Romance hausa novel Wattpad
Romance hausa novel Wattpad download romantic hausa novels from wattpad….
ABINDA KE KAWO KUKAN DADI DA SAMBATU A JIMA’I
–tsananin kwadaituwa da son aiwatar da jima’in kafin wanzuwarsa
-ga da namiji: sanin makamar inda ya kamata ka taba a jikin mace, matsawar kasan hannunka to ko shakka babu bawai sai kace da ita tayi maka kuka ba, lokacin da zatayi ta kuka tana sambatu ma bazata sani ba.
-ga diya mace: ki rinka gyara farjinki sossai ta hanyar amfani da abubuwa masu kara ni’ima,Sannan ki gano lagon mijinki,inda yafi fita daga hayyacinsa a yayin jima’i,da kuma salon kwanciyar da yafi so
-tsananta wasannin jima’i kafin aiwatar da jima’in na tsawon lokaci,tabbas idan aka aiwatar da hakan to idan akazo aiwatar da jima’i za a samu koke koke da sambatu kala kala
-lailaya beli da shiga da fitar azzakari a lokaci guda anayi ana shafa kan no-no
-tsotsar kan kaciyar maigidanki
-shiga da fitar azzakari da sauri da kofi
Karin wasu littafai da zaku so
-
Matar maza 3
-
Zuciya ta
-
Mahaukaci ko boyayyen masoyi
-
Wuka a makoshi
-
Aure da haihuwa
-
Husna Hausa Novel
-
Musayar Zuciya
-
Gangar Shedan
-
Angon mata biyu
-
A gidan mu take
-
Bafulatanar Rugga
-
Matar yaro
-
Mr Bello
-
Mijin Buzuwa
-
Gidan Uncle Complete
Powered by: www.mynovels.com.ng
Karanta Littafin Kugiya
ƘUGIYA
*HASKE WRITER’S ASSO
Home of expert and perfect writers.
*TAGWAYE BIYU.*
_*SLIMZY.*_
Wattpad@Slimzy33
_&_
_*FEEDOHM.*_
Wattpad@Feedohm
*001*
Na kauda da kaina gefe guda ba tare da na ce uffan ba, ina jin wani zafi can ƙasan zuciyata, Allah shine shaida na fara gajiya da halin Gwaggo Falmata, ta ya duk lokacin da ta zo zata riƙa shiga rayuwarmu babu gaira babu dalili, ahalin ita a can garinsu babu wanda bai san iya shegen da take yi ba, ina ce ƴaƴanta taƙwas kuma babu wanda ke da uba a cikin su? Har fa ƴan biyun na ji an ce haifa wanda har gobe babu wanda ya san inda suke? Ita ma bata damu da neman su ba, kuma har gobe bata fasa iskancin ta ba, domin in dai akan kuɗine ko a tunɓur zata iya yawo! Sai mu da ta raina ta zo mana nan don WAHIDA na ɗan abinda bai taka kara ya karya ba? Ina ce tarin samari da rawar kai kawai gare ta? Amma ba’a taɓa kamata da da wani ba, shine ta ke so ta kaimu inda zata maishe mu jari? Na ja siririn tsaki a karo na goma ina aika mata da mummunan kallo, Allah ma ne ya taimake ta Wahidar bata nan, wallahi da sai ta ƙwashi kashinta a hannu, ko da ya ke duka kanwar ja ce, sak irin halinta Wahida ta ƙwaso.
Ta katse ni, ta hanyar daka min tsawa ta ce “Wai ma tukun Wahida ce ko MAHIDA? ko da yake wannan shegen halin na ki ne ya banbanta ku.” Da yake ba kowa ne ke gane mu ba, har ma gwanda ita tana iya banbance mu wasu lokuttan.
Still dai hararar na jefa mata ba tare da ta lura ba, ina mamakin yadda za’a zo a raba mutun da gidan uban shi ba tare da yana so ba, sannan a tura shi inda babu tarbiyya bare kula, inda aka fifita kuɗi akan mutunci.
“Gafara tashi ki haɗo kayan ku mu tafi, sakara da bata son arziki ba, to wallahi tallahi ko zaki mutu yau ƙafata ƙafar ki dan uban ki, nasan banda matsala da Wahida, ko kuɗin mota na turo tsaf zata iske ni.” Ta kuma daka min tsawa a karo na biyu, har da sa ƙafa ta hankaɗata tawa ƙafar gefe guda.
