Yayi min illa Hausa Novel Complete
YAYI MIN ILLA Page One
*NOBLE WRITERS ASSOCIATION✍🏼*
°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°
“`Gidan karamci, rubutu don ci gaban al’umma, mu gudu tare mu tsira tare, alÆ™alaminmu Æ´ancinmu.“`
°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°
*https://www.facebook.com/106494781436168/*
“`Marubuciyar
Ramin Mugunta
Fulanin Tashi paid book 1&2
Baƙar Ashana
Namiji rigar Æ™aya 👉( Yayi min illa) “`
_Alhamdulil Lah! Allah na gode maka da ka bani ikon fara rubutun littafin nan lafiya Allah ka bani ikon gamawa lafiya ka yafemin kura-kuraina ka hane ni da rubuta abinda ya saɓa maka Amin_
Labari da rubutuwa.
*Ruƙaiya Abubakar Umar (Waheedat)*
Shafi na farko.
_SAHIH INTERNATIONAL SCHOOL na’ibi street goron namaye road U/mu’azu kaduna._
Yau monday tushen aiki kenan, sauri sosai ni keyi kamar zan tashi sama saboda lattin da nayi burina É—aya shine be wuce in ganni a makaranta saboda na makara yau sosai, gashi muna da nisa tsakaninmu da unguwar mu’azu kuma lokuta da dama bama samun ababen hawa da safe.
Karin wasu littafai da zaku so
-
Matar maza uku Hausa Novel
-
Doctor Eshaat Hausa Novel
-
Mahaukaci ko boyayyen masoyi
-
Wuka a makoshi Hausa Novel
-
Aure da haihuwa Hausa Novel
-
Husna Hausa Novel
-
Musayar Zuciya Hausa Novel
-
Gangar Shedan Hausa Novel
-
Angon mata biyu Hausa Novel
-
A gidan mu take Hausa Novel
-
Bafulatanar Rugga Hausa Novel
-
Matar yaro Hausa Novel
-
Mr Bello Hausa Novel
-
Mijin Buzuwa Hausa Novels
-
Gidan Uncle Complete Hausa Novel
-
Yar aiki return Hausa Novel
-
Raggon namiji Hausa Novel
-
Uncle Datti Jikina yake so Hausa Novel
-
Fataucin Mata Hausa Novel
-
Juhud Hausa Novels Complete
-
Moon Hausa Novels PdfÂ
-
Yarima Ashman Hausa Novel
-
Bandirawo Hausa Novel
-
Matar makaho Hausa Novel
Powered by: www.mynovels.com.ng
cikin lokaci Æ™anÆ™ani na isa makaranta amma duk da haka nayi latti, kai tsaye ajina na wuce na zauna tare da gabatar da abinda zan fara (ma’ana darasin ranar) ana haka se ga É—aya daga cikin malaman makarantar wadda take É—aukata matsayin Æ™awarta yayinda ni kuma ban cika shigewa mutane ba nafi so nayi rayuwata ni kaÉ—ai bansan rayuwar ance kace shiyasa nafi so na zauna matsayina ba tare da na shiga haƙƙin wani/wata ba, gaisawa mu kayi kamar yadda muka saba tukum ta koma ajinta.
Bayan an tashi tara se gata ta kuma shigowa ajina nan muka dasa labari saboda ita tana da son mutane da kuma son surutu sosai tun ina amsa mata sama-sama harya zamo muna zama muyi hira na lokaci kamin mu rabu, ana haka cikin hirar ne take faÉ—amin ai shugaban makarantar yace yana so na, É—aya daga cikin malaman makarantar tace masa an min miji babu yadda za’a yi a nemi aure kan aure.
Cikin rashin jindaɗi ƙaryar da malamar ta min nace.
“Lalle Anty Rahama, Ni kam wa ya faÉ—a mata an min miji kuwa? saboda ban taÉ“a kalan wannan hirar da wani ba”,
Galala Anty Zaliha ta sake baki tana kallona haÉ—i da faÉ—in.
