monitor a damtsen hannunta.
“Wai da ma ba ki da lafiya Ammi?”
Ya tambaya yayin da ya ƙarasa cikin falon yana kallon Ammin tasu da alamunta suka nuna cewa ba ta da lafiya. Fulani Amarya ta ɗaga kanta ta dube shi, ya shirya tsaf cikin shigar manyan kaya na wata shadda milk color, babu aikin komai a jikin rigar kayan, sai hula da ya saka a kansa wadda aka yi wa aiki da baƙin zare.
“Tun jiya nake jin jikina babu daɗi, shi yasa na sa aka kira min Dr. dan ta dubani!”
Sa’ad ya kalli Dr. Mannira likitar masarautar, wadda ke duba matan sarki da kuma yaran masarautar.
“Ina kwana Dr”
“Lafiya ƙalau Sa’ad fatan an tashi lafiya?”
“Lafiya ƙalau… Yaya jikin nata?”
“Kai! Ni kar ka bi ka ɗaga mini hankali, jinyar tawa da ba ta kai ta kawo ba za ka naimi sakani a bakin duniya.”
Ammi ta yi saurin katse shi, sai kuma ta shiga binsa da kallo tana faɗin.
“Ina za ka je na ga ka shirya?”
“Asibiti za mu je tare da Maryam?”
Ya amsa mata kansa tsaye, take Ammi ta sauya fuska tana furta.
“Maryam?… Me za ku yi a asibitin?”
“Zan kaita ne domin a dubata?”
“Uhumm”
Kawai Ammi tace tana taɓe baki tare da ɗauke kai.
“Ni da za ku ɗauki shawarata da daga ku har Takawa kun daina ɓata lokutanku a kan wannan ciwon na Maryam, domin ko makoho ya shafa ya san cewa ciwon hauka ne yake damunta…”
Sa’ad ya miƙe tsaye yana gyara zaman hular kansa.
“Kar na ɓata lokaci da yawa, bari na tafi”
Ammi ta bi shi da ido tana jinjina kai dan ta gane cewa zancen nata ne ba ya so shi yasa ya ce hakan, har ya mata sallama ya fita daga falon ba ta sake cewa da shi komai ba. Sa’ad na fita ya hangi ƙanwarsa Aysha na dosowa sashin mahaifiyar tasu.
“Aysha”
Jin an ƙira sunanta yasa ta janye idonta daga kan wayarta da take latsawa tana tafe, ta zubesu a kan sa lokacin da ya tsaya a gabanta.
“Daga ina kuma ayawe?”
“Ka aikeni ne?”
Ta faɗi cike da tsiwa tana kallonsa, ranƙwashi mai zafi ya bata a ka yana cewa.
“To rasa kunya ɓeran tanka, ba rashin kunya na tambayeki ba, motarki za ki ara mini za mu je asibiti ni da Maryam!”
Wani irin kallo ta masa tana sosa kanta dai-dai inda ya bata ranƙwashi.
“Motata?”
“Eh mana motarki, da ta wa?
Baki ta turo gaba tana juya kai alamun ita ba za ta bashi ba.
“Ko ba za ki bayar ba ne?”
“Gaskiya Ya Sa’ad ka bi mini motata hankali, na san halinka da tuƙin ganganci, ga saurin kisan mota…”
Kwacewa keyn motar da yayi daga hannunta yasa ta bi shi da kallo, sai da ya dungure mata kai sannan ya raɓata yana faɗin.
“An jima ki sa Kasim ya je ya karɓo miki ita a gareji…”
“Ya Sa’ad mana!”
Ta fruta kamar ta yi kuka, bai ko juyo ya kalleta ba ballanata ya kulata, kai tsaye sashin Takawa ya wuce, mai girmna Alhaji Saminu Garba Wakili, sarkin Dutsen jahar Jigawa.
*
Shiru ya yi tare da sunkuyar da kansa bayan ya gama furta abin da ke bakinsa. Alhaji Saminu Wakili ya yi shiru yana kallon ɗansa da ya sunkuyar da kansa cikin ladabi irin nasa, zaune yake a saman carpet, kusa da ƙafafun mahaifin nasa, yayin da shi kuma yake zaune kan ɗaya daga cikin royal chairs ɗin da aka ƙawata hamshaƙin falon nasa da su, a hankali ya aje jaridar dake hannunsa, sannan ya sauƙe numfashi.
“Alamu sun nuna cewa ka fara nutsuwa Sa’ad!”
Alhaji Wakili da suke ƙira da Takawa ya furta yana wani gajeren murmushi, Sa’ad ya yi murmushi jin an yabe shi.
“Haƙiƙa tunanin da ka yi ya dace, a matsayinka na babba, amma akwai buƙatar mu sanar da shi Sadiq mijin Maryam, domin jin daga bakinsa…”
Sai da ya kai aya kafin Sa’ad ya sake sunkui da kansa yana furta.
