Matar Buri Hausa Novel Complete

Matar Buri Hausa Novel Complete

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

Tag: Matar Buri Hausa Novel Complete

*MATAN BURI*

 

*EWF*

 

*BILLY GALADANCHI*

 

Da sunan Allah mai rahama mai jinƙai.

 

01.

 

Kallon juna sukayi a daidai lokacin da Zuly ke Æ™oÆ™arin ganin cewar bata basu kunya ba amma ta kasa, Æ™afafuwan nan suntum sun kumbura tamkar an hura balan balan, ga cikin jikinta yayi Æ™asa sosai, duk kuwa irin sanyin da ake kwaÉ—awa ita sam bata jin sanyin banda gumi babu abinda ya ke tsatsafowa daga ilahirin sassan jikinta, walÆ™iya akayi mai hasken gaske, lokaci É—aya wani tsawa mai rikitarwa ya biyo bayan walÆ™iyar abinda ya haddasa wa Zuly tsananin murÉ—ewar ciki takai hannunta ta shafi Æ™asan mararta, nan take ruwa ya soma bi ta Æ™afarta farare Æ™al, sai wani abu mai yauÆ™i dake zuwa tare da jini ya fara bin Æ™afar shima, Rahma jikinta yana É“ari ta ce, “Billy gaba É—aya banaji  wannan tafiyar zata yiyu a haka, Zuly bazata iyaba ko munaso ko bamaso saimun nemi wurin raÉ“ewa saboda yanayin ta” Numfashi Billy ta sauke mai nauyi sannan ta kalli yanayin wurin, gaba É—aya zuciyarta bata kwanta da wurin ba itafa aso samune ma ace basu baro gidanba duk a yankasu su huta, ta kuma san Rahma gaskiya ta faÉ—a, kan wani acikinsu ya yi magana, an kuma zabgo wata razananniya tsawar data haddasawa Zuly zubewa akan gwiwowinta, da sauri sukayi kanta, haka suka kamata su bakwai suka nemi bishiya suka danganata dashi, kafin kace meye wannan ruwan ya kuma Æ™walewa tamkar da bakin Æ™warya!! Sai tagwayen sannu suke jere mata gasunan susu bakwai ko wacce da ciki ajikinta wanda zaikai wata bakwai, biyu daga cikinsu ma watannin cikinsu tara cifcif, Zuly dama tun wancen satin EDD É—inta ya cika haihuwar ce Allah bai kawo ba sai yanzu. Hafsa cikin takaici ta furta “Ba dubawa ko haihuwar ba ce takaici na, babu hand gloves (Safar hannu), infection zai iya shigar ta, ba kuma haihuwar ba ce tashin hankali na, abinda za’a yanka cibin da shi, kai duk ma ba wannan ba fa ana zuba wannan ruwan ya ya zamuyi da jinjiri idan ya sauka, gaba É—aya sufa basason sanyi muba suturar arziki ba bare mu sakashi a namu” Nimcy da tun É—azu batai magana ba cikin kasala ta furta, “Dubawan dai zamuyi still saboda bazamu tabbata muna muhawara ba”  Nisawa Hafsa ta yi sannan ta sunkuya ta fara dubata cikeda Æ™arfin hali, cikin jimami ta kallesu acikin hasken dabawai ya wadata bane ba ta ce, “Haihuwar ce wlh, takai kusan 5cm ma, yanzu menene abinyi, tunda ta farko ce zata iya É—aukar lokaci kafin ta haihu idan zata iya daurewa muyi gaba saimuyi gaba saboda zamanmu anan ba wani alfanu” Gyaran tsayuwa Nimcy ta yi ta shafi cikinta sannan ta ce, “Nida bana É—auke da komai zan iya goyata ai idan ma ta kasa tafiya, kuma tafiyar ma ai zai taimake ta matuÆ™a” Haka suka rarrasheta harta daure ta miÆ™e suka ci gaba da tafiyar da basuda tabbacin inda zata kaisu saboda bawai sunsan inda suke ba ne.”

