kwarton manya complete hausa novel
kwarton manya complete hausa novel
Page 1
^^Shekaruna goma sha bakwai cas a duniya. Babana yana da mata hudu da “ya “ya hamsin da bakwai.^^
Mahaifina ya kasance dan auri saki ne, bakin abinda kunne na yaji mahaifina ya auri mata ashirin da takwas.
romantic hausa novels complete
romantic hausa novels complete download
romantic hausa novels pdf
romantic hausa novels wattpad
romantic hausa novels complete document
romantic hausa novels complete wattpad
romantic hausa novels 2022
romantic hausa novels complete pdf
romantic hausa novels
romantic hausa novels facebook
romantic hausa novel audio
aymana romantic hausa novels
aymana romantic hausa novels complete
romantic hausa novels books
romantic hausa novel blogspot
romantic hausa novel blog
romantic hausa novels download
hausa romantic novels fadeela
hausa romantic novels fadeela part 2
hot romantic hausa novels complete
hot romantic hausa novels
http romantic hausa novels
romantic hausa novels list
latest romantic hausa novels
littafin romantic hausa novels
romantic hausa novels masu dadi
mr romantic hausa novels
the most romantic hausa novels
romantic hausa novels names
romantic hausa novel new
romantic novels na hausa
romantic hausa novels on wattpad
romantic hausa novel on facebook
hausa love stories on wattpad
romantic hausa novel part 1
love hausa novel page 1
wata rana romantic hausa novels
hausa love story novels
short romantic hausa novels
hausa novels romantic story
love hausa novels wattpad
romantic hausa novel zalla
zafafan romantic hausa novels
romantic hausa novels
Babana ya kasance talaka ne baya da wata sana’a wadda ta wuce “yan bige bige, ya gwanance wurin iya karya sannan kuma babu abinda kware dashi sai cin bashi………
Talaka ne amma baya saka sutura irin tasu, idan kika gansa zaki rantse da Allah yana iya kyautar naira miliyan biyar, yasan dadin kudi sosai amma a sutura baya tausawa naira.
^^°Baya da gidan zama haka kuma baya da fili ko taki daya, munyi zama a anguwanni da dama sosai wanda duk anguwar da muka sauka suna mana lakabi da gidan inna ratata, ko kuma suce gidan yawa…
Baya da aiki sai shaye shaye sannan kuma duk gidajen cacar dake garin katsina babu inda ba’asan shi ba, ya saka kansa caca wanda ake kira da nigerful, caca ce wacce take cinye tattalin arziki kuma ba kananan talakawa keyinta ba sai masu kudin gaske saboda idan har za’a buga wasan cacar mahaukatan kudine ake zubawa.
Baya bayar da abinci haka kuma babu abinda ya damesa da rashin lafiyar “ya “yansa ko matansa, idan dai caca tayi masa dadi zai siyo kwanon shinkafa daya da kuma rabin doya,
Da safe idan zai fita zai bayar da kudin kalaci ko wane daki naira talatin babu wani abinda ya damesa da yawanku.
{}{{{}}} Wata rana can wurin wasan caccarsa aka cisa, amma baya da kudin da zai biya daga cikin abinda aka saka masa, dan haka suka cire masa sutura, tun daga inda ya buga wasan har zuwa gidanmu daga shi sai gajeran wando haka ya ratso mutane saboda tsabar shi tantirine har ya iso gida.
Babu ruwansa da tarbiyar dan sa ko yar sa, shi yasa muka mayar da gidanmu kamar gidan karuwai, domin dai kowa abinda takeso shi takeyi dan babanmu yace sana’a itace tafi cancanta ga duk diyar daya haifa, ya daina biyan kudin haya yace mu zamu rika biya tunda kowa ya kawo karfi, dan haka duk yayuna suka tashi dan neman na kansu kowa ya kama sana’a amma banda ni,
Abinda yasa kuwa shine, lura da irin kyawun da Allah yayi min, karkuyi tunanin kyawu na wasa ko ku lakaba abin da shirme ni nake gaya muku haka, bawai a gidanmu ba gaba daya zuri’armu babu yarinya mai kyau da daukar hankali kamar nawa….
Ina da kyau fiye da tunanin mai tunani, ina da diri daidai irin wanda maza ke so, ina da babban kugu sannan kuma Allah ya bani baiwar iya murzasa.
Haka kuma ina da cikar kirji ina da manya idanuwa sannan ina da fari irin na fulanin asali, gaba daya zuri’armu babu mai haske na, idan na shigo taro mata sun gama wali haka kuma babu macen da zata kara tasiri harsai na bar wurin.