Na jefa mata harara na ce “Ina? Wallahi babu inda zan je Gwaggo, ba kin ce na rabu da Ibrahim ba baida ƙashin arziki? To ki je, insha Allahu ko ganina ba zai kuma ba sai dai ƙaddara, kuma dama tun fil azal malamina ne, banda wata alaƙa dashi, amma maganar na biki Nijar babu ita, ita Wahidar dake buƙata ki tafi da ita na yafe, ni kam a barni gidan ubana.” Na murguda baki cike da fitsara, ni kaina mamakin kaina ni ke, domin wallahi duk duniya baki da wanda bana ganin mutuncin shi sama da ita duk da kasancewar ta yayar babana da suke uwa ɗaya uba ɗaya.
Ta ƙwaso ashar ta ɗan ƙara mini, dama can bakinta ba tsarki ne dashi ba “Kundun kutmar ubanki, zaki tashi ne ko sai na figi wuyan babar ki.?
Da Idan aka ce dangin ubana bala’i ne bana yadda, amma a rayuwata Gwaggo falmata ta zame mani jahannamar duniya tsabar masifar ta, na zunburi baki gefe ina gungunai, Allah babu inda zan bita, ban manta wancan karon da tazo muka tafi, haka ta riƙa jera mani maza kofar gida, wai na fita na ci banza, idan ban fita ba, da bulala zata koro ni har gaban su, gashi mintina take dibarwa mutun, na iya daɗewar da zanyi da saurayi, idan lokacin ka ya ƙare ta kuma tura ni ga wani, ma’ana idan ka bada abin kirki ta daɗa maka lokacin, kai ni fa ba ma zan mance ba a ƙarshe ma har gidan wani pastor ta turani wai ya zuban ruwan albarka, silar gudowata gida kenan, ita dai gata nan rayuwar ta a talbaɗe, ba kirista ba, ba musulma ba, ga shegen bin boka sai kace aljana yar mero, ita kam Wahida ban san me take tsinta a can ba, domin ita muna zuwa Zindar ta tura ta gurin ƙawarta, ban san irin rayuwar da ta yi a can ba, sabida a can na baro ta, kuma bayan gudowata sai da ta ƙwashi watanni a can kafin ta dawo gida.
Muryar baba na ji ya taƙare sai Innarmu ya ke ma masifa, wai a gaban ta na ci mutuncin yar uwar shi ba ta ƙwaɓa mani ba, na ɗago na kalli Gwaggo falmata da ke tsaye tana matsar ƙwalla , mamaki ya kama ni, to yaushe na mata dibar albarkar da har hawaye zasu fito daga ƙwayar idon ta? Gwaggo falmata ta ƙara fashewa da kuka ta ce “Ka ga irin kallon ƙasƙancin da ke mani, shikenan Shehu banda daraja a gidan ka.”
“Innalillahi wa’inna ilaihir raju’un.” Na fada a raina, lokacin da baba ya juyo kaina yana faɗin “Uwar ki kike harara ba ita ba, sakara da bata son ciwon kanta ba, ana so a maki gata kin ƙi fahimta, sauna arziki na kiranki tsiya na hana ki, to wallahi tunda yaya tace da ke zata tafi, sai kin bita dan kan uban ki, shashasha mara wayau, uwar me kike tsinta anan ɗin? Banda yakubunar samarin da basu wuce farantin abinci a gidajen ubannin su ba, wancan tafiyar duk wata haka ta riƙa turo mini jikka 100.”
Na kalli Innar mu, na ga ko inda muke bata kallo, tana ta wanki abinta, ban san me yasa a duk lokacin da Gwaggo Falma ta gifta kara a kan mu ba, ba zata iya tsallakewa ba, ban san me yasa akan gwaggo Falma take watsi da lamurran mu, sannan kuma ban san meyasa Baba ya ke fifita Gwaggo Falma akan uwar da ta haifemu ba, na fashe da kuka na ce “Wallahi babu inda za ni.”