See also  Inada Hujja Hausa Novels

Tafiyar kusan sa’o’u biyu acikin ruwa mai tsananin Æ™arfi zuwa wannan lokacin sun soma karkarwa da Æ™oÆ™arin neman ceto suna rungumar junansu, Zulaiha cikin rawar murya ta riÆ™o hannun Nimcy sannan cikin hasken daya mamaye sararin samaniya bayan lafawar ruwan saman ta ce, “Ni’ima dan Allah ku taimakeni kashi nakeso nayi” kallon juna sukayi itada hafsa sannan suka kalleta, sai kuma Billy ta kwantar da ita ta buÆ™aci sudan zagayeta sannan suka fara neman tayaya zasu ga meke Æ™asanta alhali ba wadatacciyar haske babu kuma wayar salula ko torchlight a hannunsu! Haka Nimcy ce wannan karon ta duba ta inda ta yi saurin É—agowa ta kalli Billy tare da cewa “Kaine ke Æ™oÆ™arin fita tana 9cm fa” A hankali ita kuwa ta furta “Innalillahi wa inna ilaihiraji’un, hasbunallahu wa ni’imal wakeel” Sun rasa wane taimakon zasu bata, gaba É—aya sai tausayinta da suke fama da shi, har zuwa sanda ta soka rirriÆ™e na kusa da ita daga haka kuma sai kan baby yazo dafe da niyyar fitowa amma hanyar tana neman matse masa, Nimcy duk iya haÆ™urinta saita soma Æ™oÆ™arin zubda Æ™walla mara misali saboda ita dama tanada rauni, tausayin kansu take gaba É—aya, sun kasance wasu irin MATAN BURI! Wanda wannan burin ne yake Æ™oÆ™arin hallakar dasu koma ta ce sun halaka, haka sukaita faman dannan saman cikinta ana matsa mararta a hankali hartayi nasarar haifar wani irin Æ™aron yaro mai girman ban mamaki mashaa Allah, zuwanshi duniya bai É“ata lokaci ba wurin cancara uwar Æ™ara saidai uwarsa ta gama galabaita, ko motsi batayi ba suna haka hasken safiya ya fara makayar su, a haka sukayi amfani da atamfa suka yaga zani suka guntule cibiyar suka rabata da uwar, sannan suka nannaÉ—e jinjirin acikin É—ankwalin uwarsa. Ganinsu a kusada wani da tafkeken kogi  ba Æ™aramin tayar da hankalinsu ya yi ba, gashi ya cika ya tumbatsa alamun ya karÉ“u a wannan daminar bakajin motsin komai sai kukan tsuntsaye, alwala sukayi dukkansu sukayi sallah É—aya bayan É—aya aruwan kogin, sannan suka dawo kan me haihuwar, inda suka fara dubata tunda haske ya wadata, Nimcy cikin takaici ta ce, “Wannan yaron ba Æ™aramar yaga yayiwa Zulaiha ba, tear É—innan har acikin Anus Billy, bamuda yanda zamuyi yanxu saidai mu yi fatan É“ullewa lafiya da kuma wuri, saboda gaskia tana neman taimakon gaggawa” Billy Shiru ta yi suka bata lokaci kusan sa’a biyu ta huta yaron sai ihun neman nono yake, a ruwan kogin suka mai wanka yanata karkarwa alamun sanyi amma ya zasuyi sannan suka É—auki hanya bayan sun tilastwa uwar ta shayar da shi abinda ba komai a nonuwan nata sai sama sama yasha, kwanansu goma a hanya mangoro kaÉ—ai suke sha, hanyar dabasusan doguwa bace saida sukayi kaukuren dosarta, hanyar dabasusan Æ™ungurmin jeji bane ba saida buri ya sa sukayi kuskuren dosarta, wannan shine gaba kura baya sayaki!.