“Ban raina azancinka ba Takawa, amma a ganina ba sai an gayawa Sadiq wannan batun ba, tun da shi da kansa ya dawo da ita gida domin a naima mata magani, kuma na san ko da an tambaye shi shi ma ba zai ƙi batun zuwa asibitin ba, shi da kansa ma ya sha kaita asibitin, banbancin wannan da wancan kawai shi ne mu za mu kaita ga likitan ƙwaƙwalwa ne, saɓanin shi da ya saba kaita a duba lafiyar jikinta”
Cike da ƙasaita Takawa ya saki wani murmushi yana jinjina ƙafarsa t, domin bai yi tsammanin samun wannan amsar daga Sa’ad ba.
“Shike nan Sa’adu… Mun baka dama ka kai ‘yar uwarka asibiti domin a duba lafiyarta”
“Godiya muke Ranka ya daɗe”
“Sa’adu!”
“Na’am Takawa!”
Ya amsa yana sake duƙar da kansa kamar mai shirin yin sujjada.
“Satin da wuce an ga gilmawar fitar naira dubu dari uku daga account ɗinka na banki… A sanina kai ba mata ce da kai ba, ba ka ciyar da kanka, babu nauyin wani a kanka, gidan da kake haya a Abuja ma mu ne muka kama maka, hatta da kuɗin mai da za ka zuba a mota mu ke biya maka, mun san babu nauyin kowa a kanka, me ka yi da kuɗaɗe masu nauyin waɗannan?”
Wani irin siririn yawu ne ya wuce ta maƙogwaron Sa’ad, kansa ya sake sinnewa a ƙasa yana saƙe-saƙe, domin ya rasa wata amsa zai bawa Takawa game da fitar kuɗaɗen, sanda zai cire kuɗaɗen sam ya mance cewa Takawa na lura da duk fice da shigen kuɗaɗen da yake kashewa, ba ma haka kaɗai ba, ya san da Takawa ya san duk abubuwan da yake aikatawa, hakan ma yasa ya saka ƙafa ya take burinsa da yake fatan ya cika masa shi.
Burinsa na son zamowa Manager a kamfanin saye da siyarwar motoci na ‘WAKILI MOTORS’ wanda ya kasance mallakin Takawa ne. A halin yanzu babu wanda yake kula da kamfanin, sai wani daga cikin amintattun Takawa da aka ba shi riƙon ƙwarya. Kuma hakan ya samo asali sakamon babu mai kula da kamfanin. Babban ɗa cikin ‘ya’yan Takawa wato Khabir Wakili ba shi da ra’ayin yin kasuwanci, sarauta ita ce abin da ya fi muradi.
Hakan yasa tun bayan kammala karatunsa aka ba shi muƙamin Shatima, ɗa na biyu cikin’ya’yan Takawa kuma shi ne HAMMAD, wanda ya bawa Sa’ad wattani uku a tazarar haihuwa, hakan yasa suka taso kamar sa’anni, duk da ba sa shan inuwa ɗaya. Tun tasowar Hammad ba shi da wani buri da ya wuce zama babban ɗan wasan ƙwallon ƙafa, tun da burinsa ya cika sai ya zamana kasuwanci da sarauta ba sa burge shi.
Daga shi kuma sai Sa’ad, wanda tun tasowarsa ba shi da burin da ya wuce zama Managern WAKILI MOTORS. Kasancewar cikin ‘yan uwansa maza biyu babu mai burin zama ɗan kasuwa ko shiga harkar da ta shafi kasuwanci sai kowa yake ganin daga zarar Sa’ad ɗin ya kammala karatunsa Takawa zai ɗauki ragamar kamfanin kacokam ya ba shi.
Amma sai abin ya zo da saɓanin hankalin kowa, domin bayan ya kammala karatun Takawa yace ba zai iya ɗaukan ragamar kamfaninsa ya danƙawa wanda bai san ciwon kansa ba, matsawar Sa’ad na son a ba shi ragamar kamfanin dole sai ya fara aiki daga ƙaramin mataki, kasancewar a duniya babu burin da ya ɗara na zama managern kamfanin a ran sa’ad yasa ba musu ya amince da sharaɗin Takawa a lokacin, aka naima masa aiki a wani gidan talabijin dake Abuja.
Har kawo yau Takawa na lura da duk wani takunsa, ba ya jin zai bawa Sa’ad damar jagorantar kamfaninsa matsawar bai shiga hankalinsa ba, domin ko kaɗan Sa’ad bai san zafin naiman kuɗi ba ballantana kashesu, kuma wannan dalilin yasa shi ma Takawa ya tsaya a kan ra’ayinsa.
“Magana nake maka ka yi shiru”
Takawa ya furta cikin shirun da falonsa ya ɗauka. Sa’ad ya rasa inda zai sa kansa, kuma babban kuskuren da zai tafka a duniya shi ne yi wa Takawa ƙarya, domin ya san idan har ya masa ƙarya to ba zai sake yarda da shi ba. Ya ɗan lashi lips ɗinsa da tashin hankali ya sa suka soma bushewa.
“Na… na… na… siyi tufafi… ne!”
“Ina na ka tufafin suke?… Ko estate ɗin da kake ya yi gobara ban sani ba?”
Saurin girgiza kansa ya yi yana fadin.