Gwaggo falmata ta hau salati tana faɗin “Amma Allah ya ɗebe maki albarka MAHIDA, watsatstsa, ubanki na faɗi kina faɗi, to bari in bar mamakin dibar albarkar da kika mani, ko da ya ke laifin uwar ku ce da ta ɗaure maku gindi ta nuna ɗan’uwana ba a bakin komai ya ke ba.”
Sai lokacin Innarmu ta tsame hannunta daga ruwan wanki ta ce “Yaya dan Allah ki daina sakani a shirgin ku, ga su nan, kayan su na a bakkon bisa dibaida, Allah ya sa a dawo lafiya.”
Maganar Wahida ce ta sa na ji wani sanyi ya ratsa zuciyata, ita kam idan zata iya zuwa Allah ya tsare hanya, duk da dai itama bana mata sha’awar irin waccan banzar rayuwar.
“Momcy Momcy..! Ta washe baki tare da rungume gwaggo Falmata cike da ɗokin zuwan ta.
Nan da nan yanayin gwaggo Falmata ya canza, yayin da tsantsar farin ciki ya bayyana a fuskar ta, ni kaina ba zan yaudari kaina ba, nasan ta fi ƙaunar Wahida akaina nesa ba kusa ba, kuma hakan bai rasa nasaba da yadda halayen su ya zo ɗaya, ni kam dama duk da muke ƴan biyu kamanni ne kawai suka ɓaci, amma hali kowa da na sa.
Gwaggo falma ta janye Wahida daga jikin ta, ta riƙe kafaɗarta tana kallonta daga sama har ƙasa, kafin ta murmusa ta ce “Biyun albarka, daga ina? Da dama ne?”
Wahida ta yatsina fuska tana kallona sannan ta ce “Yawon buɗe ido.”
A tare suka ƙwashe da dariya, kafin ta saki Gwaggo Falma ta matso kusa da ni tana kallon cikin ƙwayar idona, sannan ta saka yatsa ta gogen ƙwallan da suka bushe tana tambayar “Ya da kuka ƴar uwata?”
“Wai cewa ta yi sai mun tafi tare.”Na faɗa kalar tausayi.
“Then so what? Kin haɗa mana kayan mu, sannan ki saka min shower gel ɗin nan dan Allah, bana so na manta da shi.”
Na yi ƙasa da murya ina mata kallon mamaki na ce “Sai ki bita?
Ta maƙe ƙafaɗa “Ƙwarai kuwa, ga dai ƴanci na tsaya a prison? ”
Gwaggo Falmata ta ce “Yauwa ɗiyata da ta san ciwon kan ta, ita kanta da bata son zuwa sai ta je, tunda ba ɗibar naman jikinta ni ke ba.”
Da fa gaske Gwaggo Falma ta ke sai ta tafi da ni, yayin da Baba da Wahida suka ɗaure mata gindi, na nufi gurin mama ina roƙon ta dan Allah ta saka baki kar na je, amma da mamakina sai cewa ta yi “Kun fi ai kusa!”
“Mun fi kusa?” Na maimata a raina, wacce kusa ce tafi uwar da ta haife ka? Sau tari lamarin mama yana ɗaure min kai, idan ta yi wani abun sai ka rantse ba ita ta haife ni ba.
Babu yadda na iya haka na bi Gwaggo Falma muka nufi jibiya yayin da ta bawa Wahida kuɗi ta ce gobe ta shiga kasuwa ta mata siyayya ta iske ta, Da ga jibia muka hau machine sabida tsaro muka je dan isa, a can ne muka hau mota sai maradi, cikin lokuttan tafiyar nan babu mai tanka wani, tana jin haushin nace ba zan biyo ta ba, nima ina jin haushin ta taho dani zata canzan mani rayuwa, gashi ina jin Baba na rantsuwar ya bata mu kyauta, idan kuma na kuskura na gudu irin wancan in nemi wani uban bani ba, na ja siririn tsaki, lokacin da aka tsaida motar mu ana tambayar passport, ban san me ta faɗa masu da faransa ba, sai na ga suna dariya har da direban, sannan ya ja motar kafin ya juyo ya ce mani “Yan mata da dama ne.?
Na watsa mashi harara na ja tsaki “A’a da haggu.”
Gwaggo Falma ta amshe da “Rabu da sakara girman jiki ne.”