Ni “yar gayu ce, na iya wanka kuma na iya shafa turare gaba daya bani da tsara idan na ziyarci wuri kamshina zaiyi ta kasancewa a wurin, haka kuma idan na barsa turarena zai dade bai daina tasiri ba, sannan duk gidanmu babu mai ilimin addini na wanda na samesa ta dalilin mahaifiyata saboda nayi sauka kuma bakin gwargwado nasan hadissai amma gaba daya zuri’armu babu mai barna irin tawa, ga sani ga barna dan duk yanda nake dakai a danginmu idan har na kwallafawa raina saina bata ka tou fa lallai saina bata maka rayuwa.
Ku kasance dani a cikin littafin *KWARATA* domin jin wannan wane irin ubane ita kuma wace irin diya ce ? Kuma a cikin ita da uban waye yafi tantiranci ? Domin dai ni sana’ar da na zabawa kaina itace *KARUWANCI* danni a gani na itace sana’ar da tafi saurin kawo kudi.
Babana mahaifi shine mutum na farko daya fara budemin lasisin karuwanci, domin dai a wurin wasan cacarsa yayi kyauta da budurcina, wannan dalili yasa na zabi sana’ar karuwanci, shine ya fara ni kuma naci gaba da kasancewa da wasan domin dai masu iya magana sunce so da yawa kana koyawa mutum abu amma saiya fika kwarewa.
Abban Sojoji Hausa Novel Complete
Ni babban kamfani ce kamar yanda ake sakawa a jikin kayan masarufi ace ingrediants to nima ina da nawa ingrediants in, kamar yanda company yake sarrafa abubuwa to nima company ce mai zaman kaina.
Wannan labari a kiyayi juyashi ta ko wace siga domin yin hakan babban kuskure ne , ba kagoshi nayi ba a haka ta fadamin shi domin ina so ya zama izina ga matan aure,
{{{}}} {{{}}} {{{}}} {{{}}} {{{}}} {{{}}}
Baba da Allah ka bamu naira goma zamu cika mu siyo magi,
Ba tare daya kalleta ba yace me zakuyi da magi ? Cikin in ina tace dama kanzo ne zamu kwada,
Naira biyar ya fiddo daga cikin aljihunsa, ya mika mata tare da cewa anshi idan kin samu kudin magin ki cika ki siyomin sigari……
Mahaifiyar ta dake tsaye tana daka kulin da za dasuci kwadon tace haba mai gida idan tana da kudin zata tambaye ka ? Itama bai kalleta ba yace wannan matsalarku ce keda ita, keni yi sauri ki kawomin sigarita jiranki nake ya fada tare da shashantar da maganar matar sa.
Fa’iza mahaifiyarta ta kirata tare da cewa ina zaki samo kudin ? Bai bari Fa’izar ta bada amsa ba yace samarinta zasu bata ? Ke kike ganin bata da kudi duk yaran nan da kike kallo sun fiki kudi , ke ki hadomin da lemu mai sanyi kafin mai samomin abincin da zanci ta shigo.
Fa’iza na kokarin fita daga gidan sukaci karo da Farida a bakin kofa, da yake gidan baya da zaure wanda ke wucewa ta waje ma zai iya hango na cikin gida, gidan kuma babu kaure sai labulen buhu da aka saka a jikin kofar,
Babu sahihiyar katanga sai fasashshin buloluwa da aka jera, wanda ko yaro karami ya wuce zai hango na zaune.
Fa’iza ganin Farida yasa ta tsaya tare da cewa, Farida da Allah ko kina da kudi ki rantamin na siyowa Baba sigari da lemu, anjima idan nayi awara zan baki, babu sauran kudi a hannuna duk na kasosu kasuwa canjin daya rage kuma nakai zubin adashe kinga lokacin biyan kudin haya ya kusa.
Dan murmusawa Farida tayi tare da cewa ai tunda kika ganshi can ya mimmike kamar gawar sababi yau bashi da ko sisi, dan haka ma wallahi bazan shiga gidan ba komawa zanyi.
Tun kafin Farida ta rufe bakinta ya fara kwarara mata kira amma tayi kunnen uwar shaggu dashi ta fice abunta.
Rungume na fito da magena sanye cikin kayan islamiyata, nasha nikaf dina kayana sun dauki guga sai zabgaga kamshina nake da turarena dana siya na naira hamsin wurin masu siyar da turaren dure.