“Yanzu dama Æ™arya tayi masa kenan? lalle idan yaji wannan labarin baze ji daÉ—i ba, saboda yadda ya nuna yama sonki tun farkon zuwanki makarantar nan amma tace masa an miki miji, yanzu haka maganar da ake Ashirin da bakwai ga watan nan zeyyi aure, dun da ta faÉ—a mishi an miki miji wallahi wata Æ™awar matarsa da ta rasu ta haÉ—ashi da Æ™anwarta”,
dariya kawai nayi nace kice zamu sha biki kenan? ɗaga kai kawai tayi itama tana dariya tukum ta miƙe ta shige ajinta saboda hango shugaban makarantar da tayi.
ɓangarena kuwa ba ƙaramin haushi ƙaryar da tamin na an min miji shine ya bani haushi, lalle ma matar yo ita ɗauka take ko da yazo da kansa yace yana so na zan amince masa ne? tab Allah ya kyauta nace tukum na ci gaba da abinda nikeyi har zuwa sanda aka tashi.
Ina komawa gida na ci gaba da harkokina kamar yadda na saba, saboda ni ko da yaushe waya ce Æ™awata kuma abar hirata sau da dama bana iya barin wayata ta huta, mamana kuwa ba Æ™aramin damuwa take ba in taga na É—auki waya ina daddanawa musanman taga ina dariya nan da nan ranta ze É“aci tayi tamin faÉ—a, ni kuma É“angarena mafi akasarin lokuta ina harkar rubutuna ne, wani lokacin kuma in buÉ—e data inta hira da Æ™awayena marubuta musanman wata Æ´ar nijar marubuciya me suna Chafa’atu ina matuÆ™ar jindaÉ—in hirar da nike da ita, se kuma in leÆ™a face book inta kallon abubuwan dariya kamar me.
haka dai nike rayuwata wayata ita ce ƙawata dan in bani da class sai in shafe a wanni da yawa ina amfani da ita, sannan rayuwata kyalkyalin duniya be dameni ba,
Wash! Na jima banyi typing ba, amma in sha Allah zan ci gaba zuwa dare
YA YI MIN ILLA
*NOBLE WRITERS ASSOCIATION✍🏼*
°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°
“`Gidan karamci, rubutu don ci gaban al’umma, mu gudu tare mu tsira tare, alÆ™alaminmu Æ´ancinmu.“`
°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°
**
“`Marubuciya“`
“`Ramin mugunta“`
“`Fulanin tashi paid book 1&2“`
“`BaÆ™ar Ashana“`
“`Na miji rigar Æ™aya👉🏻(Yayi min illa)“`
Labari da Rubutawa.
Rukaiya Abubakar Umar (Waheedat).
Shafi na biyu ✔️
Bana gasa da wani ko wata, sannan bana tara samari da yawa da sunan ado ko wani abin, ni a tsarina idan mutum yazo yace yana so na to tabbas in na aminta da halayensa ina turashi wajen mahaifina ne kawai, tukum ina da lalurar da dole idan mutum yaxo neman aurena sena faÉ—a masa walau ya tsaya mu ci gaba da soyayya ko kuma ya Æ™ara gaba ya nemi wata, *(Ina kira gareku Æ´ammata da samari da kuma jan hankali Don Allah idan mutumin kirki yazo neman auren Æ´arku idan kun bincika kunga beda wata makusa to ku bashi aure sannan idan Æ´arku ya zama tana da wata lalura wacce take fama da ita ku sanar da wanda yazo neman aurenta karku rufe kuce se bayan aure tukum ya faÉ—a hakan ba dai-dai bane ba)* wannan dalilin yasa duk wanda yazo neman aurena kafin iyayena su faÉ—i lalurata na faÉ—a, wani sa’in ma zuwan farko nike faÉ—a to kaifa wane ina da lalurar jinnu zaka iya aurena a haka, ko kuwa za muyi haÆ™uri da juna tunda maza da yawa basa so su auri mace da lalura sedai in bayan aurensu ne Allah ya jarrabeta da lalurar shine wasu zasu haÆ™ura su zauna dasu hakanan babu yadda za suyi ne, sannan kuma akwai masu imani cikinsu wasu idan suka ce suna sonka to suna sonka ne har cikin zuciyarsu, wasu kuma Æ´an soyayya ne kawai ayi soyayya a wuce fagen.
