Sirrin Rike Miji

Zaman Aure Sai Hakuri Sirrin Mata

Zaman Aure Sai Hakuri Sirrin Mata

Kina matar aure sai ki xauna gida kaca_kaca komai ba kyan gani , daki a hargitse , tsakat gida a komai ya Kama gurin sa y xauna , tukunya sai ta kauna ba a wanke taba Sai xa’ayi wani girki xa’a wanke…..hmmmmm!! Da anyi magana tace wai Ni mace ce! Plx Dan Allah mu gyara mumah wlh xamuji Dadi sse domin in ka tsaftace ko’ inah Kai kanka xakaji Dadi ballantana koma mijin ki. Allah yasa mudace
By @dmin aysher Muhammad
*SIRRIN MU *
Idan kaga wata matar taci kwalliya xata fita anguwa Kai kace haka take a gidan ta
Baxa’a saka was mai gida Kaya ba Sai xa’a fita , kuma a hakan kike tunanin ya karu Miki wani
Baxa kisa Masa ai ba amfanin siya tunda na waje kikewa kwalliyar ,
Ba dole kuwa yagani a waje ya kalaba tunda a gida ba yasamu,
Kinga in yashiga halaka keki ka xama sanadi kenan , kuma daga karshe ba Wanda xai kaiki danssani.
Allah yasa mudace
By @dmin aysher Muhammad

 Zaman Aure Sai Hakuri Sirrin Mata Kashi na 1

 

“Idan namiji bai ji daɗin aure ba zaiyi tunanin kara mata ne don ya samu jin daɗi. Idan kuma ya ji daɗi zai yi tunanin ƙarawa don ya ƙara jin daɗi. Mata ku yi hakuri. Ƙarin aure ɗabi’a ce a cikin mazajen mu

IDAN KIN GANE SAIKI ZAUNA LFY!

Haka ne tabbas, kuma duk mace mai son Allah da Manzan Sa zata yi hakuri, sai ta ɗauki namiji abokin rayuwa, aboki kuma yana kuskure yana son rai sannan baya da tabbas, Allah kaɗai yake da tabbas, mai zai hana muyi hakuri mu mata

 

DA MUN HUTA DA ZAFIN KISHI

 

A lokacin da kika ɗauki son duniya kika tattara kika ɗora akan namiji tabbas, zaki halakar da rayuwar ki, domin  Allah kaɗai Ya cancanta da wannan soyayyar.

 

 

 

 

 

 

IDAN KUNYI TUNA NI

 

A lokacin da kika ɗauka sai kina ɗasawa da namiji zaki kyautata masa, da kuma biyayyar aure Hakika kina wasa da  shiga aljannar ki

 

WANNAN HAKA YAKE

 

A lokacin da kike banzatar da mijinki dan ya ɓata miki rai koh ya ƙaro kishiya zaki yi da na sani marar adadi, domin ba shine ya baiwa kansa iznin ƙarin aure ba, Allah ya umarce shi

INA MAFITA

 

A lokacin da kika ɗauka duk biyayya, kyautatawa, ihsani,  kyautatawa, farantawa, sadaukarwa da miƙa wuya da kike yi ga mijin ki domin shi kike yi ai kuwa sai in baza ki cigaba da yi ba, idan kuma baki yi ba Allah zai bashi dubun ki masu yi fiye da abinda kike masa, muddin dai mai riƙo da gaskiya ne.

 

BABU JA AKAN HAKA

 

A lokacin da kike bibiyar sahu da ƙwaƙƙwafin miji don kisan abinda yake ciki koh abinda yake akai, koh wata alaƙar da yake da wasu matan waje, lallai kuwa zaki samarwa kanki hawan jini. Domin a ƙarshen zamani namiji ɗaya tal na iya jiɓantar al’amurran mata masu yawa

 

WANNAN HAKA YAKE

 

Amma abinda ya fiye maki alkhairi shine dai, ki so namiji tsaka – tsaki domin zai iya canja maki nan gaba, sannan ki rika masa biyayya da kyautatawa domin Allah; ta hakan baza ki gajiya ba, kuma kada ki sanya shi a ran ki, domin rayuwa ɗaya kike da ita koh yau kika mutu, gobe wata zai auro,ya ci kaza ya sha maltina

Leave a Comment

error: Content is protected !!