Da sauri Baba ya tashi zaune tare da cewa Mamana barka da fitowa ? Murmushi nayi tare da cewa yawwa Babana barka da hutawa,
Yawwa Mamana za’a tafi neman ilimin ? Eh Baba na fada a takaice, mikewa yayi tare da cewa muje in rakaki, wannan shine dabi’ar mahaifina duk inda zan tafi indai yana gida tou fa lallai shine zaiyi rakiya,
A kofar gida muka hadu da Fa’iza sigarin ya ansa tare da cewa ki ajiye min lemun in dawo, shigewa tayi gida tare da cewa tom.
A tafiye muke yana zukar sigarinsa hankali kwance, Baba wai har yanzu baka samu kudin da zaka siyamin keken ba ? Na tambayeshi, magen hannuna ya ansa tare da cewa machine zan siya miki uwa ta gari.
Murmushin farin ciki nayi sannan nace Allah ya bada sa’a Babana , da amin ya ansa tare damin fatan alkairi dan mun iso bakin islamiya, magena na ansa na shige shi kuma yayi gaba.
Yau inacikin farin ciki, domin dai idan har Babana yacemin zaimin abu tou fa ko zai mutu sai yayimin, yana min san da duk duniya bayayi wa kowa irinshi, yana kaunata fiye da yanda yake san kanshi, yana so ya ganni a cikin farin ciki saboda ina da sunan mahaifiyarsa.
Yau ban wani yi karatu ba, hankalina ya tafi makarantar boko, na kagara gari ya waye dan injewa kawaye na da labari mai dadi zanyi sabon machine, nidai makarantar bokon haka nan nake zuwa dan ba abinda nake ganewa kaina fanko ne , a islamiya kadai Allah ya dafamin nake ganewa, amma a boko bana gane komai. Haka nan nake zuwa na dawo,
Koda na dawo gida na kasa boye farin cikina, amma babu damar na fada, uban da ya kasa biyan kudin haya taya zan fada zai siyamin machine ? Dan haka naja bakina nayi shiru, saboda nasan idan suka ganni da machine in zasuyi tunanin kanin Mamana ne ya siya domin shine yake dauke da hidimata.
Ina cire kayan islamiya ta na matsawa Inna sai ta bani kudi na siyowa magena kifi, bazan bayar ba shine amsar data bani , tare da hadamin da cewa itama kanta gari taci , saboda haka bataci kifi ba babu wanda zata siyama kifi.
Gaskiya Inna bazan iya ba “yar madara gari taci ba, nice sheda saboda kin hana kanki kin cida magen banza, inna ta bani amsa,
Tana fadar haka ta shige daki, na dade zaune a wurin ban samu mafita ba dan duk wanda ke gidanmu haushina yakeji kamar ya sakani wuta wannan dalilin yasa bana shiga sabgar kowa,
Saida na gaji da zama na tashi a wurin ganin ban samu mafita ba, daki naje na kwantar da “yar jinjirar mage na nabar gidan dan samo mata abinda zataci, gidane babu kayan dadi daga gari sai kanzo inama amfanin talauci, shi kuma Baba ko tsoron Allah bayayi yazo gaban kowa yaci kaza dan zalinci,
Amma duk wannan masifar Maman Fa’iza hada wani ciki ina tausayin dan nan da za’a haifa domin dai zai shigo rayuwar bala’e dama ya sani yayi zamansa baizo ba.
Haka nayi ta galbaro a cikin anguwa babu tsiyar dana samo, dole na hakura na dawo gida dan lokacin sallar magrib yayi,
Har bayan sallar isha’e Baba bai dawo gida ba, tunda naga ya wuce lokacin dawowarsa na sanyawa zuciyata salama tare da ba “yar madara hakuri, tunda ko mun tsaya jiransa bige zai dawo nasan yana can ya shawu iya shawuwa, mata hudu a gida amma yana neman matan waje. Tirrr da wannan hali.
Tunani barkatai a zuciyata, ciki kuwa harda tunanin yanda zamu wayi gari ba tare da bango ya fado mana ba, dan gaba daya gidan nan ya rube ga wani irin hadari sai bakin rai yake, lallai wannan ruwan yau idan ya kwace gaskiya akwai matsala.
Allah ka tsaremu da rayuwar talauci, rufe idona nayi domin inyi bacci addu’a nayi a fili cewa ya Allah ka tsare bayinka daga mutuwar katanga, kasa in kasance rayayya, in wayi gari cikin farin ciki, Allah ka shirya Babana ya daina abunda yakeyi,
Inna ta ansamin da amin, tare da cewa Allah ya tsare gaba daya gidan, ban mata magana ba dan haushinta nakeji ta hanani kudin da zan siyowa mage na kifi, wani busashshen garinta can ta ajiyemin kuma banci ba, nasan idan naje makaranta gobe Amisty zata kawo mana shayi da biredi daga gidansu, shi yasa kafin kekena ya lalace nake saka “yar madara cikin kwandon gaban keken mu tafi tare itama ta maida miyanta.