Haka na tashi haka nike rayuwata yara sune abokaina da kuma wayata, kasancewar mu goma cif mahaifiyarmu ta haifa ni ce ta biyu, daga Yayata Mardiya seni ke binta sai Æ™anina Abba da sauran, sau da dama Æ™awayen Yayata ko Æ™awayen Æ™anwata ummi zasu xo ni kuma babu me zuwa wajena saboda bana ra’ayinsu kamar yadda na faÉ—a tun farko, Babana har tambaya yake ni bana da Æ™awaye ne kwata-kwata bana fita daga makaranta se makaranta, sedai kawai nayi murmushi saboda ko da na shirya nace zani wajen wata Æ™awa to bana zuwa sedai na É—an wasa Æ™afata na dawo gida wannan shine kaÉ—an daga cikin tarihin rayuwata.
A hankali na saba ta malaman makarantarmu har muke zama muyi hira dasu idan an tashu break, har sabo ya shiga tsakaninmu sosai musanman Anty Zulaihat da bata ɓoye min komi dangane da rayuwarta, cikin lokaci ƙanƙani se gashi har mun ƙulla ƙawance na fara zuwa gidansu kums ko da yaushe muna tare a waya.
Yau ma kamar kullum nazo makaranta bayan an tashi break muna zaune muna kwasan dariya sega shugaban makaranta ya shigo (Section) ɗinmu, ajina ya fara shigowa muka gaisa dukkanmu tukum sauran suka miƙe suka shige ajinsu ni kuma na ci gaba da yima yara karatu, ina tsaka da yima yara karatu Anty Rahama ta shigo kanta tsaye ta fara balbaleni da faɗa akan mu dena zama wuri ɗaya da sauran malaman idan antashi break saboda yadda yara ke duduma a cikin azuzuwa ba ruwanmu dasu, gyaɗa kaina kawai nayi ba tare da nace mata komi ba na ci gaba da abinda ni keyi tana tsaye tana kallona, ni kuma a ɓangarena ban cika salwantar da miyon bakina ba akan wani ɗan dalilin da be taka kara ya karya ba, kawai ni abinda na tsana shine in zaka min faɗa ka jani gefe kayi min faɗa ba ka tsaya bainan nasi kana faɗamin ba sukari ba, hakan na ƙona min rai sosai kuma sena dunga gani baka ɗaukeni komi ba shiyasa kale dizgani wajen mutane, ganin bance mata komi bane ba yasa ta fice daga ajin ta wuce ta ajin sauran malaman ba tare da ta musu faɗan da tamin ba, saboda ina iya jiyo duk abinda yake gudana daga sauran ajin, sema wasa da dariya da suka dinga yi harta fita daga azuzuwansu ta wuce nata.
Ana tashi daga makaranta bab tsaya ko ina ba, na dawo gida bayan na huta na bama mamana labarin abinda ya haɗamu da Antyn nan ya kaiga tamin faɗa, haƙuri mamana ta bani tace ai wajen aikin kenan dole se kinga abinda bakyaso wata rana kuma haƙuri akeyi baa ramawa dan idan kace zaka rama abinda wani yayi maka ba ci gaba kenan sai ci baya, haka ta dunga bani baki tukum na haƙura.


​
Name: | [Yayi min illa Hausa Novel Complete] |
---|---|
File Type: | Download Novels as .TXT .PDF .DOC (WPS) .HTML |
Uploaded By: | www.mynovels.com.ng |
Category: | Hausa Novels Documents |
Tags: | #Hausa Novels Documents #Hausa Novels Books Complete Hausa Novels #Hausa Novels #Hausa Novel #Romantic Hausa Novels #Sabbin littafan hausa |
Novel Price: | Free |
Last Modified: | October, 2022 |
Idan Kuna Bukatar Hausa Novels Audio Ku Shiga anan Kana ku danna Subscribe a tashar My Novels TV
Zaku iya sauke Manhajar Android ta My Novels anan Domin samun littafan Hausa maras adadi

Zaku iya shiga WhatsApp Group namu na My Novels anan domin samun Littafan Hausa Maras adadi

Domin samun littafai a saukake su shiga group namu na Telegram
