Wayyo Dadi Hausa Novel
HUZA’IYYA Wayyo Dadi Hausa Novel
NA KSS.
NA KUƊI NE MAI BUƘATARSHI TA YIMIN MAGANA TA WANNAN LAMBAR..
WhatsApp only
FREE P.1.
DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAI JIN ƘAI, ALLAH INA ROƘONKA TARE DA KAMUN ƘAFA DA ISASSUN DAKA HALITTA BA KAMAR MUHAMMADUR’RASULULLAHI SALLALLAHU ALAIHI WASALLAMA ALLAH KASA YADDA NA FARA WANNAN LABARI LAFIYA KASANYA NA GAMASHI CIKIN ƘOSHIN LAFIYA.ALLAH KA BANI IKON RUBUTA DAI-DAI DA AIKI DASHI,ALLAH KA HANENI RUBUTA ALFASHA ALLAH KA SANYA AL’UMMA SU DINGAMIN ADDU’A TA GARI ADUK SANDA SUKA KARANTA LABARINA BASUYI KAICO GA ALƘALAMINA BA.TSIRA DA AMINCI SU TABBATA GA RASULULLAHI ANNABIN FARKO DA ƘARSHE WANDA BA’AI KAMARSA BA, BA KUMA ZA’AYI BA,ALLAH KAYI MASA SALATAI ADADIN DUKKAN ABINDA KA HALITTA WANDA YAKE CIKIN DUNIYA DA LAHIRA BAKI ÆŠAYA.ALLAH KA BARMU DA SOYAYYARSA HAR ƘARSHEN ƘARSHEN RAYUWA…
@@@@@@@
HAJIYA LAMI ce atsaye akan wata matashiyar mace me kimanin shekaru talatin da biyu(32) wadda ta ke fara tas kamar atsaga jini ya fito tana kwance akan wata tabarma tana bacci wanda daka ga yadda takeyinsa zaka fuskanci awahale ta ke yinsa ga tsowon cikin da ke jikinta kamar an kifa Æ™warya.Tsaye ta ke kanta tana kiran sunanta tare da zungurinta da Æ™afa tana faÉ—in…
” HUZA’IYYA..! Ke Huza’iyya tashi nan zan fita”
Karin wasu littafai da zaku so
-
Matar maza uku Hausa Novel
-
Doctor Eshaat Hausa Novel
-
Mahaukaci ko boyayyen masoyi
-
Wuka a makoshi Hausa Novel
-
Aure da haihuwa Hausa Novel
-
Husna Hausa Novel
-
Musayar Zuciya Hausa Novel
-
Gangar Shedan Hausa Novel
-
Angon mata biyu Hausa Novel
-
A gidan mu take Hausa Novel
-
Bafulatanar Rugga Hausa Novel
-
Matar yaro Hausa Novel
-
Mr Bello Hausa Novel
-
Mijin Buzuwa Hausa Novels
-
Gidan Uncle Complete Hausa Novel
-
Yar aiki return Hausa Novel
-
Raggon namiji Hausa Novel
-
Uncle Datti Jikina yake so Hausa Novel
-
Fataucin Mata Hausa Novel
-
Juhud Hausa Novels Complete
-
Moon Hausa Novels PdfÂ
-
Yarima Ashman Hausa Novel
-
Bandirawo Hausa Novel
-
Matar makaho Hausa Novel
Powered by: www.mynovels.com.ng
A razane ta farka tare da saurin dafe cikinta da takejin kamar zai huda cikin ya fito bata gama dabarar tashi zaune ba taji maganar Hajiyar akanta tana ce mata…
” Ki maza ki tashi daga wannan baccin da kika tsira na raini da nuna isa kifito tsakar gida akwai icce ankawomin da niÆ™aƙƙiyar dawa ki mulluÆ™amin tuwon dawa mai kyauma da miyar É—anyar kuÉ“ewa banson miyar daka gurzata zakiyi Æ™ananu kiyimin girki mai kyau,sannan kiyi da yawa saboda sadaka za’ayi da shi…”
Harta fice daga É—akin ta juyo da baya tare da faÉ—in…
​
Name: | [KYAWUNA JARABTA TA] |
---|---|
File Type: | Download Novels as .TXT .PDF .DOC .HTML |
Uploaded By: | www.mynovels.com.ng |
Category: | Hausa Novels Documents |
Tags: | Hausa Novels Documents Hausa Novels Books Complete Hausa Novels Hausa Novels Hausa Novel Romantic Hausa Novels Sabbin littafan hausa |
Novel Price: | Free |
Last Modified: | June, 2022 |
Idan kuna bukatar Audio Novels se shiga anan ku danna mana Subscribe
Akwai novels maras adadi a manhajar mu ta Android wadda zaku iya saukewa anan…
Domin samun littafai a saukake su shiga group namu na Telegram
Bata jira ta bakinta ba ta fice da jakarta ahannu yarinya Æ´ar kimanin shekara goma sha biyu(12)tana biye da ita abaya.