Da tunanin shayin gidansu Amisty nayi bacci, kuma dashi na tashi, tunda na farka naji yanayin garin da sanyi nasan jiya an kwana kwarara ruwa, dan haka tun kafin na sauko daga saman katifa nace Inna halan kin tara ruwan sama ?
Na tara, ai jiya banyi bacci ba saida na tabbatar na cika komai nawa da ruwa, cikin damuwa na kara jan yagaggen zanin da nake rufa dashi tare da cewa wallahi bana san wanka da ruwan sama sai jikinka yayi ta wani sulbi kamar ka kama maciji,
Banza tayi dani bata sake cemin komai ba, tsoki nayi tare da tashi ina mai mita cewa saidai kawai inyi sallah amma wallahi banyi wanka da ruwan sama, tsakar gida na fito rike da buta, ina maijin kyankyamin shiga bayinmu,
Danni tunin duniya nayi sallama dayin fitsari daga tsugune, ko zanyi bayan gida makota nake shiga, wanka kuma dama tsakar gida nake wanke jikina baya da cikina kawai nake wanke wa a cikin bayin, ina watsa ma jikina ruwa tsikar jikina tana tashi.
Dan gajeran tsoki nayi tare da daga labilen bayin na shiga, fitsari nayi na fito, a tsakar gida na wanke cinyoyina, nayi alwallah na dawo daki.
Tun ina sallah Babana yake kirana tare da cewa uwar masu gida kiyi sauri mun makara naga har 7:30am, bana so Baba yana bina makarantar boko saboda duk kawata daya gani sai ya bita gidansu ni wannan abun yanamin ciwo.
Tsaye na ganshi a kofar dakin mu yana daura agogo sai zuba kamshi yake yasha farar shadda sai daukar ido yake, murmushi nayi a zuciyata nace Baba kenan ko ba’aba ciki ba aba kaya,
Katsemin zance zuci yayi da cewa maida hankali Mama mu tafi, mikewa nayi ba tare da nayi magana ba naci gaba da shiri, a gaggauce na shirya, tare da shafa “yar madara nace zan rago miki, Babana ya rikemin jakar makaranta muka fito daga gida…….
_Gaba daya kaine sile, dan iska domin ni kai zan kira da kwarto, kaine silar rushewar rayuwata_
Cikin farin ciki muka fito daga gida, ina fadawa Babana yabi sannu karya bata jikinsa kasancewar ruwan daya kwanta saman kasa,
Cikin jin dadi muke tafe muna fira, har mun kusa fita bakin titi ya sheko da gudu tuki na rainin hankali, tuki na gadara, tuki na wulakanci da rashin arziki, tukun da basa kaucewa mutane saidai mutane su kwauce masa, duk lokacin da zai shigo anguwar nan haka yake shigowa idan ya taka mutum ya taka banza, ko dabbobi gareka saidai ka daure abunka amma badai maganar ka sakesu ba.
Tunda na hango motar nake cewa Baba dawo ta nan, amma kafin Baba ya hayo inda nake tuni yabi takan ruwan ya wuce shaddar baba ta koma brown, iya wuya raina ya baci kuma nayi alkawari ko zai kasheni tunda har ya tabomin Babana sai naci uwarshi a safiyar nan.
Da gudu nabi motar ina watse hannuwa na yanda ake zagi dakkuwa, ina zaginsa, shima Baba biyoni yayi da gudu cikin tashin hankali, yana Mamana dawo, wanda yayi nisa bayajin kira, a kofar gidanshi da yake kiwon dokunan shi anan Baba ya sameni ya rikeni, shi kuma ya fito daga motar da bulala dorina irin wacce ake dukan dokuna da ita.
Zagin dana taho inayi shi ya jawo hankalin mutane yasa duk mutane suka fito daga gidajen su, wanda ke waje suka iso wurin da muke dan ganin kwam,
Rikeni sosai Babana yayi tare da rufemin baki saboda yasan ban iya zuciya ba, shima abokansa da sauri suka rikeshi tare da cewa *Dikko* karka daketa dan Allah yi hakuri, Babana kuma cewa yakeyi ranka ya dade kayi hakuri don Allah bata san kaine ba,
Raina baci yayi ganin kamar mahaifina yana bawa yaron da haifa hakuri, dan haka na bambare hannun Babana daga bakina nace, nasan kaine kuma na zageka, ban kara maganar ba Babana ya wanka min mari.