“A’a a’a… Na wa ne suks tsufa”
Takawa ya ɗan zamo daga kan kujerar da yake zaune kai kaɗan yana tsayar da dubansa a kan ɗansa.
“Naira dubu ɗari uku har da tamanin? A kan siyan sabbin tufafi kawai Sa’ad?”
Shi dai bai yi gigin wanke kansa ba, dan ba shi da wannan damar.
“Allah ya shiryeku… Saura kwana nawa hutun da ka ɗauka ya ƙare?”
Kansa a ƙasa yace.
“Sati biyu ne ya rage ranka ya daɗe”
Takawa ya jinjina kansa yana ɗaukan jaridar da ya aje, ya gyara zamansa kan kujerar tare da ɗora ƙafarsa ɗaya kan ɗaya ya furta.
“Na rage maka shi zuwa sati daya…”
“Amma Tak…”
“Idan ka sake cewa ƙala sai ka bar garin nan a yau ko ranka ba ya so!”
Takawa ya tari numfashinsa yana kallonsa da dattijan idanuwansa masu tsananin kwarjini, ƙarfin kwarjininsu bisa kansa yasa Sa’ad saurin sauƙe nasa kasa.
“Allah ya huci zuciyarku, tuba nake ranka ya daɗe, da fatan za a gafarceni”
Ko kallonsa Takawa bai kuma ba, jiki a sanyaye ya miƙe yana masa sallama, sannan ya fita yana jin ransa ba daɗi.
*Sashin Adda.*
Maryam, Muhibba da Adda ne zaune a dinning room suna karin kummalo, daga Adda har Muhibba gaba ɗaya hankalinsu na kan Maraym dake cin abincin kamar an mata dole. Kana kallonta za ka san cewa ba ta tare da nutsuwarta, abincin take ci, amma ba shi ne a gabanta ba.
“Yaya Maryam!”
Muhibba ta ambaci sunanta tana leƙa fuskarta, kamar wadda aka jefowa tunaninta daga sama haka ta kalleta.
“Na’am Muhibba”
“Lafiya?”
Ɗan gajeren murmushi ta yi tana aje spoon ɗin dake hannunta kafin ta kalli mahaifiyarta da ‘yar uwarta.
“Jiya da daddare na samu bacci”
Muhibba tai murmushi mai faɗi, domin a ganinsu alamun sauƙi sun fara bayyana a ciwon ‘yar uwartata, a baya kwana take idonta biyu, bata komoya lumshe idonta na dogon lokaci, don tace daga zarar ta lumshesu za ta ga wani jan ƙyalle an ɗaure shi da wasu baƙaƙen zare.
“Masha Allah, ki ce har da munshari!”
Cewar Muhibba cike da zolaya. Maryam ta kuma yin murmushi, domin yana ɗaya daga cikin ɗabi’unta da kowa ya shaideta da su.
“Ba irin wannan baccin na daɗi ba Hibba, ina kwantawa baccin na yi mafarkin wani mutum a ƙofar gidana… yana sanye da baƙaƙen kaya, kawai yana ganina ya soma ƙirana yana cewa na zo zai bani magani na warke daga wannan ciwon”
Muhibba da Adda suka dubi juna, kafin suka sake dubanta.
“Ku ma kin je ɗin?”
Muhibba ta sake tambaya tana kallonta, ta girgiza kai.
“A’a ban bi shi ba na farka daga baccin… A ganinku me hakan yake nufi Adda?”
Ta faɗa cikin sanyin muryarta tana raba idonta a kansu, Adda kasa cewa komai ta yi, kawai sai ta miƙe tsaye tana jin wani abu na mamaye zuciyarta. Tana daf da fita Sa’ad ya shigo, kallo ɗaya ya musu ya gane cewa wani abu ne ke faruwa. A ladabce ya gaishe da Adda, su ma su Maryam suka gaishe shi.
“Merry wai har yanzu ba ki shirya ba?”
Yace da Maryam yana ƙarasawa ciki, yayin da Adda ta ƙarasa ficewa.
“Ina za mu je Ya Sa’ad?”
Maryam ta tambaya tana kallonsa da mamaki.
“Ba na ce miki za mu je asibiti yau ba?”
“Assha, wallahi na manta!… Bari na je na shirya!”
——————————–
_Anya kuwa wannan jinyar ta Maryam ba da walakin ba?_
_To, ga dai Akira ma ta bijiro da nata ɓangaren, sannan ina mai muku albishir da bayan Akira ma akwai wasu sauran jaruman na nan tafe a gaba, wannan kamar sharar fage ce muke.._
_And Hey! To remind you guys, ƘAWA ZUCI paid book ne, a kan ₦ 400 kacal, idan ya zama complete kuma ₦700 ne za ku iya fara payment tun daga yanzu, domin morewa wannan tafiya mai cike da zallar abubuwan al’ajabi, soyayya sarƙaƙiya, ƙiyayya, fansa ƙunci da dai sauransu._
_Za ku iya tura kuɗinku ta wannan account details da zan runbuta 5487270431 Salma Isah Monie point, shaidar biya kuma ta 08130172702_
#SalmaAhmadIsah
#Candy
#Bahadejia
#KawaZuci