YunÆ™urawa tayi tare da lallaÉ“a jikinta ta fito daga É—akin da take tare da zaman dirshan aÆ™asa ta sanya buta agabanta ahaka tayi alwalar tare da zira hijabinta ta miÆ™e Æ™afafuwanta ta gabatar da sallar azahar tare da É—aga hannuwanta tanakai kukanta ga Ubangiji mai ji da ganin al’amuran da bayinsa suke aikatawa ahaka harta É—auki lokaci sannan ta lallaÉ“a daÆ™yar ta fito tsakar gidan tare da leÆ™awa kitchen É—insu ta sauke idanuwanta akan tafkeken gas É—in da suke girki da shi yayin da buhun gawayi yake ajje awani É—an lungu dake kitchen É—in wanda suke amfani da shi lokaci zuwa lokaci idan gas ya Æ™aremusu base sunyi jira har lokacin da za’a É—uro ba,gefen gawayin ta kalla inda tayi arba da iccen da akamata umarnin aiki da shi ta ke taji wasu siraran hawaye suna sakkowa kan fuskarta masu tsananin É—umi,jan jikinta tayi ta jingina jikin bango dan ji take yi Æ™afafunta suna rawa kaÉ—an-kaÉ—an,sakin jikinta tayi ta zauna sosai dan bazata iya jure tsayuwar ba duk jikinnata yayi tsami kamar wadda aka daka.Innalillahi wa’inna ilaihi raji’un! Ta faÉ—a tare da dafa kanta da hannu bibbiyu tahau surutai kamar wata zautacciya…
” Nikam shekara nawa ne zanyi arayuwata nakoma ga mahaliccina?,tsawon shekarun da nayi na rayu cikin matsalolin rayuwa da baÆ™in ciki daga wannan se wannan shin me nayiwa rayuwa haka ne…Nikam wai haka duk wani maraya yake fuskantar rayuwar Æ™unci da ruÉ—ani? Me zanyi na samu sauÆ™in…”
Maganar ce ta katse mata lokacin kuka yaci Æ™arfinta zufa se tsattsafowa takeyi tako ina na jikinta tanajin yadda Æ™irjinta yayi mata nauyi cikintama ya dunÆ™ule waje guda gaba É—aya jikinta ya saki banda ajiyar zuciya ba abinda ta ke iya saukewa…
Sannu ahankali ta ke aikin afarfajiyar gidan dake babu murhu se wasu manyan duwatsu da aka kakkare tukunyar da su,tana yi tana riÆ™e cikinta da takejin yana wani irin juyi kamar ranar haihuwarsa ta tsaya,ahaka cikin galabaita harta Æ™arasa tuwon ta kwashe sannan ta sake miÆ™e Æ™afafuwanta awajan tana gyara tukunyar miyar da ta daÉ—e da dawuwa tafara gurza kuÉ“ewar da riÆ™aƙƙu sunfi yawa acikinta,sannu ahankali take juya miyar da ta fara kumfa inda bayan ta dai-daita ta É—ebo ruwa da nufin ta É—ora akan garwashin itacen bata ankaraba seji tayi wani irin zugi da raÉ—aÉ—i sun ziyarceta acikin lokaci Æ™alilan wanda hakan ya haifar mata sakin ruwan da cikin rashin sa’a tukunyar ruwan ta suÉ“uce tayi kan tukunyar miya