Tunda nake a duniya magana mai daci ko muni Baba baya fadamin ita, yana tattalin rayuwata yana kaunata amma yau saboda wani sakarai ni Babana ya daka,
Ina cikin wannan bakin cikin Baba ya bashi hakuri da taimakon abokansa ya hakura suka ja banza suka shiga gidan da yake kiwon dokuna,
A raina na dauka alkawari yanda Baba ya dakeni saboda Dikko saina rama dukana a wurinshi…… Hannuna Baba yaja muka taho yana bani hakurin marin da yayi min, wai yayi haka ne saboda Dikko kar yayimin wani abu, saida ya sakani napep sannan ya koma gida,
Cikin bacin rai na tafi sch amma tabbas Dikko sai yaci kaniyarshi..
kwarton manya complete hausa novel
P 2
Duk sanyi sanyin da akeyi saboda ruwan da aka kwana kwararawa a daren jiya hade da wani irin iska mai dadi amma Baba zufa yake kamar an tsare mai jegon da a saman gadon kara……
Cikin tashin hankali ya fara cire kayanshi yana dorawa a saman katanga, sai bakinshi dake motsawa babu wanda yakejin abinda yake fada saidai lokaci bayan lokaci yakan goge zufar data bulbulo daga jikinsa..
Ganinshi cikin wannan yanayi ya dagawa kowa hankali, gashi ya fita da farar shadda amma ya dawo da shadda kamar miyan goro,
Idan yana cikin yanayin fushi baya so kowa yayi masa magana haka kuma bayasan ganin kowa kusa dashi, mata da “ya “ya suka gane haka shi yasa babu mai shiga sabgarshi, idan yana cikin yanayin damuwa Sultana kadai ke zuwa wurinshi ta bashi hakuri kuma ya sauka saboda soyayyar dake tsakaninshi da ita,
Har na isa makaranta tunanin yi hakurin da Babana ya bawa jakin dana manta sunanshi nakeyi, sunanshi ya bacemin kwata kwata na manta sunan da aka kirashi dashi, nidai Allah yayi min jakar kwalwa, saboda ko “yan gidanmu ba dukansu nasan sunansu ba, amma na alakanta abun da yawan da muke dashi, yayin da wasu suke ganin rainin hankali ne……
Ko a aji naso na bawa Amisty labari amma na manta sunan wanda zan fada mata, Amisty itace kadai abokiyata duk a ajinmu, abinda kuwa yasa na zabeta tana da kokari sosai kuma idan ana jarabawa tana bani satar amsa,
Amisty irin yaran nan ne da idonsu ya waye tun suna cikin zanin jarintaka, bata da labari sai labarin maza, bata da aiki sai kallon B F, duk hotunan da zaka gani a cikin wayar Amisty hotunan tsiraici ne, walau nata walau na wasu, babu mai tarayya da ita saini kadai domin an dade da canfata cewar tana lesbian, nikam babu abinda ya dameni idan dai zata bani shayi nasha a tashi jarabawa ta bani satar amsa idan anyi rubutu nima tayimin a littafina shikenan banda wata damuwa.
Lokacin dana shiga aji har malami ya shiga ya fita, ga rubutu nan a saman allo, bana gane sunan subject haka nan kawai na kalli allon nadan basar tare da cewa ashe malam harya fita.
kwarton manya complete hausa novel
Da Eh kusan rabin ajin suka amsamin dan ina da masoya sosai, wasu saboda kyauna suke sona yayin da wasu kuma gashin kaina yake daukar musu hankali, okey shine abinda na fada kamar wata shegiyar baturiya dan itama okey din na dade ina koyonta a bakin Amisty dakel dai na samu ta zauna ram a cikin kaina, idan na fadi okey zakayi tunanin nasha turanci na koshi, amma babu abinda nake ganewa duk duniya sai sallolina biyar da Allah yasa na iyasu saboda nacin zuwa islamiya.
Ina zuwa mazauni Amisty tace yau ina kika baro mana Baban namu ? Wata irin faduwar gaba naji dan nasan Babana shima ba karamin tantirin dan iska bane, kodai itama Amisty Baba ya zagaya ne ?
Kinyi shiru, Amisty ta katsemin tunani na, maganata daukewa takeyi duk lokacin da ake tambayata abu, ina da nawar magana akan magana karama sai inja lokaci sosai, inayin in ina kadan wannan dalilin yasa ban cika yawan magana ba.