See also  Sanadin Labarina Hausa Novels Download

Karanta Littafin Ni da Yaya Sadeeq

Jinjirin iskar safiya tana kaÉ—awa yana Æ™anÆ™ame jikinshi wuri É—aya cikeda nuna alamun jin tsananin sanyi, yama kasa buÉ—e idonsa, uwar sa dake rungume da shi wasu zafafa. Hawaye suka silalo daga idonta suka kwaranya har suna sauka akan kuncin yaron da kuma cikin bakin sa, rufe ido ta yi na wani lokaci sannan cikin tausayin yaron ta furta, “Zamana acikin matan buri bai janyomun komai ba sai taagwaron dana sani mara misaltuwa, haÆ™iÆ™a danasan duniya ta zata juya acikin daÆ™iÆ™a kaÉ—an dana roÆ™i Allah ya amshi raina kafin zuwan wannan ranar! Da akace kaina kaÉ—ai na saka a wannan fitinar bazanji komai ba akan É—an tayin jinjirin da baisan komai ba a wannan duniyar mai ruÉ—arwa! Dafa kafaÉ—unta Nimcy ta yi cikin tausayawa kansu kafin ta ce, “Zulaiha dan Allah ki sassautawa kanki da waÉ—annan kalaman marasa amfani, dukda kuskuren da dukkanmu amma babu shakka wannan abin wani yankine daga cikin Æ™addarar mu da duk dabara bazamu taÉ“a iya kauce mata ba, dan Allah karki janyowa kanki wani ciwon, ga haihuwa a wannan yanayin ga kumburi na tabbar jininki ne ya hau” A raunane ta kalleta, har lokacin muryartaba sarÆ™e tana rawa ta furta, “Yanzu Ni’ima ta ina zamubi mubar wannan wurin, kwata kwata bana ganin iyakar ruwan nan ta hanyar tsayinsu sai faÉ—insu, yaya zamu tsallaka? Ko baya zamu koma, yarona sanyi yakeji Ni’ima, kalli yanda yake karkarwa” DuÆ™ar da kai Nimcy ta yi cikeda jimami hankalin ta ya tashi fiye da tunanin, gaba É—aya ta kumbura, ga alama sambatu ta ke, ga iyayen yanka ta ko ina a jikinta, gaba É—aya kana kallon yanayin ta zaka fahimci tsantsar wuyar datake ciki, ga Æ™aunar jinjirin da takeda tabbacin idan akaci gaba da tafiya a haka bazai kai labari ba! “Inshaa babu abinda zai sameshi, bara in goyeshi da É—ankwali na kinji” Shiru sukayi na wani lokaci kafin daga bisani su yanke shawarar bin hanyar kaucewa ruwan ko zasu samu mafita.

See also  Ni da Dalibata Hausa Novels 1 & 2

 

Idan Feezo jajir sanda ya ke kallon wurin, cikin tashin hankali yake magana da Bash, “Yaran nan sun iya rainin hankali da samun wuri, su har sunga wurin guduwa a wannan Æ™ungurmin jeji? Zanga mai cetonsu duk duniya, bazamuje neman su ba, amma na tabbatar su zasu dawo neman mu, idan suka kai iyakar jejin nan babu shakka zasu nemi mafita da kansu” Bash cikin takaici ya ce, “Feez ga kuma ko waccensu mun kusa cin riba akansu, inaga wannan Ni’imar ce kawai batada ciki a cikinsu, amma ai duk sun tsufa wahalar ciki ma bazata barsu suyi nisa ba amma abina bamu saniba yaushe suka tafi? Yaufa satinmu biyu bama nan” Shiru Feezo ya yi na wani lokaci sannan a hankali ya riÆ™e wandon sa, “Ita waccen Zulaiha zata kanshe a banza, ban taÉ“a haÉ—uwa da mace mai daÉ—in ta ba, har ina shirin ajiye ta inyita sukuwa a kanta, tafiyarsu batamun zafi ba kamar inda zan sauke nauyin marata, kasan a zaria na hau mata sama da goma kafin mu dawo bamai irin taste É—inta wlh” ÆŠab murmushi Bash ya yi “Feez amma kasan ka ce mun zan hau in É—ana inji ko?” Tsaki ya ja mai sauti, “what ever dai tunda basa nan ai abu ya lalace, amma idan suka dawo saina wulaÆ™anta su wlh, tunba Zulaiha ba laifi biyu, ina fama da jarabarta kuma yau ya dace ta haihu ko?” Bash yana tsakin shima ya furta, “Yau kuwa ya dace ta haihu, idan sun raba jinjirin da uwarsa magana ta Æ™are” Shiru sukayi cikesa baÆ™in ciki sannan suka juya kawai tare da barin gidan gaba É—aya!

 

MATAN BURI!! LITTAFI MAI CIKE DA SARƘAƘIYA DA KUMA SABON SALO MAI ƘAYATARWA.

 

MOM NU’AIM.

07084161619.

 

 

 

 

 

1 thought on “Matar Buri Hausa Novel Complete”

Leave a Comment

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Scroll to Top