wanda hakan ya haifar da zubar mafi yawansa cikin miya ya nemi waje yayi zamansa a ciki.”Innalillahi wa’inna ilaihi raji’un,ya rabbi ya Rabb! Allah kai kasan me kake nufi da ni da wannan ibtila’in da ya sameni awannan lokacin Allah ka shiga lamurana dan arziÆ™in tsaftataccen MARAYA Annabinka ka cire ni acikin ruÉ—anin rayuwa”, Ta Æ™arasa faÉ—i tare da sanya gwuiwoyinta aÆ™asa ita tama rasa tsakanin kuka da ihu wanne zatayi itadai tabi ta zurawa miyar da ruwa ya fita yawa idanu sai Æ™ifÆ™iftasu take yi kamar mara gaskiya.
“Munafuka Azzaluma macuciya kalar cutar da kikamin kenan yau? wato jiya kinyimin É—anyen tuwo yau kuma kinyimin miyar ruwa to wallahi kinyi a abincinki kuma yau tsakar gida zaki kwana sauraye su miki hukuncin zaluncin da kikayimini…
Yau naga makirar yarinya wato so kikeyi duk dukiyar da ubanki ya mutu ya bari sekin Æ™arar da ita da rashin tattalinki ko?,to wallahi Æ™arya kikeyi baki isaba dan nima É—an uwana ne kingama cin rabonki tunda sau huÉ—u ina aurar da ke kina dawomin to wallahi wahala yanzu kika farata agidannan dan bazan taÉ“a É—aukar raini ba da mutunci na kisa araina ni,a’a bazata saÉ“u ba bindiga a ruwa tunda abinda kika zaÉ“awa kanki kenan seki zauna kowane miji kice ya zalunceki nan kwa ba’asan kece baÆ™ar azzaluma ba”
HAJIYA LAMI tana kaiwa nan a zancenta tasanya ƙafa ta harbeta tare da hayewa benenta tana ci gaba da sababinta.
“Wallahi yanzu Æ™waÆ™walwata ta buÉ—e na gane duk wani tuggunki yanzu sam bazan ragamiki ba dan ba ke kaÉ—ai aka rubutawa Æ™addara ba da har zakiyi aure har huÉ—u kifito kice baki dace ba kowa yaji wannan ma yasan zancen banza ne,inba haka ba ni yara na nawa amma ko yaji basu taÉ“a yi ba se ke dan kinga dukiyar ubanki ce kullum seki kaso aure kizo muna gugar kafaÉ—a to wallahi angama idan zaki fita ki nemo inba haka ba keda abinci sedai kiga ana ci agidannan badai nawa,banza shashasha gaki da kyau da komai amma bazaki nemi kuÉ—i da kyanki ba sedai ki zauna kina wahalar banza to kizauna yunwa ma ta isheki banza sakarya…!”
Dafe kanta HUZA’IYYA tayi da duka hannuwanta guda biyu wanda ta ke jinsa kamar zai tsage saboda masifa,innalillahi wa’inna ilaihi raji’un! kaÉ—ai bakinta ke iya ambata dan gabaki É—ayanta jinta ta ke kamar ba ita ba,daÆ™yar taja Æ™afarta ta shiga É—akin yaran da ta ke kwana domin ta zura hijabinta tayi sallah sai kuma zancen wankin uniformÉ—in auta ya faÉ—o mata…
ƳAR GATAN MAMA.