Dan gajeren murmushi tayi tare da matsawa, zauna tacemin tare da maida hankalinta akan allo taci gaba da kwafar note. Zama nayi tare da cewa wane malami ne ya shigo ?
Malama dai , wace malama ce ? Malamar English ! Me take koyawa na tambayi Amisty, turanci ta fadamin a takaice, murmushi nayi tare da cewa yarinya ai na gane dama dan inji idan zakiyi min karya.
Kedai kika sani, ni ciro littafinki na rubuta miki idan kin gama rainin hankalin naki, Amisty ta fada…….. Bude jakata nayi sawon wani lokaci na kasa gano littafin da Amisty tacemin, tun ina dubawa a cikin jaka har na fito da duka littafan banga littafin turanci ba, dan gajeran tsoki nayi tare da cewa Amisty inajin nabar littafin a gida gaskiya.
Daukar littafin tayi domin shine a sama, ajiyar zuciya nayi dan nima ta gane wata jar wuya ce , nace da yake jiya nayi karatu na dauka na barshi a gida ne, tou kawai tacemin bata sake magana ba,
Haka malamai mata da maza sukaci gaba da shigowa har aka tashi daga makaranta, a bakin get din makaranta na tsaya ina jiran isowar Babana , tabbas nasan zaizo duk inda yake naji yana kusa dani yana zuwa bada jimawa ba.
Banfi minti 2 ba Babana ya iso cikin wata irin kafirar mota yanzu ma yasha wanka ya murza wata irin dakekiyar shadda, sai kasaita yakeyi, murmushin jin dadi nayi domin dai Babana ya kankaro min mutunci na idan yayo wanka saboda dan gayu ne na koyi a idon duniya…..
Cikin farin ciki na isa jikin motar na bude gidan gaba na wani kame abuna, zugar kawayena ne sukayo kanshi suna gaishe shi kamar yanda suka saba idan yazo daukata,
Dan murmusawa kawai yakeyi tare da karkacewa cikin izza ya jawo wasu irin “yan dubu dubu wanda shi kanshi baisan ko nawa bane , Amisty ya mikamawa tare da cewa ku saka kati.
Yana basu bai jira godiyar da suke mishi ba yaja mota muka tafi……, ba’a hana alkairi amma inajin bakin cikin abinda yakeyi, yabar gida da yunwa yazo waje yana alkairi, gida bai koshi ba yakai ma na waje banda gori da zagin iyayenmu babu abinda akeyi a cikin anguwa cewa Babanmu yana tsaye akanmu amma duk mu tsinannin Allah ne mu , haka zaisa ayi ta shiga da buhun na, na shinkafa gero masara katin katin na madara sugar da komai na sarrafawa idon duniya sun gani haka zai biyo dare ya kwashe abinshi yaje ya siyar wannan rayuwar zalinci ce, kuma bai sani ba kanshi kawai yake yaudara,
Kasa hakuri nayi nace gaskiya Baba ni kadaina zuwa daukoni makaranta daga yau, ba tare daya kalli inda nake ba yace miyasa Mamana ? Kawai banajin dadin abinda kake ne , me nakeyi wanda bai miki dadi ba ? Wannan kudin da kake bayarwa dama gida kabawa su Inna sukaci abinci gidan kowa yunwa ta kamashi babu mai wani sahihin abinda zaici maganar daya ce kullum daga gari sai kanzo.
Dariya yayi sosai tare da cewa Mamana kenan, aisu wannan mutane basa godiyar Allah, kima daina biye musu dan kona basu kudin cefane makalewa sukeyi, duk wanda kika gani a cikinsu daga mai tumaki goma sai mai shanaye babu adadi, idan na basu kudi boyewa sukeyi su hana ku abinci, suna can sun sayi dabbobi sunkai kauyika an boye musu, idan kuma kina magana akan abinda akayi ma wani kuma wannan halin shi ake kiran da hassada idan kikaga anyi ma mutum alkairi koya samu wani abu kikaji bakin ciki a zuciyarki shima hassada ne, kuma ita hassada tana cinye kyawawan ayyuka ne kamar yanda wuta takecin karmami, kuma yawan surutu yana sa mutum ya zama sakarai , ki daina hassada kuma bakinki shiru akan fadar wasu maganganu akaina idan kinki ji kuwa jahannama tsaye ko kina san ki shiga wuta ne uwar masu gida ?