Wani buzu dake kusa dani ya ƙara matsowa jikina, ya kai hannu ya zunguri nonona da gangan tare da kauda kai yana kallon waje, ganin bance komai ba ya bashi ƙarfin guiwar saka hannu ya matsa mani nono ba tare da kowa ya lura ba, raina ya ɓaci na koɗa mashi mari ina faɗin “Idan ka kara taba ni sai na ci mutuncin ka.”
Gwaggo Falma ta ce “Ke lahiya? Meye haka, kina hauka ne? Dan Allah yi haƙuri.”
Na ce “Ya yi hakuri? Idan ka hakura Allah ya tsine maka albarka, banza ɗan iska, ƙirjina ya taba fa.? Nan da idona ya cika da ƙwalla.
Direba ya ƙwashe da dariya ya ce “Ya gansu chass ya kasa haƙura.”
Buzu dai baice komai ba, ya sha mur ya cigaba da kallon waje kamar ba shi na mara ba, Gwaggo Falma ta watsa min harara ta ce “Idan ya taɓa nononki sai me? Ban san shegantaka, mu nan ba komai ba ne.”
Cikina cike yake da rashin kunya sabida takaicin abinda ya min, don haka na ce “Ai da yake garin yan iska ne.” Ta taso mini da masifa na zakalkale na mata rashin kunya, yan motar na ta bata haƙuri tana ɗebe mini albarka, to dama wace albarka zan samu a zama da ita? Babu sai dai kayan takaici.
Gari ya fara duhu muka shiga maradi, muka hau adaidata dala 160 ta kaimu gidanta dake kusa da ekol, ƙaton gida mai gate, ginin zamani komai ciki, dama na san ɗakin da baki ke sauka, don haka na ja jikkata na kai can, na shiga toilet na yi alwala na fito na shinfida dankwalina na kabbara sallah, bayan na gama ta shigo ta miko mani wayar ta tace “Lalubo mini lambar Samuel.” Da yake idan dare yayi haske na ma idonta yawa.
Na amsa da “Sim one ko two.?
Ta ce “Na farko.” Na kira na miƙa mata ina hammar yunwa, ta samu bakin gado ta zauna ta saka wayar a sifika, ringing ɗaya ya ɗauka “Hello mama.”
Da yake da mama naji dukkan mutane na kiran ta. Gwaggo falma ta ce “Kana ina.?
Ya ce “Ina gida.”
Ta ce “To na dawo, ka zo ka raka Mahee gidan John ta ƙwana acan, nima ba a gidan zan ƙwana ba, kuma ka san yadda suke da kare.”
Ban san wace Mahee take nufi ba, sai da na ga ta juyo tana kallona ta ce “Mahee, za’a zo a kaiki gidan John ki ƙwana.”
Na fara dube duben inda zan ga Mahee, ta daka mani tsawa “Da ke nike? Ko Mahida kike so na kira ki? Nan ba Najeriya ba ne, daga yau sunan ki Mahee.”
Na ƙwashe da dariya ina nuna kai na “Ni Mahee? Ikon Allah to me ya ci Mahida.?
Ta ce “Ƙauyanci.”
Na tabe baki na ce “Na ji amma babu gidan da zanje in ƙwana.”
Ta ce “Las, sai Samuel ya taya ki ƙwana shikenan kin ga kun ƙara fahimtar juna, ki saki jikin ki yaron kirki ne, ubanshi duwan ne zaki samu arziki, dama don ya ganki ya sa na kira shi ki ƙulla alaƙa.”
Kafin na bata amsa ta sake kiran shi ta ce “Yau ango kake, yar tawa anan zata ƙwana, sai ka yi shirin tararta, ka taho da abin taɓawa.”
Baki buɗe nake kallon ta har ta yanke wayar ta jefa mani harara tana tambayar “Lafiya.?
Na ce “Na ji….!
Ta katse ni “Dakata kar ki mini dogon surutu, zan baki maganin hana ciki, kuma mu anan ko da kin haihu arziki ne, babu shege kamar ku can Nijeriya, mu anan ɗan soyayya ake cewa, ko dan saurayi.”
ƘUGIYA na kuɗi ne normal group 500 page ɗaya kullun, sai VIP 700 pages biyu inshaAllah, aƙwai discount ga early bird, ku yi maza kar a yi babu ku.
Leave a Comment