A , a Babana, amma zan fadawa su Inna gaskiya su daina irin abinda sukeyi zalinci ne, abun tausayi Baba kaji yaran nan suyi ta kukan yunwa wallahi ni har tausayinsu nakeji, kyalesu Mamana kina iya fada musu gaskiya suji haushinki barsu da halinsu…………….Maganarsa ta kare ne a daidai lokacin da muka tsaya wata majalissa.
Fita muje, fitowa mukayi daga cikin motar muka tunkari taron dandazon mazan, kallo daya zakayi musu kasan cikakkin “yan tasha ne ko wannensu ya koshi da iskanci,
Gaishe su nayi tare da matsawa daga gefe na zauna, kai bata abincin nan taci mu wuce, Babana yayi maganar a daidai lokacin da yake zama,
kwarton manya complete hausa novel
Mikomin abinci akayi a cikin ci ka yada, { take away } gyara zamana nayi tare da juyawa inda babu mutane naci gaba da aiki, daga nan bansan abinda yaci gaba da faruwa ba, saidai naji hayani tayi yawa sosai anata bawa Babana hakuri ana rirrikeshi.
Cikin tsananin bacin rai yake cewa da Allah ku sakeni wallahi saina kwakwale mashi idanuwa tunda nayi rantsuwa saina makantashi duk cikar garin katsina babu wanda ya isa ya hanani aikata abinda nayi niyya, da sauri na tashi nayi wurin Babana ina bashi hakuri,
Abokin fadan Babana yake cewa, yo kai “ya “yan wasu nawa ka batawa rayuwa, saini kawai dan na kalli diyarka nace babban lambu zaka nunamin rashin kunya, cewa nayi zan shiga ciki ? Yabawa fa kawai nayi…. Sai kawai hankali ya tashi ?
Sanin kanka ne duk kasuwar data burgeni saina ci ta hanyar shiga inyi siyayya a cikinta, duk gidan giyar daya burgeni idan na shiga saina sha kwalba biyar karanci kenan idan banda kudi, haka kuma idan naga gidan karuwai zan shiga ne inyi ta ciyayyar abinda ya sawwaka ba tare dana gajiya ba,
Ka sani nima nasan haka, tunda saina gama nake ma gwanjon mata, banyi maka shamaki da matana ba haka diyana, kenan yanzu idan nace ka bani aron Sultana mu bata dare haka zakazo bakin kofa kayi tamin babatu ?
Da sauri Babana ya rufe idanuwan shi tare da kauda kanshi gefe guda, tunda ni bansan abinda ya assasa fitinar ba, tou miye b’ata dare ? Kila shaye shayen su suke nufi,
Jinjina kai Babana yayi tare da cewa kaci sa’a Mamana tana kusa amma zan maida ita gida na dawo na nuna maka karyar barikanci, yana fadar haka yaja hannuna mukayi gaba, har muka iso gida baiyi min magana ba, saida ya tabbatar na shiga gida sannan ya koma,
Da sallama na daga buhun kofar gidanmu na shiga, gaba daya gidan suna tsakar gida uwaye da yara, yaran mazansu da matansu sun gurfana gaban wani dakekin mutum bakikkirin da cikinshi kamar ace Allah saukeshi lafiya, ni a tunani na assembly ake musu saida naga Inna na tuna ba makaranta bace.
Saida nazo daidai inda suke nayi musu sallama kamar yanda na saba, ina kokarin wuce yace ke zonan, ban kalleshi ba kuma banzo ba haka kuma ban tsaya ba naci gaba da tafiyata na kusa shiga dakinmu naji yace waccan yarinyar ta raina mutane wallahi da nayi niyar yin hakuri amma na fasa sai kun tashi kunbarmin gidana.
Hayani ta kwace bakajin maganar wani duk maganar ta koma iri daya yi hakuri , Allah ya taimake ka Allah ya kara arziki ka taimaka dan Allah karka tashemu, kaji hauka akan wannan rubabben gidan suke wani hadashi da Allah yayi hakuri, Allah ma yasa ya tashemu nayi addu’a ta a bayyane,
Zainab ce ta tashi taje wurinshi tana wani irin karye karye, sai kace karyar gidan karuwa taga maza, magana tayi mishi babu wanda yaji abinda tace, saidai suka fita da mutumin, ganin tafiyarshi yasa kowa ya tashi yaci gaba da sabgar gabanshi,
Babana da Zainab bansan yanda suka kare da mutanen su ba, haka Dikko bansan inda yake ba, dan an dauki wani lokaci banji labarin yazo anguwanmu ba,
Kwanaki da dama sun shude, rayuwa tana tafiya babu abinda yayi gaba sai ci baya ake samu, amma ni na samu ci gaba na rayuwa domin dai Babana ya siyamin sabon machine kamar yanda yayi alkawari, a cikin matanshi kuwa maman fa’iza ta samu karuwa ta aihuwa, yanzu mun zama mu hamsin da takwas cas a gidanmu,
Zaune nake a kofar dakinmu ina yanke farce na, “yar kyakkyawar magena tana shan madara, Baba ne ya siyomin madarar da yawa nake bata danni yanzu na daina tausayin “yan gidanmu tunda na gane duk munafikai ne, Kuma Babana ina gani duk safiya yana basu kudi amma bansan ko nawa bane,
Kadangare ne ya fado daga saman bango fef, yana ganin mage ya ruga, ita kuma daina shan madarar tayi tabi kadangaren da gudu, nima binta nayi ina kiran “yar madara’ dan bana so tana cin kwarika, kadangare ya rugawa mage, ni kuma nabi magen haka muka fita a guje mu dukanmu muna gudu a tsakar santa….
Shima a guje ya shigo kamar yanda ya saba, ganin yanda mutane ke rike yaransu, masu tumaki na kamawa hakan ya tabbatar min dashi dinne ya sake dawowa,
Nima kokarin kama “yar madara nakeyi, amma kafin in isa wurinta tuni dan iskan yabi ta kanta da mota ya wuce, jininta yayi tsartuwa a saman fuskata, yana wucewa na ruga na durkusa wurin magen, saida tayi miyau………. Sannan ta daina motsi, wata irin ashariya na babba tare da kurma wani irin ihu dan naji bakin cikin takata da mota da akayi.
Cikin kuka na nufi inda yake, dama ina jiran zuwan shi saboda marin da Babana yayimin ta dalilinshi, shima din jirana yakeyi saboda zagin da nayi mashi waccan ranar, kowa yana jiran kowa,
Bayan yayi parking ya fito ya zauna saman bayan mota, yauma bulalace a hannunshi yana wasa da ita, sai wani cin cingom yake sai kace karuwa…
Abokan da yazo dasu waccan ranar yauma sune ya dawo dasu, mutum biyu tsaye a gefen damarshi biyu a haggunshi daya kuma tsaye ta gabanshi ya dade da bakin glashi,
Lafiyayen kato ne mai kirar “yan dambe, singileti ce a jikinshi sai wani maski maski yakeyi kamar anyi mishi wanka da mai, dan nesa dasu na tsaya tare da cewa a cikinku waye yake tuka motar nan ? Na nuna motar da hannuna,
Nine nan, mai kirar “yan dambe ya bani amsa, sannan yaci gaba da cewa ko wani abu ya faru ne ? Saida na kalleshi sama da kasa sannan nace da Allah mi yasa ka takamin mage ? Nayi maganar cikin sanyin murya, bashi ne ba nine na taka ta, kema idan kika tsaya a hanya gobe haka zanbi ta kanki in wuce kinji ko an mata, duk shi Dikko yayi maganar.
Mai kirar “yan dambe ya anshi maganar cewa, ubangida na yanajin dadi yayi da yaga yana wulakanta talaka irinki, yana farin ciki idan ya zauna daga nan muka fara watso kayanku daga cikin kangon can, da nayi niyar murde miki wuya ki mutu , mutuwa irin ta beraye a ranar da kika wa mai gida rashin kunya, abu daya yasa ban kasheki ba kasancewar ke ba kowa bace,
Murmushi yayi tare da cewa ta hanya mafi sauki za’ayi miki hukunci, juya kisha kallo, juyawa nayi a hankali dan inga abinda yake so na gani, babu gidanmu tuni wurin ya koma fili, lokacin da na juyo babu su Dikko babu alamarsu dan tuni sun jima da tafiya daga wurin.
Salati nayi tare da tunkarar inda “yan gidanmu suke tsaye cirko cirko domin babu abinda aka bari suka fitar dashi komai an danneshi cikin kasa, sai motaci dake ta kwashe kasar wurin,
Ina zuwa kusa da Inna da zumar tambayarta abinda ya faru ta rufeni da duka tare da cewa miya hadaki da Dikko kin dauko mana fitina kin jawo mana masifa Allah kadai yasan karshen wannan masifar.
Cacai cacai kowa hayani yakemin a saman kai babu damar a dakeni Babana yaba mace rasid’i, ke kuma diyar gida kimin magana kijawa uwarki masifa, dan haka abinda kawai suke cewa miya hadani da *DIKKO ?* …………….
Pingback: Ruwan Dare Hausa Novel Complete - Hausa Novel
Pingback: Ruwan Dare Hausa Novel Complete - Hausa Novel